Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 121

Chapter 121

Mage Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

amma ya ki zuwa, gashi ni ba sakina ya yi ba" Dan saurarawa ta yi ta dan dago dan gannin shin tana sauraronta? Gannin Ammi na kallonta da kyau ya saka ta ci gaba da faɗin "Idan laifi na masa tsakanina da shi ai ya ci ace ya yafe, idan kuwa fadana da yara ne ba ruwansa ya fita a ciki domin tsakanina da su ne" Da mamaki Ammi ke kallonta a kasan zuciyarta kuwa faɗi take 'Ikon Allah, wai ita a gidansu ba'a fada mata ka so mutun ka so d'ansa ba?' Dubanta ta kuma kai wa wajen Ummu dake dan jijjiga Nusaiba, ko nauyinta bata ji haka take jibgata a baya ta yi ta jijjigawa, a yan kwanakin da ta yi da yarinyar ta matukar sabawa da ita domin yanzun Mama sak take kiran Ummu da shi kamar yanda sauran yaran ke faɗa. Mikewa ta yi ta nufi wajen Muryarta a dan dake ta ce "Sannu fa?" Dakatawa Ummu ta yi ta juyo daga wajen yaran dake ta mata surutu Ido cikin ido suka kalli juna, ita dai bata santa ba, sam bata taɓa haɗuwa da ita ba, ko hotonta bata sani balle ta shaida ta. Ba wata shigar firgita mutum ce a jikin Ummu ba, domin riga doguwa ce sakakkiya baka a jikinta Sai dai yannayin tarin kamalar da fuskarta mai cike da yalwataccen gashi da ɗan murmushi ya saka Mardiyya jin shakkun yi mata magana a gatsai gatsai Dan haka sai ta dan kakari murmushi ta ce "bani ita na rarrasheta ko zata yi shiru? Kallon da Ummu ke mata dan ta fahimci ko wacece ita, sarai ta san matar ta hoto amma ko ita bata taba haɗuwa da ita gata gata ba A hankali ta ringa kunce goyon kafin ta juyo da Nusaiba ta mika mata ita Da farko idon yar a rufe yake, hakan ya sa ta yo lufff a jikin Mardiyya, sai da Mardiyya ta ce "A'a, bata da lafiya ne? Jikinta zafi haka me yake damunta?" Jin muryar ya sakata buda idannuwanta Kallonta take kafin ta fara rigimar sai ta koma wajen Ummu (idan baku manta na Nusaiba yarinya ce karama, ko a haka Mardiyya ta kasance mai yawan zaginta hantararta da yawan faɗa, a rayuwar yanzu ko ɗan naka ya mallaki hankalin kansa sai da addu'a da kawar da kai, bare yar yarinyar da ta samu mai rarrashinta da nuna mata soyayya hakan na iya haifar da son nisantar mahaifiyarta da ta haifeta, karamin abu ne hakan) Da mamaki ta kalli Ummu, da yanayin shashanci ta ce "ke ko har kin canza uwa ne haka zaki ringa kuka a hannuna?" Ummu kam wajen ta bari ta koma saman kujera ta zauna tana mai bin Wudiliya da kallo wace ke zaune tana bin kowa da kallo itama Wani murmushin ta yi ta kuma maida dubanta wajen yaran Da idannuwanta take gallawa duk wanda sukai ido hudu harara, sai dai a yanayin yanda ta lura sun rigaya sun hade kan nasu na iya shege wato kar wanda ya gaishe da Mardiyya? Sallamar Dayyabu ne ta saka su duban wajen Shine ya fara shigowa cike da yalwatacciyar fara'a a fuskarsa Bayansa wata yar budurwa ce kyakyawa fara tas , ta saka abaya baka har kasa ta yane kanta da mayafinta Du sai yaran suka shiga murnar zuwansu Zahrau ta mike tana yafa dan kwalinta cike da nuna kulawa suke yiwa budurwar yayan nasu barka da zuwa Kasa ta zauna kanta kasa tana murmushi tana dan murza yan yatsunta, shi kuwa yana zaune kusa da Ummu yana mata magana kasa-kasa, haka kuma kannansa duk sun zagaye shi ban da Zahrau da ta shiga hidimtawa bakuwar cike da fara'a Hannun Bilkisu ya dan doke ya ce" Mairama ki barni da tsegumi wai ba yayarku bace ku je mana ku tambayeta" Jin abinda ya fada ya sakata dan dago dubanta tun bayan gaishe su da ta yi Dan murmushi ne a fuskarta kafin ta mika hannu a hankali ta furta "Ku zo" Sai da suka kara kallon iyayen nasu kafin duk su yi wajenta Ai kuwa ta ringa cafe hannayensu suna gaisawa duk da ba sakin jiki suka yiwa juna ba amma fuskarsu da mawadacin farin ciki Baki ta tabe kasa-kasa ta ja tsaki sai kokowa take da Nusaiba dake son zuwa wajen Ummu Ammi ta kai dubanta wajenta ta ce "Mardiyya, barta ta je wajenta mana, mamanta ce fa, mahaifiyar Najeeba ce" Da sauri ta dago ta kai dubanta wajen Ummu, Sam Ummu bata kallonta, hasalima dariya take yiwa maganar DAYYABU na irin rigimar da suka sha kafin budurwar tasa ta yarda ta zo gaishe da su A hankali ta furta "Na ji dadin jin haka, hakan na tabbatar min da tarbiyyarta, har ma na ji ina zumudin kasancewarta matar yarona" Tana maganar tana kai hannunta gefen fuskarsa ta dan shafa a hankali sunna dariya a tare Wani irin abu ne ya tokare kirjinta kokowa take da abinda zuciyarta ke tambayarta, dannewa take dan kar ya fito fili tana kara kallon su UMMU da DAYYABU ga kuma AMMI dake ta sakin murmushi da alama ta manta abinda ya kawo su gidan ko meye. Zuciyarta ce ta ci gaba da fadin 'What? Meye wannan? Wani irin abu ne wannan? Ko dai yar uwarsu ce? Meye tsakaninsu mai karfin da take zaune rashe rashe a gidan Ammi haka? Goye da Nusaiba ga kuma yaran sai wani hira suke uwa wace ta haife su da cikinta?' Daga dogon corridor din dake hadawa da bangaren SULTAN iso ya ringa shigowa cikin maganar mutun kamar biyu Da sauri Ammi ta kai dubanta, hakama Zahrau da du wani wandake wajen Ita ce ta sanyo kai, cikin shigar da ta tafi da ita wato alkyabarta ce sai dai kamshin turaran ba wanda ta je da shi bane, kamshin turaran SHAHEED ne ya fara dukan hancin duk wani wanda ke wajen Da sauri yayunta suka yo kanta, domin ja ta yi ta tsaya tana mai jin kunyar kallon su ido cikin ido Wani irin farin ciki ne ya lulube zuciyar Ammi a lokacin da ta fahimci komai Ummu ta sadfa kanta tana murmushin cin nasara DAYYABU ne ya mike shima cike da farin ciki ya yi wajensu A hankali suka kamota suka nufo ciki da ita Budurwarsa da kallo take bin su, tabbas yau ta kara yarda da irin soyayar dake tsakaninsu, cike da mangari take dubansu, a ranta kuwa ji take inama ace sune haka? Ita bama yan uba bane aman ba wani kulawa da junna da suke da yan uwanta A ranta take jin zata dauri niyyar kusantar yan uwanta koda kuwa ba zasu kulata ba har su samu fahimtar juna Kanta a sade yake baki daya yau kunyarsu take ji, ji take duk sun gane abinda ya sameta hakan ya sa ta kasa hada ido da su sai kara sada kanta take DAYYABU ya ce "Ke wai menene?" Jakadiya da babar baiwar bangaren SULTAN ne kawunnansu sade JAKADIYA ta furta" Allah ya ja da rai , Allah ya taimake ki , Sarki na gaishe ki, yana mika sakon gaisuwa da godiya, yana neman afuwar jinkirin zuwan GIMBIYA" Ammi ta kara yin murmushi kafin ta gyada masu kai suka mike suka fice

Table of Contents

Chapters

191 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191