Chapter 105
Chapter 105
tana kallonsu sunna kallonta Dan murmushi ta yi tana girgiza kanta ta ce" Alhmdulilah ala kulli hallin" "Zaku iya maimaita kalmar godiya ga Allah subahanahi wata Allah kuwa?" Ta sake fada tana kallonsu A hankali suke gyafa kawunnansu A sanyaye ta sake furta" Alhmdulilah" Summa da daidaya sai suke fada sunna kuma yin shiru da bakunnansu A sanyaye ta ce" IBTISAM kin ga nima ban yarda cewar sun rasu ba" Da sauri NAHIDT ta kalleta a raunace ta ce" Mama haba Mama" Mama ta yi gagawar cewa" Haba Nahidt, to ai ba sabo bane, ba laifi bane, ba haramun bane, abinda nake ji ne na fada , kuma ina mai tabatar maki tun daga cen kasan zuciyata nake jin cewa basu rasu ba" Tsatsareta suka sake yi da ido har Shuwwa ta ji idannuwanta na zafi a hankali ta ce" Mama kema baki yarda ba ko?" Mama ta gyada kanta tana sakin hannunta ta dafe gaban goshinta tana fadin" Kin ga, su sun rayu da ku ba tare da sun fada maku garinsu ba, Menene dalili? Kasata mai dadin riko a zuciyya?, Ko daga rami ka fito watau aka ce cen ne asalinka zaka ga ko ka tare a karshen kasashen duniya lokaci zuwa lokaci kana sako maganar garin haihuwarka kana begenta harma ka ringa fadin abubuwan da kuke da shi masu daraja a garinku, aman ace iyayenku basu da shaukin zanta haka a tare da ku kadai da Allah ya basu? Wannan shine tabatuwar labarin mahaifiyarku , na yarda cewa Hamza yyayanku ne kuma danginku ne suka wakilci daurin auren IBTISAM, sai dai labarin mahaifinku ne na kasa kamo zaren maganar, shi kuma wanene shi?, Shin shine mahaifin Hamza ko kuma shi din wani ne daban mai tatare da boyayan Al'amari?, Abinda na sani shine zuciyata ta kasa aminta cewar sun rasu, ban sansu ba, ban taba ganninsu ba, ban san me ke tafe da rayuwarsu ba, aman ina ji ban yarda da sun bar duniya ba........." Ajiyar zuciya take ta saukewa ta dora da fadin" Ni dai mutun ce kamar kowa, ban isa na iya cire maku damuwarku ba, aman kun san me? Zamu tashi tare mu je saudiya da ku, zamu je wajen da kuka zauna da iyayenku shekaru masu yawa baya, zamu sake bincikawa sannan mu sake bibiyar hakan, Daga nan zamu amshi dama wajen ikon kasar mu je mu duba kaburburan su, zamu roki Allah idan sunne ya saka mana salama da dangana a zukatanmu, zamu yi iya yinmu, idan har amsar ta zo daya ce cewar babu su, zamu zo mu zauna mu fahimci junna, domin a rayuwarku komai ya yi min banda al'amuranku na furucin bakinku, da wasu abubuwan, a matsayina na wace zan rikeku tamkar uwa a wajenku zan fada maku gaskiya cewar dole zamu kasance masu laushi, matan da suka amsa sunnayensu mata, a farawa daga yau, daga yanzu yanzu yanzu zan fara da baku kadan daga cikin sirikana, ba gudu ba ja da baya kuma sai kun yi domin ni mamanku ce!" Gaba dayansu har wani tsigar jikinsu ke tashi, dama bayan Malan akoy wasu mutanen da suke rike da dabi'un mutane masu daraja na gidan duniya?, Basu kara yarda da lamarin na gaskiya bane sai da ta gama barawa masu aikinta salahun dukan abubuwan da take so su kular mata yau sannan ta aiki Lami zuwa bakin hanya ta siyo mata manyan Po na hawa biyu, sannan ta ja su makeken dakinta mai dauke da falo da dakunna biyu a cikinsa bayan falonta ta shige daka da su ta fara ciro kayayakin da gaba dayansu sai da mamaki ya fara kashe su kafin su maida hankalinsu kanta domin wani zama da Shuwwa ta yi a kasa ta baje kafafuwa ta sakata mikewa ta sakata ssake zamanta ta halin nuna mata cewar mace yarinya ko baba, ya dace ta kiyaye zama irin na wara kafafuwa, ta iya zama na hade kafafuwanta ko a ina zata zauna, wannan din zai hanna mata saurin kamuwa da iskar gaba Kayayakin da ta fara fitarwa sunne SASAKEN BAURE, Kananfari, Cristaux de menth, ta raba masu aiki kan daya ta dora dahuwar sasaken bauren nan, daya kuma ta zo ta daka kananfari, sannan ta ciro abin cire akaifa da kayan gyara ta baje masu a nan kafin ta koma falo dan amso Po din ( bayanin yadda ake anfani da su a page na gaba in sha Allah) ___________________________________ Daga wajen da suke tsaitsaye sunna kallon kokowar da ake dima tsakanin Lieutenant Ganaral da wannan bakon marar lafiyar abin na daga masu hankali, sunna so su shiga aman umarnin da ya bada cewar a barsu ya saka kowa ke tsaye jinninsa a akaifa yanna kallon abinda yake faruwa Matarsa dake tsaye hannayenta rungume a kirjinta muryarta a sanyaye ta ce" Ta yaya za'a ce mijina mahaukaci ne, haukan yaushe ya same shi ne?, A da mijina ba mahaukaci bane, shi dai burinsa mu bar kasar nan, dan Allah ku cewa wancen bawan Allahn a salamemu mu bar kasar nan, mun tuba bama son zaman garin dan Allah" Likitar da ta gama sauraronta ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Idan kuka fitan ina zaku je?, Me yasa yake maimaita kalmar a barshi ya tafi? Ya tafi ina? Ina danginku ne?, Ko baku da kowa ne?" Zata kuma yin magana gaba dayansu suka juya a firgice jin datijon nan ya fashe da kuka, domin abu yake dauka yana makawa Ganaral dan ya barshi ya fita aman mirsisi mutumen sai ya ki koda kwakwaran motsi ne, kuka yake yi kansa da kafarsa a haukace ya ce" Wayo Allahna baka gannin abinda nake gani ne?, Bina ake yi da wuka ana huro min wuta, kasheni ake son yi, kuma shekara yau daya bayan daya shekara goma sha biyu rabona da y'ayana, sun dauko mu mun zo da mu nan dan su halaka mu? Na ce na bara masu koma me suke so , ni burina na rayu da iyalina cikin kwonciyar hankali da nutsuwar zuciya, ko na tambayi da yawa ne?, Ku barni na je ga IB.................. " 😩😭 I'm sorry I'm seek walahi 👏👏👏👏💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥 *ALK'ALAMIN K'ADDARA TA* 💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥 *The Hero writer* *SAJIDA* _Bismillahir rahamanir rahim_ PAGE:. 43 *P͓̽R͓̽E͓̽S͓̽E͓̽N͓̽T͓̽* *S̉T̉ỎR̉Ỷ ẢN̉D̉ W̉R̉ỈT̉ỈN̉G̉ B̉Ỷ* *S͞͞A͞͞J͞͞I͞͞D͞͞A͞͞* *T͞͞H͞͞E͞͞ H͞͞E͞͞R͞͞O͞͞ W͞͞R͞͞I͞͞T͞͞E͞͞R͞͞'S͞͞ 👇🏻* 1 *yar mahaukaciya* 2 *Banida zabi* 3 *Duk karyar kada* 4 *Baka ce* 5 *Daga tafiya daukar soja* 6 *Kutkale* 7 *Makauniya ce* 8 *Mage mai kwanciyar daukar rai* 9 *Duk nisan jifa* 10 *Dutse* 11 *Idan Ka Raina Inda Kake*. 12 *Neman Na Kaina* 13 *WATA KOKOWAR* *The Latest Qualitative New Book ALKALAMIN KADARRATA* *WANNAN BOOK NA KUDI NE BA FREE BANE, IDAN KINA DA RA'AYIN KARANTASHI KI GARZAYO KI BIYA KUDINKI YAR UWA ZAKI SAMU BONUS NA DUKAN LITATAFAINA CIKI HARDA NA KUDIN DA NA GAMA KWANAN NAN, KI GANE................ALKALAMI NA DORA, NA ZUBA RUBUTU......IN SHA ALLAH ZAKI NISHADANTU SANNAN KI KARU💓💓💓* Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi. Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar 08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo. Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618 Ga ƴan Niger zaku
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188