Chapter 66
Chapter 66
da tsiya ya kasance ka fad'a kan wace ba ita ba?" Dubansa ya kai kan matar tasa dake kukan ita ma cike da dana sani ya furta" Anyi haka? Mijinki ya zo maki kin fito da suturar da tayi kamanceceniya da ta baiwar Allahn nan? Idan waje ya ga kin nufa ina kika lab'e masa ya fito waje nemanki? Kina ganni ya aikata haka baki katse masa hanzari ba ko baki gani ba?" Fashewa tayi da kuka tana k'ara sada kanta muryarta na rawa ta ce" Allah ya huci zuciyarka a yi mana afuwa, a gafarta mana, a ji k'anmu, tabbas hakan ya faru daidai da abinda ya fad'a, kuma a lokacin da na zo fita lab'ewa na yi dan ina jin haushinsa ya hana min wasu kud'ad'e, dan ina so yana fita na koma na d'auka domin mun jima muna gaba tsakaninmu sakamakon mahaifiyarsa ta nunan cewa kar na yarda ya yi yan mata ko ya yi tarayya da 'ya'yan turawa a waje shi kuwa yayi budurwa shine ni kuwa nake nuna masa fushina ta hanyar hana masa abinda yake buk'atar." Sai kuma ta k'ara sadda kanta tana kukan da na sani da tarin nadama. Kansa yake girgizawa ya ma rasa me zai ce? A hankali ya furta" Ga irinta nan, ga irinta nan, kin yiwa sarakuwarki muguwar hud'ubar ita ma kar a mata kishiya ga inda abin ya kaiki, lalle ke ba uwa ta gari bace, ke ba mata ta gari bace sannan ke ba shugaba ta gari bace, tabbas kema hukunci zai hau kanki domin ba zan iya ci gaba da zama da ke a matsayin matata ta aure ba." Baki d'ayansu a zabure suke kallonsa sai a lokacin SHAHEED yayi gyaran murya yana kallonsa ya furta" Allah ya huci zuciyarka, Allah ya ja da zamaninka tuba muke." Baki d'aya suka ringa maimaitawa banda su NAJEEBA. Kansa ya k'ara sadawa ya shiga fadin" Tabbas wannan lamari idan ma da ganganci a ciki to fa zanen k'addara ce, abin ne ya zo a harhad'e, shi ga abinda ya fitar da shi daga d'akinsa ita ma ga irin lokacin da ta kai tare da yan uwanta suna shashanci maimakun su kasance a cikin bautar ubangiji!" Sasautawa yayi ya kuma d'auka da cewa" Tir da matar dake gudun shinfid'ar mijinta, tabas kina cikin tsinuwar ubangiji sannan kina da naki kason a cikin wannan lamari." Dubansa ya maida wajen yarima ya kausasa muryarsa ya furta" Tir da namijin da ba zai iya rige arzizimun wandonsa a lokacind a fitinarsa ke harbinsa ba!" Sai kuma ya maida dubansa wajen Gimbiya ya sasauta muryarsa ya furta" Kaico ga uwar da zata ringa shinfid'a hanyoyin b'araka a cikin ahalinta, domin kuwa wannan uwa ta d'auko hanyar tarwatsa iyalanta da al'uma mai yawa, dan kuwa mu dukanmu muna samun tarbiya ne daga iyayenmu, daga bakin lokacin da aka samu gurb'attaciyar tarbiya lamarin b'atanci zai yawaita a cikin al'umah." Sassauta muryarsa yayi yana kallon sarki ya furta" Rud'ani, tashin hankali ya hana min kallonsu a cikin idannuwa, sai dai ya zama dole zamu hau wata shari'ar a yau a wajen nan dan danne wata b'arakar, amar yanda na fad'a cewar a duniya baki d'aya babu mumunan sirrin da fitarsa ke haifar da mugayen sakamako irin sirin masu mulki da kuma manyan malamai da masu iko, akan d'auki hakan da fuska biyu, masu d'aukarsa da mummunar fuska ta hanyar kwaikwaya sukan yi yawa a cikin duniya baki d'aya, k'alilan ne ke yi masa kyakyawan fahimta har su gane b'atancinsa." Kuma kausasa muryarsa yayi ya furta" Ba'a kyauta ba, an tafka abinda Allah ya haramta, sannan an shiga hakin baiwar Allahn da bata ji ba bata gani ba." Shiru ya kuma yi kafin ya dubi wajensu. Muryarsa ya sanyaya sosai kafin ya furta" UMMUKULSUM, shin zaki iya jurewa, ki jajirce, ki d'auki hak'uri ki yafewa bawan Allahn nan duba da irin abubuwan da suka gabata da shaidar wace abin ya faru a sanadiyarta ? Zaki iya yafe masa har cikin zuciyarki? Ki tuna Allah na yafewa bayinsa masu yafiya ya Ummu." Kanta dake kife a jikin kafad'ar Najeeba tun daya kama k'afarta yana gunsheken kukan nan ta ji wani irin tausayinsa ya tsirga mata haka kawai sannan wani irin tsigar jikinta ta ringa tashi, bata k'arasa jin tausayinsa ba sai da ta ji kalaman mahaifinsa da kukan mahaifinsa da shi kansa. Gimbiya ce ta k'ara duk'awa tana kallonta muryarta na rawa ta furta" Ki rufa masa asiri, ki rufawa kanki Ummukulsum, kar ki manta kema mace ce, fitar sirin nan tamkar fitar da sirrinki ne, ki rufe shi dan girman Allah." Cire dubanta ta yi daga kanta, muryarta na rawa ta furta" Na yafe masa." Sai kuma ta fashe da kukan da ya saka Najeeba wace jikinta ya d'ume da zafi kanta na sarawa ita ma fashewa da kukan tana k'ara rungumeta, Zahrau kuwa ta zama wata mutun mutumi sai juya kai take baki d'aya ta rasa me take ji. Hamdallah yayi kafin ya maida dubansa wajen sarki a sanyaye sarki ya ringa sakin ajiyar zuciya, muryarsa a sanyaye ya furta" ina neman alfarma, ina neman alfarmar a bar min ita a nan gidan, ta yi istibra'i a d'aura masu aure, domin na rantse shi zai gyara abinda ya lalata." Daga Gimbiya har matarsa a tsorace suka kalli sarkin da ya watsar da su yana cike da jin haushinsu, sam tamkar basa wajen tun da ya masu tambaya yayi watsi dasu. Da baya ta kai zaune tana mai d'ora hannayenta saman kanta a b'oye, kishiyarta kuwa bayan tarin tausayin yarima domin yaron yana da mutunci sosai, sai kuma tarin al'ajabin abinda ke shirin faruwa, auren yarima da matarsa aure aka yi na zobe, yar k'awar gimbiya ta k'ud da k'ud wace ak'idarsu d'aya cewar ba za'a yi masu kishiya bace ya aura, hakan yasa Gimbiyar ke taya ta yak'in maganar kishiya sai gashi a yau abu biyu ya faru da su baki d'aya, wato wanzuwar *KISHIYA* a tsarin da basu ajiyeta ba. Kansa ya kuma sadawa yarima ya k'ara duk'awa shima yana rok'an hakan. Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya furta" zamu juya gida a jirgin safe in sha Allahu, zan yi kira na sanar da abinda ake ciki." A haka dole aka tashi, sarki na zaune saida kowa ya tashi sannan ya bi bayan Zahrau dake son shiga d'akin jikinta a mace. Hannunta ya kamo ya maidota baya A hankali ya sakata cikin jikinsa ya rungumeta yana buga bayanta kad'an kad'an kafin ya jata suka koma saman kujerar Sai a lokacin ta samu kuka ya kubce mata cike da tsoro take nuna masa ba zata iya zama ba yan uwanta a wannan gidan da ya gama tsoratata ba. Sosai yayi anfani da hikima ya ringa rarashinta har ta dawo nutsuwarta ta ringa sauke ajiyar zuciya da kansa ya mata alk'awarin zai nemi alfarmar malan ya bashi y'aya biyu k'annenta su tare da ita su tayata zama kafin a kawo mata Ummu. Da wannan ya samu ta kwontar da hankalinta kafin ya rakata har d'akin suka ci gaba da gabatar da sallah baki d'ayansu suna godewa Allah da irin wannan ranar. .................................... Zabura ya yi tsaye sai kuma ya yanke jiki ya fad'i zaune saman kafet d'in
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188
- 189 Chapter 189
- 190 Chapter 190
- 191 Chapter 191