Chapter 56
Chapter 56
daukan amarya ne suka karaso ba A nutse ya ce" Ki ji tsoron Allah a zamanki da shi, ki yi masa biyaya da dukan karfin iyawarki, ki sani aljanarki ce zaki je nema Shuwwa sannan ki dauka zabinki ne shi din ba hadaki akai da makiyinki ba, zaki kwatanta haka?" Malan ya fada yana sake kallonta hakan ya sa ta sake jin zuciyarta ta karye sosai, ta kalle shi, ta juya ta kalli gogonsu ta kasa furta koda A ne Gogonsu ta yi murmushi tana zama a kusa da ita sosai ta kamo hannunta na dama tana kallonta ta ce" IBTISAM, gashi na sanki a kuraran lokaci, duda ba mutuwa mukai ni ko ke ba aman zaman aure zama ne na tafia aa rayu da miji ba shirme ba, ki sani ni mamanki ce, Allah ya jikan mahaifiyarki ba zaki kuma yin kukan maraicin rashin uwa ba, kar cenjin da kika samu ya rude ki SHUWWA jinnin dake gudu a cikin jikinki ba na ja da baya a gaban gwagwarmaya bane ko wace iri ce, uwa uba babar kokowar duniya itace ta mace da mijinta, da yardar Allah furucinsa zai dawo bege a gareki, maza yiwa Abanki salama mu tafi ba'ai masu dare a wajensu duda matar uban gidansu za'a kawo ta yiwu mu ko karfe nawa muke son shiga ko fita muna iya yi kanmu tsaye" ta karashe da dan barkwonci bata kula da kallon kun shiga uku da Shuwwar din ke binta da shi ba Wannan jawabi da gogonsu ya saka bata daukarwa Abanta alkawarin zama lafiya da abokin gaba ba, da wannan aka luluba mata abin rufa abinda ba'a taba yi mata ba, a yau kuma uwa uba rakiyarta harda NAHIDT wace sai da aka zo shiga dankareriyar ferarin da za'a kaita a ciki Malan ya sake jadada maganar cewa daga cen a sada NAHIDT da gidan Hamza bisa umarnin manyansu Ita dai a yau bata da ja in ja da KOWA, kai bama zasu gane bane aminiyarta da kanwarta ta aurar fa? Ai yau ita shagali takeda a gabanta mai zafin gaske, a dai kai rigimatu kurjin gwuiwar nan a dawo a ga bidi'a ta arziki, yau Malan zai gane itace Nahidht (🥺 Hum) Lafaya ce aka nada mata a saman wando da rigarta masu santsi farare kal , hakama lafayar fara ce kall Sun tanaji kayan nan ne saboda irin wannan lokacin da sukai tunanin zasu sadata da dakin Hamza ne A tanadin nasu harda makup suka so cencada mata sai dai a yanzu ta tsaya a kan kafafuwanta ta nuna cewar bata cikin yaren makup, su je kawai su sadata da dakinta kowa ya kama gabansa, a cikin zuciyarta kuwa kudirinta shine abinda sunna zuwa zata biyo bayansu? Shirme suke yi da batawa kansu lokaci Matar tsohon ganaral, watau maman Hamza da gogonsu ne rike da ita a tsakiyarsu A hankali bayan sojojin dake tsaitsaye sun bada damar ana iya fitowa da ita Matar tsohon ganaral kasa kasa sosai ta furta" Ki karra sada kanki My daughter ta yadda yarensa ba zasu ga fuskarki cikin sauki ba, domin matar uban gidansu kike, zasu ganki ne bayan ya ganki" Jajayen lebunnanta ta dan dantse a hankali, domin tunda aka ringa ambatar masha Allah tap wannan tsaro haka? Gabanta ya farra faduwa, saima da aka ringa fadar to wai dama haka gidan baban yake kamar a turai? Ta ji zuciyarta na yi mata mugun bugu na zartacen ka'ida Bindigogin dake hannayensu wa'inda suka ririke su biyar a laye a bakin hanyar shiga bayan sun gama yin jawabai na oyoyo da maraba da zuwa wa madame din oga ne suka daga sama suka harba wanda hakan ya saki gigitacen karan da ya firgita dukkan wani bakon al'amarin, ya saka shauki ga wa'inda suka san ana haka kuma sai mai matsayi ake yiwa hakan watau sai matan manyan ake tarba da hakan Cikin wa'inda karar bindigar ya zowa a ba zata harda SHUWWA , hakan ya sa ta damki hannun gogonsu muryarta cen ciki ta furta" GoGo bindiga" Tsinkayo muryar NAHIDT cikin murna tana fadin" Kai soja duniya ne, tarbar oyoyo da kukan abin kisa ake yi, mtssss tsakani da Allah soja zan tafi" ya sakata sauke nanauyar ajiyar zuciya tana sasautawa Gogonsu rikon kasa kasa ta sake fadin" Mahaukata, komai nasu a haukace ba irin na mutane ba, komai basu kya yinsa a nutse ba sai a gigice, cen ku da bindigarku!" Ita dai goginsu yar daria abin ya bata domin rabin jikin Shuwwa din a jikinta yake dan ta dan rankwasa jikinta sakamakon jin da ta yi santsin wajen na son dagata da dogon takalminta ya maka kasa bayan bata ra'ayin hakan, bata gannin gabanta ga jaraba sun tanaji acokal dan su cocoka gaban Hamza, asge Hamza yayansu ne? Kai jamai Dukan yan rakiyar amaryar da suka zo sanadiyar Tsohon ganaral da mutanen Matar Malan uwar gida da matar Malan din kanta a bayansu suke, a lokacin da suka ja suka tsaya sunna shirin shiga Nahidt a sanyaye kamar ba ita ba dan Shuwwa din ta ji maganarta ta ce" Gogonmu, dan Allah ku dan tsaya Shuwwana ta yi adu'a kafin ku sadata da cikin gidanta" Dan matsawa ta yi kusa da Shuwwar din a nutse ta shiga furta" Shuwwan Mamah, shuwwan Abanta, Shuwwan yayarta? Dan Allah ki yi adu'ar neman alkhairin auren nan kin ji? Kin ga kamar da ran iyayenmu, kina gannin wata daraja da ta lulubeki kuwa ? Gaba daya sai na yarda mai daraja kika aura, dan Allah Ibtina ki yi adu'ar shiga cikin gidan nan da fatan zaman lafia da mijinki kin ji? Ba dan ni ba" A hankali IBTISAM ta lumshe idannuwanta sannan ta bude ta shiga dan kokarin bude gaban furkarta dan ta kalli yar uwarta da muryarta kadai take ji Tana budewa sukai ido hudu da junna ashema a gabanta take kadan sannan ta hade hannayenta waje daya tana kallonta Tunda aka fara lamarin daurin auren nan sai yanzu murmushi ya subuce mata a saman fuskarta da ta ga irin abinda yayarta ke yi mata idan tana so tai mata biyaya A hankali ta saki hannyensu ta damko na yayarta sannan ta dan matsa jikinta ta rungume ta a jikinta sosai Muryarta cen ciki tana dan rawa rawa ta ce" Ban taba tunanin zaki iya barina a nan ba mamanah, Nahidt ke ce Mamanah kin va Abama haka ya miko ni" Ajiyar zuciya Nahidt ta yi tana share mata fuskarta ta ce" Alkhairi muke fata mu dukanmu my baby, kin ga Abanki yana son ki, Allah ya saka masa sonki kamar y'ar da ya haifa, na tabata ba zai miko ki ya manta da lamuranki ba, nima kuma za'ina zuwa kulun kulun wajenki, now ki tayani mu yi adu'ar neman tsari da shedan, da dukan abin ki, adu'ar neman alkhairi a zamanki, koda na kwana daya ne ai kin san alkhairin kwana daya ya fi rashin alkhairin kwana daya kau?" Kai ta gyada da kanta suka yi adu'arsu suka fara shiga sannan sauran suka bi bayansu Iyakancesu matar Tsohon ganaral ta yi a fallo su su hudu kadai suka haura sama domin Fauziya tana gidab Malan itama a gau za'a mikata dakinta da sun koma Ita da kanta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188