Chapter 9
Chapter 9
Biyu,ya Mallaka ma Abba na K'ofar Gida,a Kasuwa kuwa yana da Shagon Saida Yankunne masu daraja,聽 Aikin Kafinta kuma be bari ba, don ya zama Ogan kanshi yara ne dashi. Kasancewar ya gama karatu da Matsayi mai kyau, wani Mallamin su ya bashi shawarar zuwa Zaria neman aiki don ya gani a Newspaper ana Neman wanda suka gama Makaranta,ya samu Abba yace "suje Zaria neman Aiki" Abba yace "Wallahi Sada baka da Godian Allah, Aikin me zakaje nema? Kana da Sana'oinka, yo ko ni da Shago na daya a ba zanje neman wani aiki ba, balle kai,Mallam kawai ka zauna tare da matarka, nima hakan zanyi" Sada yace "ai ba laifi idan aka k'ara hanyar Samu" a tak'aice Abba yace "to ba yanzu ba nidai Allah ya baka Saa". Fir ya k'i bin Sada Zaria, Sada ya tafi da takaddunshi, cikin ikon Allah, aka dauki Sada Aiki, kuma zaa dinga bashi Albashi mai tsoka. 聽 Ran Juma'a yake zuwa Kano ya koma ran Lahadi, sosai yake kula da Matarshi da Hajjonsu, harda Abba, duk abunda zai siyo ma gidanshi sai ya siyan ma Abba, dalilin haka ne Abba yayi relying kan Sada,har ya zama raggon Mutum, zuwa da dawowan da Sada keyi na daga hankalin Hajjo, don ta kanji a Radio Hadarin Motoci daga wannan gari zuwa wannan gari, wannan zuwan da Sada yayi ta mishi magana "Yanzu kai Sada, baka jin wahalan tafiya ko? Baka gudun Sharrin k'arfe?" Yayi murmushi yace "Umma, Allah zai kare, tunda ina daku ai dole nake zuwa ganinku" Hajjo ta jinjina kai, tana son Halaiyar Sada, yana da kula sosai ba kamar Abba ba, shi da yake cikin gari sai yayi kwana 8 ko fi bata dorashi a idonta ba, ta nisa tace "Sada, tunda matarka na hutun Makaranta, ka dauketa ku koma chan gun aikin ka, alabasshi in ta koma Makaranta ta dawo" dadi kamar ya shide shi, dama kunya ce ta hanashi tafiya da Yesmeen, yace "Umma kefa?" tace "in dai ta nine kuyi zamanku chan ka maida hankali gun aikinka, amma na san ba zaka iya ba sai kazo ganina da danuwanka, to ko zuwa bayan wata1 haka sai ka dinga lek'omu" yayi godia yaje ya sanar da Yesmin, itama sosai taji dadi don tana kewan Mijinta. 聽 聽 Zuwa yayi ya gaya ma Abba shawarar da suka yanke, yace "ai dama hakan yafi, zuwa da dawowan nan akwai matsala, gwara ku koma chan" nan suka danyi fira kadan har ya ke gaya mai Mairo na da juna biyu wata 3, murna kamar me gun Sada,ya zaro dari biyar ya ba, yace "ga goron Albishir" Abba ya yi dariya, yace "ai ka shiga ciki kai mata sannu don tana ta kwaikwai, ba don yaso ba suka shiga gidan Abba, kawai shi har yau hankalin shi be kwanta da ita ba, tana zaune ta tara uban miyau a baki, yace "Madam ya jiki?" cike da yatsina tace "da sauk'i" Allah ya k'ara sauk'i" Abba na murmushi yace "Gobe zaya wuce Zaria da Yesmeen" ta dan yi yastina kafin tace "au haka zata tafi bata mana Sallama ba?" Sada yayi adria yace "maida wuk'an zamu biyo da safe kafin mu wuce" bata ce komai ba, din har yanzu bata daina jin wani abu game da Sada ba, haka suka fita, har k'ofar gida Abba ya rakashi yace "to a gaida Umma da Yesmeen". 聽 聽 聽 聽 Bayan Wata Daya Kwana biyu kenan ta ke jinta wani iri, tashin zuciya da k'warnafi ke damunta, bata yi k'asa a guiwa ba Sada na zuwa ta sanar mai, yace ta shirya suje Asibitin Shika, haka ko akayi, gwajin farko ya nuna tana dauke da juna biyu wata daya, Fadin farincikin Sada bata baki ne, haka ya dinga Addua. Washegari yaje Kano ya sanar ma Hajjo, Hajjo tayi adduan Allah ya raba lafiya, a lokacin Cikin Mairo na da wata huddu, fi'ili da iyayi dai Mairo nayi, ita bata son kaza ba ta cin kaza, kullum sai ta ci tsiren Hansin,shi ko Abba ya ta biye mata. 聽 聽 Lokacin da watan Haihuwan Mairo ya tsaya, lokacin Yesmin suka koma Kano, Yesmeen tayi ja sosai, cikinta na wata biyar yayi dabas a jikinta, ta zama abar shaawa, da taje gidan Mairo kai mata Akwatin da Sada yayi na Jariri, baki Mairo ta bude tana kallon Yesmeen, kasa boye hassadarta tayi, ko murnan ganin kayan batayi ba kamar yanda take mamakin chanzawar Yesmeen. Don bala'i, saboda da damuwa a ranar ta fara nak'uda, bayan yan wasu awanni ta haifo yaronta dan Jazir dashi,daga Asibiti tace ita a wuce Gidan Hajjo da ita, Hajjo ta tarbeta sosai. Yesmin ta kama zanin da Mairo ta bata wurin haihua ta wanke su tas. Haka a ka dinga tarairayar Mairo da Jaririnta.Rago Sada ya Siyo, ran Suna yaro yaci ABDULMAJID. 聽聽 Yesmeen ce Rainon AbdulMajid, Allah ya dora mata son yaron, itace wankin kayan kashin shi,har Abba kance mata Ummin AbdulMajid. AbdulMajid na da wata 4 Yesmin ta haifo danta Namiji,Farinciki gunsu ba a magana, har Yola Sada yaje ya gaya ma Iyayenta,da zai juyo aka hado shi da tsohuwan da zata kula da ita, Akwati guda Sada ya yi ma Uwar Jego da Jaririnta, harta Mairo sai da ya siyan mata Atamfa da Lifaya na fitar suna, ran Suna Yaro yaci ZAID. 聽 聽 聽聽Jim kadan bayan Haihuwan Zaid Mallam Iro ya rasu, Mutuwar ta girgiza Sada,yayi kuka sosai, Allah sarki tun kafin a rufo shi babban danshi yace akwai dukiyar Sada a gun Mahaifinsu, Sada yace "a bari a gama zaman makoki sai ayi magana" amma shi Dan yace "aa, Baba yace da ya rasu a damka maka Dukiyoyinka" Mukullin Shagon Kasuwa ya ba Sada, kasa karba yayi sai Abba ya karba, haka aka suturce shi aka kaishi gidanshi na gaskia. 聽 聽 Sada ya dauki nauyin gidan Mallam Iro don ba zai taba manta Alherinsa gareshi ba. A na haka ne Sada suka tattara ina su ina su suka koma Zaria, Zaid na da Wata daya, sam ba haka Mairo ta so ba, so tayi su zauna tare tayi ta ganni abubuwan da suke ciki. 聽聽 Bayan 40 ne Sada ya samo ma Yesmeen makarantan Ungozoma(Midwifery),Goggo na nan, Haka suka cigaba da Rainon Zaid. 聽 聽 聽 Bayan Shekara Hudu 聽 Alhaji Abba Abu ya kalli k'aninshi Alhaji Sada Abu yace "Gida yayi kyau sosai, Allah ya sa Alheri, sai ayi Sauka ku tare" Alhaji Sada ya murmusa yace "InshaAllah, yauwa sai maganan Makarantar Abdul dina da Zaid,tunda bakinsu bude yake ya kamata a sakasu a Boko da Islamiya"聽 Alhaji Abba yace "to ai sai a saka sun". Alhaji Sada ya Gina Gidanshi a Sharadda, Gidane hadadde wanda sai wane da wane ke mallakan irin gidan,yana da motarshi mercedez 190, da ya siya Motar nan ne ya ba Alhaji Abba tsohon Motarshi starlet, bayan ya siya musu gidan da Alhaji Abban ke Haya, duk sun zama Alhazawa, don shekaru biyu da suka wuce Alhaji Sada ya biya musu Makka su 5 har Hajjo, sukaje suka rage farali. Kudi gareshi amma ba su rufe mai ido ba, ba su sa ya dau rawanni tsiya ya daura ma kanshi ba don har Yau yana aikin Kafinta. Yana kamantawa duk abunda
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169