Chapter 48
Chapter 48
ya sa kowa shafawa A hankali ya dago hannayensa daga tsayen da yakr ya shafa fatiyar yana jin kansa na sara masa Shi yau ya yarda da maganar malan mahaushe, ya fito kama barawo yau barawo ya kama shi Gaishe gaishe ake yi, hakan ya saka shi neman hanyar da zai silale dan ya koma wajen aikinsa ko zai samu hayaniyar da DAD ya siya masa ta dan sake shi, gaba daya kwaramniyar wajen ta dame shi Hannunsa da aka rike a lokacin da yake dan sauri dan ya gifta kofar gidan ya tafi ya saka shi juyowa a nutse yana kallon Abansa Murmushi CHIEF OF ARMY ya yi ya ja hannunsa ba tare da ya ce da shi komai ba ya nufi cikin gidan da shi a ransa yana ayana' Akoy rigima, akoy kura, Allah ka sa mu fi karfinsa' Mutanen dake tsaitsaye suke nausawa sunna shigewa, a nan ake nununa shi ana fadin wai Allah shine ya auri SHUWWAR? zuciyar amaryar malan tamkar zata buga, dama wannan rantsatsen sojan na jarida ne zai auri wannan yarinyar? Balaki, bilahilazi in wani tudu in wani gangare sai ta bi ta fada masa shima ya yi hankali ya kwashi HIV! Hannunsa ya dan ja yana kallon Father wanda ya juyo yana kallonsa Sai da ya dane dukan bacin ransa kasa kasa yana hararen mutanen dake kallonsa kar wasu mahaukata ya ce" Bayan auren dolen ina kuma zaka kaini ne?" Father ya yi murmushi bayanane ya sake jan hannunsa yana fadin" Inda su Malan suka shiga zamu je, zo mu tafi mana " Bakinsa ya dan tabe yana biye da shi har suka shige falon Kanshin falon na nan, sanyinsama haka, koke koken da ake yi kuma ya dan tsagaita asalima su da suke daka sun dunkule waje daya sunna jira ne a shaida masu an daura auren Fauziya da Hamza dan su tatara su koma gida gaba dayansu da Hamzan wanda ya ki motsawa nan da nan daga kusansu , asalima a jikinsa ne du suka dodora kawunansu, sannan kasancewar kofar fallon mai madubi ne mai nauyin nan ya sa ba'a jij abinda yake faruwa a waje hakama abinda yake faruwa a ciki na cikin ba zai ji ba Tunda su Malan suka shigo yan matan da Hamza suka dago sunna kallonsu, hakan ya sa shigowar MUHYIDEEN da CHIEF OF ARMYMA a kan idannuwansu ne Gabanta ne ya tsili, ya tsilira ya rugurguzo ya zubo kasa a lokacin da ta ga fuskar la'ananen da ya yi kiran kuraya fa ita ya kashe mata aure wanda ya kara saka mata tsantsar tsagwaron tsanar sojoji bayan wace take da ita a ranta ta da cen cen cen Idannuwanta dake warwaje ta sake rukowa a kansa lokaci daya ta kama hijab din nan ta cire dan bilahilazi a yanzu sai ta ji hijabin zai shaketa ya kasheta domin kwata kwata ta nemi numfashi ta rasa , wani tashin hankalin ganninsa kadai ya sakata nuno shi da yatsarta manuniya tana fadin" Kai? Me ya kawoka gidan nan? Hala kaima abokin Wani ne a nan? Baka san na yiwa kaina alkawarin idan na kuma ganninka sai na shakeka ba? Aunty kin ganshi nan, shine Wannan, bari ka gani!" Tana fada ne tana dira ta tsalake kafar Hamza dake mike yana kallonta da mamaki baki bude, hakama duk wani dake falon kai balema wa'inda suka gama daura masu aure yanzun sun fi kowa kamewa a tsaye sunna kallonta a lokacin da ta nufo LIEUTENANT GANARAL dake tsaye kikam yana kallonta da son tinano a wajen da ya santa ta dira, ta cira ta ........ 😂😂😂😂 Comment hlz😭😭😭❤️❤🔥❤🔥 ALKALAMIN KADARRATA❤️❤🔥❤🔥 Na SAJIDA 1️⃣8️⃣ Babu wanda ya kawowa ransa cewa a cikin kasar nan, a kusa kusa akoy halitar da zata nufo MUHYIDEEN da wannan garajen a lokacin da ita SHUWWA, yar mintsiniyar Yarinyar nan ta daka tsale ta nemi kai hannayenta wajen wuyansa dan ta aiwatar da alkawarin da ta yiwa kanta na sai ta shake shi idan har ta hadu da shi ko a ina ne, ta kuwa nemi aikata hakan a haukace tana fadin" Bayan ka jaza min ya maka min sakin a ofishin sojoji tamkar wata yar ta'ada, shine zaka kuma yin gigin zuwa wajen nan? Wollah yau ko ni ko kai a gidan nan!" Dan kaucewar da ya yi yana sake kallonta da fasarar ko ita wacece na shirin darsuwa a cikin kwakwaluwarsa, lokaci daya ya gane yarenta ya kuma haskota harma ya tuna ko wacece ita da lokutan da ya ringa ganninta kwaya biyu tak Abinda ya sa gaba daya ta bace masa mugun gyaran nan da ta dauka na mamaki wanda ya karru a kyanta na da Da mamaki ya dan motsa hannunsa yana tareta dan sake zuwa ta yi da kai kamar rago tana son kawo masa tunguzo tana wani ihun fadin" idan a cen kana takamar da yarenka a wajen ai gashi yau na kamaka babu mai iya tare maka!" Sallalamin da iyayen ke yi a bayane ne ya saka Malan da ya yi mutuwar tsaye dan zabura kamar an gwaura masa mari da madaukakin mamakin al'amarin Shuwwar da ya kisan sumar da shi wai harda yau ta kama wannan bawan Allahn da idan a hadiye ne zai sakata a bakinsa ya hadiyeta ba tare da ya sha ruwa ba domin ba zata gimshi makoshinsa ba tafa hannunsa ya yi ba shiri dan shine abinda ya fara zuwar masa kwakwaluwa kusa kusa yana fadin" Subahannalah, Ke Shuwwa, ke Shuwwa meye haka wai? MIMIMIMijinki ne fa, me kike yi haka ne wai?" SHUWWAR da ta ja wata dungar sai ta samu kanta da yin kiskirim tamkar an zabga mata bulalar rakumi a fuskarta ta dauke hankalinta gaba daya na sekwani kafin ta saketa, dan kuwa sai da ta maimaitawa kanta yaren malan a cikin kwakwaluwarta tamkar karatu kafin ta iya fasa bakin ta gane me ake nufi, hakan ya sa a hankali ta juyo tana kallon Malan da mamakinsa ya kasa boyuwa hakama dukan mutanen dake wajen , ita kuma da wani kallo kamar na tsoron abinda ya fito a bakin Malan din bakinta na rawa rawa ta ce" Innnnnnna ce aure aka daura na Fauziya da yayanmu, ni kuma nawa sai na samu wani mijin kau Abana?" A yadda ta yi maganar zaka gane baban burinta Aban nata ya bata amsa ne da eh y'ata, sai ta samu déception mai matukar girma a lokacin da yake furta mata kalamai kamar haka" Bayan an daura nasun kema aka daura naki da LIEUTENANT GANARAL MUHYIDEEN MUHAY na kasar nan baki daya wanda daga CHIEF OF ARMY sai shi a iko a kasar nan, shine a tsaye a bayanki gayanan kike aikata aikin nan haka IBTISAM!" Ido, baki sa Hanci su NAHIDT suka zarro gaba dayansu harda Hamza jin wai LIEUTENANT GANARAL MUHYIDEEN MUHAY ne aka aurawa kanwarsu? Wauh , su abin ya basu sha'awa ne, ya birge su ne, ya taba zuciyarsu ne MUHYIDEEN din kuwa da mamaki ya kalli CHIEF of army yana nuna Shuwwar dake daf da kafafuwansa muryarsa ciki ciki ya ce" Dama wannan ce ka aura min Dad ?" Da hannayensa ya nuna wajen kansa alamun gyadi gyadi ya ce"Mahaukaciya ce fa, nd yarinyar nan du haduwar da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188