Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 67

Chapter 67

Mage Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

hannayensa aje saman kansa muryarsa na rawa ya furta" innalilahi wa'inna ilaihi raj.une, hasbunnalahu wani'imal wakim aya ta tabbata a kaina ni MUTALAB gashi, abinda na aikata ya kamo ni da wuri haka a kan yarinyata." Sai ya fashe da kuka yana kallon yanda D'AYABU ya tsurawa sarki ido kamar wanda ya suma a zaune. Da sauri Anmy dake kukan itama ta kaleshi a firgice jin zai tona asirin da suke lullub'ewa kansu da k'afarsu, zai tonawa kansa asiri a cikin irin rud'anin nan da suke ciki zai k'ara masu wani. Duban da Ummu ke masa ne ya saka shi k'ara sada kansa yana hawaye Ummulkhair ta kalli Najeeba wace ita ma ita take kallo kafin Najeeba ta bud'a bakinta a hankalΓ¬ tana kallon Ummulkhair tana dan yatsine fuskarta tace" eyah, eyah, yau kin yarda da ayar tambayar da na d'ora a kan maganar da Abih kan fad'a wani sa'in?" Maida dubanta tayi wajen Abih a sanyaye ta furta" *ABIH, WACE AYA CE TA TABBATA A KANKA?* komawa sarki yayi ya jinginar da bayansa jikin kujera yana lumshe idannuwansa, ta faru kuma ta k'are, rikicin cikin gidansu zai k'ara kunnuwa a yanzu, ya tabbata wani tashin hankalin ne zai k'ara kunno kansa hakan ya saka ya idasa had'e fuskarsa da dukan wani abu wai shi annuri ya lumshe idanuwansa a lokacin da Anmy a firgice ta kallesu tace "... Happy juma'atπŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ» *MAGE* _(Mai kwanciyar d'aukar rai)_ πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ» *Na* *SAJIDA* πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝 β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ 27 A firgice, a rikice, a tsawace Anmy ta ce" yaya muna cikin wannan tashin hankalin zaki yi mana wata tambaya kina mai kokarin tirke mun tamkar kece uwarmu mu kuwa y'ayanki? Baki daya yan matan sai abin ya basu mamaki, yannayin Anmy din ya saka jikinsu ya yi sanyi harma du suka zuba mata ido da wani irin duba na mamaki Anmy ta kawar da kanta tana jan hancinta tana kara rintse idannuwanta da sukai mata luhu luhu ranta hade ta ce" ku tashi ku je dakin ku Jiki sanyaye du suka mimike, Najeeba ta kara waigowa ta kalli mahaifinta ta ga kansa a kasa sannan hannayensa sai rawa suke, ta kai dubanta wajen yayansu ta ga shima kan nasa a sade shi kuwa kuka ne yake a hankali ta saci kallon mai martaba ta ga ya yi wata kwonciya a jikin kujerar ya daga kansa sama idannuwansa lumshe rawanin dake kansa ya kara fadi sakamakon yannayin kwonciyar nasa, shigar alkyaba ne a jikinsa mai ruwan duhu wace ke da igiya wajen wuyanta, fari kal din hannunsa daya ne a waje yana rike da sandar girmansa dake ajiye a kusa da kafarsa, sai dayan dake dafe da gefen zuciyarsa Da sauri ta cire dubanta a kansa ta juya da wani irin sauri ta bi bayan yan uwanta Sunna shiga da sauri Ummulkhair ta zube a kasa tana mai dora hannunta saman kanta tana dubansu a rikice ta ce" shin kun fahimci abinda na fahimta? Kun gane cewar akoy wani gagarumin sirin dake damun mahaifinmu wanda da alama mahaifinmu ya shafa wanda nake kyautata zaton idan har ya fito fili mun kade? Najeeba ta jefar da iPhone dinta saman kujerar dake ajiye ta cire alkyabar jikinta ta jefar ta zauna a kusa da Ummukulsum ta shiga cakuda gashin kanta Dagowa ta yi da wani irin yannayi ta ce" aya ta kasance a kansa da wuri? Bai fadi haka ba sai da ya ji cewar wannan tsautsayi ya afku da Ummu? Me ke faruwa da mahaifinmu? Wace aya ce wannan ta kasance a kan ubanmu? Ummukulsum dake share hawaye itama ta budi bakinta a hankali ta ce" sai jake jin tsoron abinda zuciyata ke fada min, sai nake jin tsoron abinda nake tunani Ummulkhair ta ce" me kike tunani ummu? Ummu itama ta dora hannunta a kanta ta ce" sai zuciyata ke ce min bayan mahaifiyata mai amsar kudin zina ce mahaifinama ya taba fadawa wata Da sauri Najeeba ta matso kusanta tana daga hannunta da ihu ihu ta ce" ke ke, yi min shiru, walahi zan tsinka maki mari idan kika fadi cewar Abih ya taba yiwa wata fyade Ummulkhair ta shiga yarfe hannayenta tana fashewa da kuka ta ce" Najeeba ai ba haka ta fada ba, abinda kike tunani ne kika fada kuma nima abinda nake tunanin kennan innalilahi wa'ina ilaihi raj'une me ke faruwa da mu? Itama Najeebar baki daya kafafuwanta ne suka gaza daukanta Tana kokarin zubewa kasa Dayabu ya shigo Da wani irin sauri ya karaso ya tareta a jikinsa suka kai kasan tare Da rarafe sauran suka karasa wajensa suka rungume shi sunna kuka baki dayansu Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, yake maimaitawa hankalinsa a tashe ya shiga fadin" tabas kadara, mumunar kadara ta faru da kanwata, sai nake jin ba wanda ya kaini jin ciwo duda irin yanda aka fada min lamarin cewar ba da son ransa ba, duda na san Allah ya kadarto hakan, sannan har an yanke hukunci zai zama mijinki aman zuciyata ta kasa daina hawaye Tsoro nake ji , walahi tsoro nake ji Idan ita ummu ta faru da ita a wajen mutunci wajen da aka isa a tankwasa karfe komai taurinsa ku fa? Shin wace irin kadara ce ta afkawa mahaifinmu ya aikata mana haka? Da sauri Najeeba ta dago kanta tana kallonsa DAYABU da hankalinsa ke tashe ya shiga fadin" ba zan iya kuma zuba maku ido kuna yawo haka ba, du ku fitar da mazan aure a cikin manemanku a yi maku aure ku tare a gidajenku hakan zai saka mani nutsuwa a cikin zuciyata, walahi idan ayar nan ta kuma kasancewa a kan wani a cikinku bana tunanin zan iya yafewa Abih! Lebunanta ke hadewa da junna sai jimkesu take tana kara budewa A rikice ta ce" me me ya yi ne wai? Me ya yi? DAYABI ya sasauta masu rikon jin du sun dago shi suke kallo Kansa ya sada ya kasa magana hakan ya saka Ummukulsum dora hannunta a kai ta shiga zunduma ihu tana son mikewa ta yi burgima ko zata ji sanyi, cikin muryarta take fadin" shikenan uwa karuwa uba karuwi ko dai ni shegiya ce ban sani ba? NAJEEBAma dake kuka tana kallonsa ta ce" yaya waye shege a cikinmu? Ummulkhair kam sai ta kame, gaba daya ta kasa kuma motsa hannayenta tambayar da yan uwanta ke yi take jiran amsarta Hannunsa ya saka ya rufe bakin Ummukulsum sannan ya ringa bin Najeeba da kallo wace ta zama uwa wata wada ke son tashi sai tsale take tana kai kawo sai kuma ta tsaya tana kallonsa gashi kanta baki daya ta balbaza shi hannunsa ya saka ya jata kasa da karfi hakan ya sa ta yi wani irin zama dabar a gabansa gabanta na yi mata wani irin tsalen albarka kamar zai bale ya fito daga kirjinta Wayarsa ya dauko ya shiga galeri Hoto ya fitar saman wayar tasa ya mika masu Har rige rigen amsar wayar suke suka tsurawa hoton ido Yannayinsa a kansu ya ce" sunnanta *HUWAILA* , sati daya ne tsakaninku ita da Najeeba, Tana nan garin zaune gidan kannin mahaifinta tana karatu a lycee Du da iein tarin kamanin da take kamar

Table of Contents

Chapters

191 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});