Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 79

Chapter 79

Mage Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

ta ji wanda ya aureta nan fa hankalinta ya k'ara tashi idanuwanta suka rufe ta ko wace hanya neman abinda zata lalata lamarin take, shine ta ringa tak'ale tak'ale ganin dai b'angaren Zahrau yarinya ce mai matuk'ar biyayya da matsanancin kamun kai, hakama mahaifiyarta sai kawai ta shiga yada masa magana cewar yanzu da sarkin ya ji ya aikata haka yaya za'a yi ya so had'a zuri'a da shi? Shine fa shima ya ce da ita "In banda abinki Mardiya ni kuwa na had'a da ke?" (Wato idan baki ya san abinda zai fad'a bai san amsar da za'a bashi ba) shine fa ta ringa fad'e fad'en maganar da idanuwansa suka rufe ya wan wanka mata mari domin fadi take" yanzu haka ba ita kad'ai bace shegiyar har sauran duba da irin yanda suke da halayya na shegu." Kamar wani wanda shege yake da halayya tasa daban, hakan ne ya saka Abih hankad'ata yana nunata da yatsa ya ce ta daina sheganta masa y'aya. Sai aka yi rashin sa'a ta kaiwa madubi duka, dama abinda zai kaita gidan sarki take nema sai kawai ta fad'a motarsa ta nufi gidan sarkin, tun da aka fito daga sallah ta tsaya a hanyarsa dogarai na kakarewa aman sai da ta yi yanda ya gane itace kafin ta fasa kuka ta yi hanyar b'angaren Anmy. Burinta ta fasa wannan sirrin y'ayansa su san abinda ya aikata, ta wanzar da tashin hankali tsakaninsu da mahaifinsu da su kansu. A hankali Anmy ke girgiza kanta kafin ta ringa furta "Innalilahi wa inna ilaihi raj'une." Da sauri ta shiga tatara k'annanun da su suna cike da tsoron ganinsu zaune gaban mai martaba dan su tsoronsa ma suke, sai Nusaiba dake ta mak'alar wuyan DAYABU tana wasa. Anmy du ta tattara su ta tura su ciki tana jin kamar juwa zata kifata da k'asa. Shi Kansa sarki sai ya sada kansa k'asa yana jin yanda kansa ke sarawa, ayau yana tare da b'acin ran da wannan fitinaniyar ta haddasa masa, sai ga wani gagarumin da ya tabbata Anmynsa sai ta shiga matsanancin tashin hankali, uwa uba Abih. Abih gaba d'aya jikinsa ne ya ji ya fara masa wata mijirya kafin ya d'ora hannunsa daidai zuciyarsa ya rintse idannuwansa wasu zafafan hawaye suka shiga biyowa gefen kumatunsa. Anmy ta sada kanta sai kawai ta fashe da kuka tana girgiza kanta tana b'oye fuskarta dan kunyar da take ji da irin maganar Mardiya. Baki d'ayansu hankalinsu ne ya k'ara tashi, hakan ya saka du suka rasa ina zasu nufa, wajen Anmy din ko wajen Abih? Da rarafe wa'inda suka fi kusanci da Anmy suka yi kanta suka ruk'unk'umeta, wa'inda suka fi kusanci da Abih kuwa Ummukulsum ce da Dayabu suka yi wajensa da Nusaiba suka had'e a jikinsa. Mamakin hakan ya saka Anmy d'agowa hannunta na rawa ta kai dubanta wajen SHAHEED ta ga kansa a sade, aman ya damk'i sandar dake kusa da k'afarsa da damk'a mai tsananin da ya hadasa jijiyoyin hannun nasa k'ara yin tsaye rad'o rad'o. A rikice take tatab'a jikinsu ta shiga fadin" baku yi mana fushi ba? Wallahi zan fad'a maku yanda aka yi, kun san k'adarar bawa bata fice shi kar ku yiwa mahaifinku da ni kaina da na taya shi b'oye sirrin nan fushi." DAYABU dake dafe da hannun Abih wanda ya dafe daidai zuciyarsa muryarsa na rawa rawa ya ce" ABIH, kar ka kashe kanka a irin wannan lokacin da matarka take son tona asirinka dan manufarta da mu kanmu bamu sani ba, Abih mun san da maganar nan dan girman Allah ka sassauta kar ka had'iyi zuciya domin idan ka mutu mu mukai asara ba ita ba." UMMUKULSUM ta ririk'e hannayensa tana dannawa ta ce" Abih zafi nan ke maka? Idan yana zafi mu je asibiti, Abih wallahi wallahi bama jin kunyar ubanmu ko haushinka domin a haka muke son ka." NAJEEBA ta k'ara rik'e Anmy tana b'oye fuskarta a jikinta tace" Anmy, meye na kukan? Kanmu aka fara ko kanmu za'a rufe?Anmy, koda mu dukanmu ne shegun shine aka ce zamu zo mu shak'e maku wuyan a kan me hakan ta faru? Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, Anmy ba shege bane abin gudu, d'an halal d'in aman mai halayan shege! Anmy, ai ba daga yannayin da aka haifeka kake nuna halaya ba, halayanka na nuna wanda ya baka tarbiya." "Anmy, kowani tsuntsu kukan gidansu yake yi! Koda dubu ya tara mu ubanmu ne, babu wata hallitar da zata zagar mana shi bamu sauke hak'oranta k'asa ba na rantse!" Ummulkhairma kukan take tana kara share hawayen Anmy ta buda bakinta ta ce" Anmy, ku daina kukan nan haka, kin ga fa Abih sai rike daidai zuciyarsa yake Najeeba ta saketa tayi wajen Abih ita ma ta d'ora kanta gefen k'afarsa tana jin kamar ranta ne ake wasa da shi, irin yanda iyayen nata ke zubar da hawaye sai ta ji tsoron Allah ya k'ara shigarta, wai kunyar duniya kennan, duniyar ma yayanka, ina ga kunyar Allah? (ALLAH, ALLAH, DAN GIRMANKA DAN SOYAYARKA DA FIYAYEN HALITA ALLAH KA SHIRYE MU, KA YAFE MANA, KA SA MU GAMA DA DUNIYA LAFIA, KA RUFA MANA ASIRI DUNIYA DA KIYAMA). Anmy da Ummulkhair ma da rarafe suka k'arasa wajen Abih, Anmy ta d'ora hannunta inda hannunsa yake tana hawaye tace "Ya isa, daga yau nauyin sai ya tafi ya baka lafia, yaya sun ji, sun sani sun sani." Sai ta had'e kanta da su suma sunna ta hawaye, shi kuwa da hannunsa yake daddab'a su yana jin wani irin a cikin ransa. SHAHEED kuwa abu d'aya ya hana shi tashi daga zaunen da yake shine shara'a, ya hau kujerar nan ne dan ya yi shara'a tsakaninsu tana zaune ta kawo k'ara ne, du irin kukan da mahaifiyarsa ke yi tamkar ana narka dalma ne ana zuba masa a k'irjinsa. Mardiya kuwa baki da hanci duka a bud'e suke ta yi wani fik'i fik'i tana ganin abin na neman juyewa a kanta. Anmy dake kuka tayi saurin d'agowa, hannun Dayyabu ta damk'o sannan ta damk'o na yayanta tana hawayen nan ta ce "Insha Allahu ba zamu yi kunya ba, insha Allahu Allah zai yi ta rufa mana asiri." A hankali ta kuma fad'in" *YAYA, DAYABU, SHIN ZAKU BAIWA MAI MARTABA AUREN Y'ATA?* *INA BARAR AUREN YARINYATA WA SARKIN DAMAGARAM, INA BARAR AUREN Y'ATA WA YARON KA*?" Ta karashe tana mai hade hannayenta da nuna Abih. Tunda ta fara neman auren ya d'ago da rinanun idanuwansa ya tsura mata daga ita har yayan nata da kuma y'ayan nata, suma y'ayan mata biyu da suka yi saura sai ya zamana kukan nasu ya d'auke d'if sai kallonta da suke da kallo irin na son ta idasa maganarta. Anmy ta k'ara kamo hannun Abih na dama tana mai k'ure shi da kallo, gwara a yita ta k'are, gwara ta nunawa Mardiya a lokacin da ka so wulak'anta bawa Allah kan rufa masa asiri, gwara ta fad'i muradinta idan ya so ko wace wace, idanuwanta a kansa, su kuwa idanuwansu a kanta inda zuciyoyi suka shiga bugawa tamkar zasu b'allo su fito daga k'irjin da dama a wajen. A sanyaye tace " _Idan kun yi comment zafafa, zaku samu zafafa🤣, wasan fa yanzu ne ya fara._🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻 *MAGE* _(Mai kwanciyar d'aukar

Table of Contents

Chapters

191 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191