Chapter 85
Chapter 85
cewar Nahidt na iya zamewa rayuwar mijinsu mugun jarabawa ko kyakyawar jarabawa, ta kasa yin irin nata ta koyi hakuri ta koyi kaunar kasancewar Nahidt a tare da su, harma ta fuskanci cewar jihadi ne idan har ya aikata hakan, su kuma idan suka talafa masa zasu samu nasu sakamakon mai kyau, ita abinda ta fi kwarewa a shi shine wannan daga kan da jiji da kai ita ga matar malan, ta bi ta rikita lisafin masu karamar kwakwaluwa na cikin anguwa ta koya masu gori da kadarar mutun, dan rashin hankali ta koya masu abubuwa mararsa ma'ana har sai yanzu da daidaiku ke gane wacece ita suke barin makarantar izgilinta sunna fuskantar rayuwa , A tausashe ta budi baki zata yi magana a tsawace Furera ta dakatar da ita da hannunta tana fadin" Dila Malama kar ki ce min komai a nan, da bana nan da kin ci min amana kin lalumi karuwa an lakawa mijina an ci amanat..............................................." Tassssssssssssssssstssssssssssss tsadadan marin da ya sauka a kusa da bakinta ya sakata daukewar magana da firgici harma ta juyo a haukace tana kallon wanda ta auna mata tikiten tashin hankalin nan na kakausan mari mai balakin zafin tsiya Ido ta kwalalona lokacin da ta ga ikon Allah, ba ita ba, harta da Hajia Matar Malan, da Nahidht idannuwan suka zarro a lokacin da Shuwwa ta cire Hijab dinta ta je da gudu ta janyo cazar waya idannuwanta sun kade a haukace ta ce" Baki gane ba Furera, an jima da daina zagi , bara na ci ubanki a cikin gidan naki ki kai karata ke har yar tasha ce a nan? Da nake raga maki kin dauka dan kin isa ne? Tunda baki da hankali bara na gwada maki shegantakama iyawa ce sai ki samu dalilin tsanarmu da zaginmu, banza jahila da kike anfani da laifin wani kina zaginsa da shi bayan ke dinma halita ce da Allah ya halita baki da tabacin yaya gobenki take!" A haukace ta zuga mata zugawa guda ta daga ta sake zabga mata , hakan ya sa da dukan karfinta take kokowar son kwace bulalar sai dai kamar yadda SHUWWA ta fada mata cewa shegantaka iyawa ce, haka abin yake, bata san cewa idan ka tashi neman fitina jinjinar kanka kake yi ta yadda zaka yarda da kanka cewar zaka iya, ta dauko da zafi tana wasa da shi a hannunta ne bata san cewar akoy masu dibansa daga cikin tukunya su kaishi baki ba, ta yi wasa da damarta tun ana bata girma sanadiyar mai girma har ta kai wajen da aka ajiye gefe aka fuskanceta a matsayinta na mutun Da karfi ta hankadeta hakan ya sa ta maku da jikin garu tana haki ta nunota da yatsarta ta ce" Kin jima kina zaginmu da sunna karuwai, kin jima kina dukan kirjin ke kin isa ba'a isa a auro maki karuwa cikin gidanki ba? Furera an fada maki ban san cewa kece matar da ta bini gidan sarakuwata ta ce ni karuwa ce har mamansa ta saka ya sakeni ba?, Ko baki san cewar na san da kafin na tare kika je kika yi bayanin wacece ni wa Elhaj mai shinkafa ba har ya bani tikitina a cikin mota?, Ko ji kike ban san cewa ke din nan kece wace ta yiwa matar uban mijina bayanin wacece ni ba har aka hanna shi tarewa a dakina har zuwa ranar mutuwar aurena ba?, Ke takamarki musulma ce ke anya kina jin tsoron Allahn da ya haliceki kuwa?, Kin san zaki mutu kuma zaki je gaban ubangiji me zaki ce masa a kan tsangwamarmu da tsanarmu da kika yi dan mun kasance masu aikata laifi wa shi da halicemu maimakun ki yi mana nasiha ne?, A anguwa kin tare gaba kin tare baya kin kula mana shari kala daban daban ya zamto makotanmu bamu da kyakyawar alaka da su dan kin nuna har mata bi muke yi? Ke meye shedar fa zaki bayar a gobe kiyama a kanmu ne?, Furera walahi sai kin mike mun kashe junna yau a falon nan ko ni ko ke!" A haukace ta sake yin kukan kura ta nufeta tana ihun fadin" Ki tashi na ce ki tashi!" Dan gyarn murya ya yi yana idasa shigowa ya yi salama a sanyayensa yadda ya saba ya sake sauke idannuwansa a kansu Kuka ta fashe da shi daga wajen da Shuwwa ta makata da garu tana lankwashewa irin bayantan nan tamkar bayan nata ya kalle tana fadin" Innalilahi wa inna ilaihi raj'une me na maki?, Me na yi maki da zaki dakeni harda hadani da garu bayan kin zageni ta uwa da ta uba? Me na maki ne a rayuwa zaki zo har cikin gidana ki wulakantani da min ikirarin mijin da nake takama da shi kun gama da shi kun shanye shi?" SHUWWA ta yi murmushi tana juyawa wajen mayafinta da ta cire ta ajiye ta dauka tana maidawa a kan gashin kanta da tuni ribom dinsa ya cire a kasa ta nanada da cazar dake hannunta sai da ta daure da kyau kafin ta juyo wajen da Nahidt ke zaune, ta ga a zaunen dai take tun zarro idannuwan da ta yi bata kuma yinkurin yin komai ba sai uwar gidan Malan ce ta ce" Ki ji tsoron Allah Furera, ki guji kafurin kishi Furera, idan kikai haka jin dadin na kankanin lokaci ne a cikin gidan duniyar, zaki je ki samu ubangijinki a kiyama, ki sani Furera koda jin dadin muzgunawa wani ya zame maki a duniyarki har ki je ga kiyamarki ne to fa da zarar kin mutu kin hadu da sakamakon abinda kika shuka kennan har zuwa tashin kiyama, shin yaya zaki yi idan ubangijinki ya tsayar da ke a gabansa ya tambayeki abubuwan da kika aikata a duniya bayan ya haliceki ne dan ki yi masa bauta me zaki ce? Ke ce hada wannan da wanan, kece zagin kadarar mutun, shin ke kin tabata kin isa ki juya salon rubutun ALK'ALAMIN kadararki ne?" Malan ya sake furta" ASALAMU ALAIKUM " Juyowa malama ta yi a nutse tana amsawa kafin ta matsa gaba daya ta bashi hanya ya shigo hakan ya sa Furera sake rakata da mugun harare mai zafi tana ji a cen kasan zuciyarta a duniya idan akoy makiyinta bayan matar nan ne, bata taba gannin mace mai kafurin hakuri da jarababen biyaya irin uwar gidan Malan ba, da ba dan ita ta san me take nacewa a zamanta da Malan ba da ko dan hakurin matar nan ta barshi ta yi tafiyarta nesa da shi, sai dai malan din ne duniya ne, ba zaku gane ba malan duniya ne A nutse ya masu nuni da wajen zama gaba dayansu Shuwwa ta cije baki da abin dukanta a hannunta tana jin haushin zuwansa bata farfasawa wannan tsageran jiki ba wai shari ne zata yiwa mutane ikon Allah, tabas sai ta koya mata hankali ko yau ba, wannan alkawari ne ( kai jama'a kamar irin zaka ladaftar da yaron da ka haifa din nan Da sauri ta zagaye Shuwwar ta karasa wajen zama ta zauna a gantsare dan so take malan ya ganewa idannuwansa cewar mahaukaciya yake neman yin taraya da ita ko me? Sai da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188