Chapter 11
Chapter 11
Kar ki ce min bayan halin rayuwar da muke ciki kin manta cewar D'a baya auren matar ubansa koda kasa ta binni idonsa? Da ace ba'a dauran aure da mai shinkafa bane ake iya duban wani abu makamancin haka, aman aunty so kike mu fara shiga hurumin ubangijinmu kuma?" "Kin ga SHUWWAR kar ki sakani a uku bayan wanda nake ciki mana, ni bana nufin aure ya shiga tsakaninki da shi dan Allah aman kuma ya shigo cikinma ai ba laifi bane ko?" NAHIDT ta fada tana kallonta da tsatsareta da manyan idannuwanta SHUWWAR ta girgiza kanta tana juyawa wajen ABDUL Mutalab da ya kai duke a wajen ya kurawa waje daya ido a sanyaye ta ce" Ka yi hakuri , ban san sunnanka bama, ka ga du iskancina bana son taka dokar ubangijna,, domin na yarda da mutuwa kuma na yarda da tsayuwa a gaban Allah gobe kiyama, shi yasa nake kiyayewa, nake matukar kiyayewa dan da tarin laifukana idan na sake bayana da irin wannan wanda nake tunanin cetonsama zan iya rasawa watau annabi Muhammad sallalahu alaihi wa salam" Ta sake sauke ajiyar Zuciya tana fadin" ka ga sakina ya yi a cikin motarsa bayan ya gama zazagin yayata da sunnan karuwa, shi yasa na tarda shi gidansa nima, idan dan wannan ne ka barshi ya rama abinsa, aman ni babu wani abu da zai iya shiga tsakanina da d'a namijin da ba muharamina ba da ya wuce aure, AURE nake so na yi, so nake na yi aure mai daraja na raya sunnar ma'aiki, ina so idan na mutu mijina ya salaci gawata, ina so na haihu na samu ahali irin na kowa, ina so na zauna a kasata duk rintsi na kula da y'ayana na basu tarbiya, ina so na rayu da su har karshen rayuwata, kai a ganninka idan na fara biye biyen y'ayan mazan da suka sakeni na nemi Allah ya zuba ruwan sanyi a saman ALKALAMIN KADARRATA kuwa?, Zaman lafia nake nema, bana neman idasa lalacewa" Daga haka SHUWWAR ta yi shigewarta ciki da jakar kudinta a hannunta ta bar yayarta da binta da kallo baki a sake tamkar tashar anguwa uku sannan ta maido dubanta kansa da sauri jin wata murya garjejiya ya bude yana fashewa da kuka Ido suka zarro daga ita har Fauziyar sunna kallonsa yana zaune dangalgal yana fadin" Innalilahi wa inna ilaihi raj'une, leke leken abanmu sai da ya kaishi ya leko wannan yarinyar kuma ya aureta dan wulakanci sannan ya saketa? Gashi Allah zai kama shi a kaina bayan ni kadai Allah ya bashi d'a namiji na kamu da son abinda yake haramun a gareni koda ya bar duniya? Innalilahi wa inna ilaihi raj'une yanzu yanzu fa na ganta a gidanmu idona ya rufe a kanta ashe haramun dita ce Ita din? Aunty kun tabata Shuwwar ta haramta a gareni kuwa? babu irin sabanin bakin nan da malamai kan yi a kan wasu fatawowin ? Kun tabata harshensu ya zo daya a kan wannan lamarin? Ba abinda ya shiga tsakaninsu fa" Kallon junna suka sake yi a karro na ba adadi suka kuma kallonsa, gannin tsakaninsa da Allah kukansa yake ya saka aunty cike da tausayawa ta ce" Ka ga, ka daina kukan nan hakanan, ka tashi ka shigo ka zauna har a ga yaya garin idan kana iya fita sai ka tafi gida, kar ka damu Allah zai daidaita zamu tambayi malaman mu ji ka ji?" Kai ya ringa gyadawa aman bai shiga ba ya sheda mata yana iya yawo shi dan takardarsa ta likita da kuma wada aka basu yanzun a hannunsa take Sunna tsaye sai da ya fita sannan suka kalli junna Fauziya na fadin" Yaya zaki ce masa ya dawo bayan kin san wannan abun haramun ne kuma kin san ta san haramun ne ko daureta muka yi muka kaita zata kunto kanta ta dawo ta same mu, balema ta yaya hakan zai iya faruwa?" NAHIDT ta shiga takawa dan ta he ta sanyo motar gida sannan au rufe tana fadin" Ke baki ga zai sume mana ba a nan? Ni ba dan hakan zai gyaru ba na ce zamu tambayi malamai kuma ma ai ilimi fadi gareshi, ko waye kai ba zaka ce ka san komai ba a kan lamarin, idan fa akoy wata aya da ta halata hakan? Bayan wannan kawai dan dai gani na yi idan ya sume mana ina zamu iya shiga da shi ne a haka" Ita dai tana biye da ita ta bude mata gidan da kyau ta sanyo motar ta rufe suka rurufe ko'ina suka nufin falon Sunna shiga Fauziya ta sake ja ta tsaya ta ce" Kin ga, kin sha saka kila wa kala a kan maganarki ki dawo kanta, koda hakan halak ne ki ajiye maganar dan gidan mai shinkafa, kin ga mutun ne mai iyali, y'ayansa yawa ne da su a duniya, koda auren muka je wasu suka daura masu mun siyar mata walahar rayuwa, ba zasu taba karbarta ba koda bayan ran mahaifinsu, maganin kar a yi karma a fara , ki ajiye kwadayin hakan gefe mu fuskanci reality da sauki a garemu baki dayanmu" NAHIDT ta ce" to uwata, na ce to uwata Fauziya,, na kula du kun daukeni a wata dakikiya ko wata kura, na ce maku na bar maganar ko?" Fauziya ta tabe baki ta yi gaba a ranta tana ayana' da ace ban san ko ke wacece a kan maganar son farantawa IBTISAM bane da sai ki fadi haka, ke burinki wani wanda zai sota a haukace kamar wannan saurayin, wanda koda ya ji menene sana'armu ba zai gujeta ba ki aura masa ita, bayan idan har muka yi haukan kaita gidansu yaron nan soyayar sai ta dawo ta zama kiyayar da kare ba zai iya sinsinawa ba, baganin kar a yi kar a fara' __________________________________ Aikin da suka wuni yi, suka kuma raba dare a kai ya saka shi magana yana lumshe ido tamkar wanda ya yi marisa Wayar dake kange a kunnensa ya sake saurarawa yana jin muryar mahaifiyarsa dake magana cikin hawaye wanda hakan ne ya saka shi ajiye komai ya masu alamu ya shiga ciki A hankali ya kai zaune bakin gadonsa muryarsa a shake dan ya wuni yana ihu da bakinsa ya ce" Kuka kike yi?" Shiru ta yi tana hadiye kukan dake tukota hakan ya saka shi fadin" Mamah, kin san irin ilar kukanki a kaina fa, saboda Allah dan kawai na saki mace sai ki yi kuka?" Yanzun kasa rike kukan ta yi tana fadin" Kawai ne? Sakin macen na ce kawai ne? Ana cewa kai ta haka hau ya shigeka auri saki shin gaskiya ne? Yaya kake so rayuwa da mace wace zata zamto ta amsa dukan komai a kan daidai bayan ita din da kanta an hakiceta ne da kashin hakarkarinka dake tankwashe? MUHAY daga kara siga a tea?" A hankali ya ringa murza hannunsa ya ce" Ba iya shine damuwar ba " Mamansa ta ce" Mecece damuwar?" A hankali ya ce" Nikakiyar kwalba ce ta zuba mij a tea ba siga bane ya yi yawa" Sai da mahaifiyarsa ta mije tsaye a zabure tana fitar da idannuwanta ta ce" Ka ga, kar ka fadi haka dan zama da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188