Chapter 178
Chapter 178
dafe goshinsa da wata irin juwa dake son maka shi da kasa ya juya mata baya kansa na sara masa, a hankali ya shiga cira kafarsa yana neman hanyar da zai fita a dakin, baki daya jikinsa kuma rawa yake masa Bata dakatar da shi ba sai hannayenta da ta harde a kirjinta tana mai binsa da kallo har sai da ya bacewa ganninta sannan ta saki dan murmushi tana share hawayen da ta yi forcing ta fitar a gabansa ta karasa gaban madubin nan ta zauna A hankali take tsara kwaliya a fuskarta a kasan zuciyarta kuwa fadi take 'Zan zame maka mace wace ta fi kowace mace rauni da zubar da hawaye a gabanka, SHAHEED ba zan yarda ka cin min ina zaune ba' Da kallo Ummulkhair dake zaune goye da NUSAIBA a bayanta wace ke rigima ta bi shi da kallo domin ita daya ce a falon, itama an sakata zama ne dan ta duba Mardiya da aka gama shaidawa cewar gatanan zata zo domin abih ya yi kiran Ammi ya fada mata cewar Mardiya ta yi rantsuwar daga gidan cen zata zo wajenta Kanta ta sada da sauri sakamakon ido hudun da suka yi tana dan kara jijiga yarinyar, sam basa jin nauyin goyanta su kam, kansa ya cire ya fice a falon Tana shirin mikewa ta shige ciki wajen Najeeba ta ji an banko kofar an shigo falon Mikewa ta yi a tsorace tana kallon wace ta shigo a haka din MARDIYA da kanta ke hayaki sakamakon labarin da aka kawo mata cewar Abih ya gyarawa UMMU gidansa dake Jeune cadre ya zuba mata kayan alatu tamkar gidan zai tsage dan kaya, ga wani irin fita daban da ya yi a anguwar, bata yarda ba sai da ta je ta ganewa idannuwanta duda mai gadi ya hanna mata shiga aman daga inda take ta ga abinda ta gani shine ta koma masa ta same shi gadan gadan da tashin balagar rashin kunya, ya mata banza shine ta ce zata zo ta sammu Ummun su yita ta kare, ba zata amshe mata miji ba bata isa ba tsohuwar banza kawai Gadan gadan ta idasa gaban Ummulkhair ta ce" Ke ina tsohhuwar guzumar uwarki take? " Ido Ummulkhair ta zarro tana kallonta, ita dai bata da fada irin nasu, bata iya hayaniya sosai din nan ba, Ummukulsum ta fi ta iya maida martanin rigima, har solofiyo suke ce mata ita da Zahrau, hakan ya sa ta dan rike kafar NUSAIBA dake daidai cinyarta tana kallonta ta ce" Wace haka kuma Mardiya? " Mardiya ta matso da wani irin balaki ta hankadata, bata shiryawa gannin hakan ba hakan ya sa ta je baya gaba dayanta ta fadi da bayanta saman Nusaiba jikin karfen kujerar falon Wani irin tartsatsin ihu Nusaiba ta saki kafin ta dauke dif Da gudu suke firfitowa daga kofa daban daban A guje suke nufo yar uwarsu dake yashe a kasa tana ta kokowar son kwonto Nusaiba da ta kara nauyi a bayanta sannan gwuiwar hannunta na zubar da jinni Da wani irin gudu AMMI ta idasa wajen ta shiga son kama su hankalinta tashe bakinta ya kasa furta komai Da wani irin sauri UMMU ta ture NAJEEBA dake son karasawa itama aman sam bata iya gudu ko sauri ba hakan ya sa take wata tafia tingil tingil hankalinta tashe Mardiya dake tsaye idannuwanta rufe ta ce" Baki dayanku bakinku a hafe ko? Bayan auren cin amanar da son zuciya kuma shine za'a kaita sabon gida tana tsohuwa ni a barni a gidan da yara suka tashi suka lalata? Walahi ban ga yar iskar da ta isa ta shigar min gidan miji ba! " Tas , fuskarta ta amshi wani irin fitinane, mahaukaci, zazafan marin da ya sakata kwala ihu ta juyo tana kallon kantamin hannun da ya sauke mata biyar Bai wata wata ba ya kara dauke fuskarta da wani tsadaden, wulakantace, fitinanen marin da ya sakata yin luuuuu cike da mahaukacin mamaki da al'ajabi ta kwala ihu ta ce" Kan uban cen kaya sa, ni ka mara? Ashe kuwa zaka iya marin Mutalab da MARIAM? zaka iya marin uwarka mahaifiya? " Da wani irin hauka hauka ya shiga kunce belt din dake daure a kugunsa , gannin haka Najeeba, da Ummukulsum suka rigaye shi afka mata, kan kace meye wannan kanwarsu bakuwarsu da yake itama jinnin shuwan ne ke yawo a jijiyoyinta ta afka masu, yaren suka ringa neman wajen kai mata duka Ummu ce ta daka masu wata irin tsawa mai hade da gunjin kuka, AMMI ta dago da NUSAIBA a hannunta wace hannayenta ke yin lagai lagai muryarta cike da kuka ta ce" Ta kashe ta, ta kashe yarinyarta ta cikinta, ta kashe Nusaiba! " Gaba dayansu ne suka idasa juyowa wajen iyayen nasu a tare, cikinsu mutun uku ne suka zube a summe sakamakon gannin irin jinnin dake zuba daga keyar NUSAIBA, Abih da shigowarsa kennan a hankali ya silale a wajen zaune dabas ya dora hannayensa bibiyu Yaya Dayabu ya daga kafarsa ta hagu ya fara takawa tana masa nauyi ama a haka ya ringa janta har ya karasa wajen AMMI dake kuka ido rufe tana maimaita innalilahi wa'ina ilaihi raj'une A hankali ya dora hannunsa wajen jinnin yana kallon yanda idannuwan yarinyar suke kakafe sannan jikinta ya dauki wani irin sanyi harta da fatar jikinta ta yi fayau Da sauri ya saka dayan hannun nasa yana gurgusa gashin kanta , muryarsa hade da wani ihu ihun kuka yake fadin" UMMU, wayo mun shiga uku, Ummu ku tare jinninta kar ta mutu, Ummu wayo ta kashe mana kanwarmu, ku kama mana kar jinninta ya kare, wayo Nusaibata, ku tare jinnin nan ya bar zuba kar ya kare AMMI, wayo Abih, Wayo Ummulkhair, NAJEEBA, wayo Bilkissu, wayo Najeeb zo ku tare jinnin kanwarmu na zuba daga kanta" UMMU dake kuka ta saka hannayenta tana janye nasa, muryarta a ciki dan tsabar kukan da take ta furta" innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, Allah ka yi mana maganin masifar da ta fi karfinmu, Allah ka jikan yarinyar nan, ka sa ta huta, DAYABU ka bar dannawa Nusaiba ta rasu fa baka gani ne? " Qi kamar wada ta kara rikita dakin, gaba daya wa'inda ke jijiga wa'inda suka summanma sai suka kara rikicewa, Najeeb kam ya rukunkume mahaifinsa ya cusa kansa cikin kirjinsa yana kuka dan shi tsorata ne ya yi da gannin jinnin dake fita daga kan kanwarsa wace shekara daya ce tak tsakaninsu yanzu haka da kokowa suka rabu ta fara rigimar da ta zame mata jiki kwana biyun nan, domin haka kawai zata kama kuka tana dora kanta a jikin du wanda ke kusa da ita, kuma jikinta lafia kalau ba rashin lafia ba ba komai ba, hakan ya sa Ummulkhair ta goyata suka fito falo shi kuwa ya kwonta ya shiga baci Wani irin ihu DAYABU ya yi, a lokacin da NAJEEBA ta fashe da wani irin kuka hannayenta duka biyu saman kanta tana nuna Mardiya da ta yi wani irin wuri quri hannayenta duka biyu a saman kanta tana maganar da ba'a jin me take fada, ama da alama ta zauce ne dan kuwa magangannu ne take ta saki tana kuma kallon du wani mahalukin dake wajen Kukan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188
- 189 Chapter 189
- 190 Chapter 190
- 191 Chapter 191