Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 168

Chapter 168

Mage Book 1 Complete Hausa Novel 1,194 words 0 views Progress saved
Download Book

ce" ai ba'a yi wata ukun ba " Dan murmushi ya yi ya bata amsa kamar haka" na san da ba sai an yi wata ukun ba, kema kuma kin sani " Hakan da ya fada ne ya sakata da sauro ta daga kafarta ta bi bayan yar uwarta har kamar ta ci tuntube, shi kuwa banda murmushi ba abinda yake harda sauke ajiyar zuciya Sunna karasawa kofar baban falo ne suka samu sakon su dakata Mai martaba na zaune da iyalansa, su kansu na kofar basu san cewa ya shige tuni da yar bak'arsa ba. ......................................... Mahaifiyar Mardiya dake zaune a saman tabarmarta a waje sansaya tana kallon yayansu Mardiya da ya kawo mata maganar daura auren MUTALAB ta sauke ajiyar zuciya ta kai dubanta wajen da Mardiya ta mike tsaye lokaci daya, Sai da ta kara sauke ajiyar zuciyar takaicin halayan yarinyar tata ta ce" Masha Allah, Allah ya basu zaman lafia, Allah ya bata ikon kula da y'ayanta bisa amana, ai ka gani hakurinsa ya masa magani, domin kuwa a labarin da na ji a kan ita matar nan tasa sun yi zaman amana, halin rayuwa ne da kuruci ya raba su, kadara dai ta Allah, tunda yanzun ta dawo gare shi Allah ya basu zaman lafia " Cike da datako ta karashe maganar, danta na murmushi ya ce" bakima sani ba ina, sai kin ganshi, kina gannin yannayin yalwataciyar fara'ar kan fuskarsa zaki gane yana cikin farin ciki, tabas mace ta gari ita ce sila ta zaman lafia " Su kam hira suke, basu san irin kokowar da Mardiya ke yi da numfashinta ba, basu san ta mike ba, basu ma san ta dan matso kusa da su ba, sai Karan ihunta da zubewarta kasa ne ya ankarar da su halin da take ciki Da gaske ta summa, summa ta yi, bata numfashi, Hankali tashe mahaifiyarta ta ce" Alhamdulilah ala kuli halin😊 [3/31, 11:36 PM] BAK'A CE: πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ» *MAGE* _(Mai kwanciyar d'aukar rai)_ πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ» *Na* *SAJIDA* πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝 β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ 6 1 Cike da tashin hankali mahaifiyar Mardiya ke kallon yaronta ta ce" Summa fa ta yi da gaske, ka dauko mota wannan yaron mu kaita asibiti " Kansa ya girgiza ba alamun tashin hankali ko wani abin a tatare da shi ya ce" ina, idan har muka ci gaba da nuna mata ita din wata aba ce mai darajar da ta fi ta kowa to tabas ci gaba rashin mutuncinta zai yi maimakun ya tsaya, ki duba ki ga yanda rayuwarmu ta samu cenji sanadiyar aurenta da wannan bawan Allahn, mutumen nan bashi da bakin ciki, bashi da rowa, bashi da wariwa tsakaninmu, duba ki ga ya bani gida ga mota sannan ya nunan hanyar nema, a gaskiya idan har Mardiya zata ci gaba da haka da kaina zan nemi da ya salameta, domin kuwa darajarsa ta kai wajen da zan iya ture Mardiya na rungume shi, dan kuwa a duniya da mai mutunci nake iya zama, Mardiya kuwa idan tana so ta yi summa bakwai! " Baki bude ta raka shi da kallo, sai yayarta ce ta kama mata ita suka kaita daki suka samo ruwa suka shiga shafa mata Tana farkawa a firgice ta farka, bata tsaya adu'a ko wani matacen jiki ba sai wata ashar da ta luluka tana fadin" walahi basu isa ba, basu isa ba, daga ita har shi din basu isa ba, shine ba neman shawarana ba komai sai dai na ji a gari ya auri tsohuwar matar da ta je saudiya yawon kilakinta ta dawo, matar da tana magana idannuwa na mata rawa? Dama na san abinda ya kawota gidan nan walah8 dan ta asirce min miji ne, aman bata isa ba sai ya saketa shi dinma bai isa ba !" Mahaifiyarta ta girgiza kai ta ce" kaya, kaya, Allah wadaran naka ya lalace, to ki bi a sanny Mardiya kar ki manta igiya daya keal ta rage tsakaninki da shi, sannan da kike maganar bai isa ba ke a wa? Da acema matar mutunci ce ke sai a tausaya maki a kama maki harma ya ji tausayinki da nauyin fada maki zai kara aure, aman ai du mace mai irin halayanki sakamakonta kennan! Kuma da kike cewa ta je kilaki kar ki manta zato fa zunubi ne koda ya kasance gaskiya ne, koda yake na kula ke din aikin zunubin ba yau ba kika bashi gaba ba baya ba, Allah ya shirye ki " Yayarta ta yatsina baki tana kallon yanda take cenza kaya bama sauraron maganar mahaifiyar tasu take ba har ta gama ta dauki yar jakarta ta fice bata tsaya jin komai ba Ajiyar zuciya ta sauke a fili ta ce" inaga ban zame mata ishara ba, sai ta je ta kaso auren ta dawo mu layu idan wannan innuwar ta shige mu tarbi wata, kin ga ina bara na dauki yan cenjin nan na fara saro mana dan abubuwan batarwa dan kuwa na ga alamun yarki bata da hankali gwara mu fara nema kar abubuwa su cakude mana muna zaune yaya kuwa ga iyali sai hamdallah " Ita dai mahaifiyarta abin duniya ya isheta hanyar da Mardiya ta bi ta fice kawai ta kurawa ido To a wannan ranar du inda Mardiya ta san zata samu ABIH ta je harta da wajen abokannansa inda yake zama aman bata ganshi ba, karshe dai sai ta mayar da kanta dakinta ta tare tare da kudirin zaman jiransa dan kuwa ta tabata du abinda ba zai kwana waje ba, kuma a shirye take da su baki dayansu, zasu san su din kannanun mararsa mutunci ne, Wasa wasa tana zaman nan har karfe goma sha daya, karshema bacin wahala ne ya yi awon gaba da ita, a lokacin da Abih din ya dawo batama san ya dawo ba, shi kansa motarta ya bi da kallo ya tabe baki yana kara gwada kiran number UMMU dake masa wasa da hankali wai wani itafa ba wani dan soyaya ta dawo aurensa ba, dan mutuncin y'ayanta ne, dan haka karma ya wani yi tunanin dan wani abin ne ta dawo masa! Wannan takaicin ya saka shi bacin shima ba tare da ya ko kula bangaren Mardiyar ba. ....................................... Karfe dayan dare da yan mintunna kennan, du wani bawa mai dauke da gajiya yana kwonce a irin wannan lokacin yana dan hutawa koda kuwa mai yawan nafilfilu ne kafin lokacin motsawarsa ta yi ya gabatar da nafilar dare Sai dai kashh, banda SULTAN SHAHEED dake zaune saman kujera mai zaman mutun daya ya kurawa waje daya ido Ya kai ruwa ya kai tsaki, ya kuma kai kansa kasa ya roki Allah kan ya kama masa, domin yakan rasa baci a idannuwansa a irin lokuka irin wannan, yakan zama mai cike da tsoron Allah da tsoron haduwarsa da ubangijinsa, yaya talakansa zai kwanta? Shin yaya bayin Allah ke rayuwa a kasarsa? Ya jima rabonsa da ya yi bada kama ya shiga gari, ya zama wajiba ya koma rayuwar bada kamar da yake yi yana cakudawa da al'umar Damagaran, ta hakan yake sannin yawancin matsalolin dake faruwa a cikin garinsa, Bai ji motsinta ba, bai ji shigowarta ba, sai jin lalausan

Table of Contents

Chapters

191 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191