Chapter 123
Chapter 123
ina hura hanci rai bace da kudadena da katina na banki na tafi na bar kasar haihuwata" Sasautawa ta yi sakamakon hawayen da ya fara zubo mata daga gurbin idannuwanta A hankali ta ci gaba da fadin "sai dai kashh, da na sani, da na kawar da kaina, na hadiye wulakanci da neman fitina da tashin dukiya da irin yanda kudi ke dukan kansa ke saka shi aiwatarwa a gareni na rungumi yan dagwai dagwai dina na rayu da farin ciki, domin kuwa daga bakin lokacin da na sauka, na fara kokarin ciyar da kaina, tufatar da kaina, neman abinda zan yi dan inganta rayuwata duk da tarin takardunna, da dukiyar da na tafi da ita ta gadona da iyayena suka bara min, sai rayuwata ta zamo wata sabuwar rayuwa mai cike da duhu duk inda na ga yaro ko yarinya sai na saki murmushi sai kuma hawaye ya biyo baya Idan na zo kwontar da hakarkarina wani sa'in idan nonona ya soke ni sai ki fado min a raina Nakan zabura ni kadai a dakin hotel dina ina jin kamar muryarki kina fadin *"MAMA, ZAN YI FITSARI"* Na rayu cike da burin zama wata abu, da son goge ku a rayuwata na manta da ku na sake wani auren na haifi wasun Sai dai me? Ashe na yiwa kaina mugun illah ta hanyar shakuwa da ku, Makwoncinmu daya A tsakiyarku nake kwanciya inai maku tatsuniya kunna hayewa jikina kuna kokoyi, Idan kukai fada nakan ji hankalina ya tashi, zan saka ku shirya ta hanyar nuna maku ilar abin Na saka shakuwa mai tsanani a tsakanina da ku, da yayanku har ya kasance na zabi kulawa da yara a matsayin karatuna" Sosai take hawaye hakan ya saka ta saka hannayenta ta toshe bakinta dan kuka take son yi sosai Dayyabu kansa da yake mai saurin hawaye ne idannuwansa sun cika da kwalla, hakama sauran du hawayen suke zubarwa ciki kuwa Harda Najeeba dake hango duk abubuwan da take fada a zahiri kamar a lokacin komai ke faruwa da rayuwarsu Mikewa ta yi da sauri ta juya da nufin tafiya, domin ita dai da bakinta ba zata iya furta masu dalilin fushinta ba Karron da ta ci da shi ne ya sakata kokarin zubewa Sai dai bai bata damar hakan ba ta hanyar tareta sosai da hannunsa kafin ya maidota dakin da kyau kusa da yaran ya aniya zaunar da ita yana kallonta a sanyaye ya ce... 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻 *MAGE* _(Mai kwanciyar d'aukar rai)_ 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻 *Na* *SAJIDA* 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ 46 A sanyaye ABIH ya ce" ina zaki je bayan ina jiran wannan ranar shekara da shekaru dan na baiwa Najeeba amsar tambayarta wace du sauran yan uwanta ina iya basu amsa kai tsaye na dalilin da iyayensu suka bar gidana aman ita na kasa bata amsar?" A tsorace take kallonsa, bakinta na rawa ta ce" amsar? Wace amsar kake tunanin zaka iya fada masu?" Abih ya dan yi mata murmushi mai ciwo a hankali ya furta" haba *SIRRINA*, baki san sun san wani *Sirrin* rayuwata mai tsanani kuma suka hakura suka ci gaba da mutuntani ba? Yaya kike so ki ci gaba da fuskantar irin wannan shariya da abubuwan da y'arki kwalin kwal ke maki a kan namijin da ya kuntata maki? Kina da bukatar samun girmamawa, soyaya, kallon daraja daga wajenta, tabas kina samu daga wajen yan uwanta aman ita din ke kika haifeta fa? Dan Allah ya isa haka, ki barni na fada" Har bakinta rawa yake ta furta" aa, ba ruwanka da abinda ke damuna, ni ban rokeka fadin wannan abin ba, ina fadawa Allah idan lokacin ta dubeni ya yi zata dubeni dan kanta" Murmushi ya yi yana dubgure kanta ya karasa da sauri ya zauna gaban y'ayam nasa ya ce" ba ga irinta ba, ci gaba zata yi da boyewar, tana kakare laifina, ita dai a haka take so ta kare?" Najeeba, na auri mata goma sha bakwai a rayuwata Cikinsu ba wace ban haihu da ita ba, kuma ba wace ta ga girman y'arta take fecewa Na birne mace uku a gidana wa'inda suka rasu a hannuna, sauran goma sha ukun nan du rabuwa muka yi, banda mardiya ta sha hudu Najeeba, kamar yanda kuka sani, wasun dalilin na tarda su sunna dukanku ne, wasun rana tsaka zaku tubure da rigimar bakwa son su, wasun zasu nunan ba zasu iya rike y'aya birjik haka kawai bane, wasun zalamarsu ta saka, wasun kuwa sun aikata abinda ya hana min yafe masu ne ya saka ni rabuwa da su aman banda *NANA MARIAMA* Sai da ya kalli UMMU dake kallonsa da mamakin wai da gaske bayanin zai yi ya yi murmushi ya ce" aminiyar BILKISSU ce, wato Ammi dinku, ita ta yi mata gorancen aurenta, sun kasance masu raba ayya daya, sunna rike sirrin junnansu duda BILKISSU ta bata shekara UKU a haife wanda hakan ya saka idan ta yi niyar tsokanarta ko idan tana cikin yannayi na tashin hankali takan kirayeta AUNTY domin takan ce da ita "Bani da kowa sai Allah sai ke" Min sasanta kanmu da NANA MARIAMA a lokacin da nake amsa sunnan Yaro da kudi, ina jin wani irin tashen kudi dake daukana yana yawo da ni yana dadani da kasa Na tara y'ayan sai dai ba wai takamaiman su din ne a gabana ba, ina dai da wani irin kaunarsu a zuciyata wada ke sakawa idan aka yi katari na dan zauna na ji damuwarsu to fa ko wace iri ce zan dage na magance masu banda zama da su da kukawa da tarbiyarsu da kuma gane irin ilar sakin iyayensu da shigowar bakin fuska a matsayin sababin iyayensu ke janyo min Sai da na auri NANA MARIAMA na fara gane meye ma'anar zuri'a, Tanadinta zuri'arta, burinta zuri'arta, farin cikinta zuri'arta, abokannanta zuri'arta a lokacin ta shigo ta tarda mahaifiyar Ummukulsum da tsohon cikin Ummukulsum Zamansu bai yi nisa ba na sawake mata a lokacin da ta haifi yar jaririyarta sakamakon gannin itama ta haihu yanzun zata fara ware nata daban sauran daban wanda na kamata da hakan sau uku karshe dai na sawake mata na ci gaba da koyon rayuwa a wajen NANA Mariama Fadace fadace, rashin zaman lafia, rigingimu na tsakanin miji da mata kan hada mu, sai dai wani ikon Allah daga lokacin da zan tabo ku zata zube a kasa gwuiwoyinta a kasa tana kuka ta ce" ka yiwa Allah ka yiwa Annabi muhamadu salalahu alaihi wa salam ka barni na huta, ka barmin yara su huta, kai baka gannin yarintarsu, soyayarsu, karfin zuciyarsu? Kar ka hargitsa min tarbiyarsu ko ka birkita min zaman lafiyarsu, yaren nan sune farin cikina, kai ka san ba dukiyarka ko kyanka ya saka nake hakurin zama da kai ba sai dan yaren nan" Abinku da wanda shedan ya rigaya ya buga min ganga sai na sheke da daria sai na kalleta a kaikaice na ce" ku ji shishigi malan, yara ina ruwanki da su? Su tashi a tashama mana na san tarbiya ta Allah ce ba ta wani ba, dan haka idan kin gaji da zama da ni ki kama gabanki!" Zata kawar da kanta, ra mike
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188
- 189 Chapter 189
- 190 Chapter 190
- 191 Chapter 191