Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 83

Chapter 83

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

line dinku, so tun muna shaida juna get lost". Ran Mairo ya baci amma ganin fushi ba nata bane yasa ta zube kan guiwowinta biyu, tana rok'on ta da ta bata ko da bashi ne, amma haka Her Excellency ta shafewa idonta toka ta karta mata rashin mutunci karshe tace " ko ta tashi ta fitar mata daga Gida, ko ta sa Security suyi mata wulakanci, su tozarta ta" ganin ba kirki ne dasu ba, kuma in ta tsaya mata rashin mutunci, to abun zai sake kwaye mata, saboda wa ya isa ya ma matar SSG wulakanci? Jakkarta ta fizga da karfi kana ta juyo ta wurga ma Her Excellency kallon zamu sake haduwa, kafin ta fita fuuuuu. Kwantar mai da hankali take tayi tunda ta kirashi a waya, be san meyasa ba, a duk lokacin da yake magana da Hajia Aynarh, yana samun kanshi cikin nishadi, a yanzu da yake cikin tashin hankali, sai ya tsinci kanshi cikin saukin zuciya, yanda take jawo mai hadisan daukan k'addara ya k'ara burgeshi, abunda yafi burgeshi shine, da yaji tace zata taimaka mishi da ko da Miliyan biyu ne, ta burgeshi matuk'a, amma sai yace da ita "Hajia Aynarh, nagode kwarai da irin guddumuwan da kike bani da Iyalina a duk lokacin da bukatar hakan ya taso, amma gaskia ba zan amince da wannan ba, mungode Allah ya saka da Alheri, Allah ya baki ladan niyya". Shagwabewa tayi kamar tana gabanshi, tace "Haba Alhaji Abba, kar ka min haka, wallahi nayi niyya, nasan ba zan iya biya muku bashin nan ba, amma a dan rage, DonAllah kar ka juya hannun kyauta baya". Murmushi ne ciro yayi yace " dagaske ba zamu amsa ba, mun sa Gidan nan a Kasuwa, za a siyeshi fiye da Miliyan 20, InshaAllah zai kai 30 din, karki damu mungode". Ba yanda batayi ba, amma Fir Alhaji Abba ya k'i, chan tace "to shikenan, zan dai zo in tafi da Muhsin da Zinatu Gidana, sai su cigaba da zuwa Makaranta daga Gidana, don kar tashinku yayi affecting dinsu, ka tuna barinku Abuja, da k'yar aka samu Zinatu ta sake". Alhaji Abba ya jinjina kai yace " to kinga wannan ba zan hana ba, dama basu san da zancen ba, Yaronki kadai ya sani, ya hana a gaya musu" Hajiya Aynarh tace "Allah Sarki AbdulMajeed, sosai yake bani tausayi, Allah ya kara mai hakuri da dangana, InshaAllah zan zo Bayan Laasar na dauke su" haka sukayi Sallama. B e san tsawon lokacin da ya dauka a haka ba, yaci kuka har ya gode ma Allah, rashin aikinyi ya fi daga mai hankali, yanzu in suka bar Gidan nan, ya rayuwansu zai kasance? Abinci zai musu wuya? Ya zaiyi ya kula da Mahaifanshi da k'anen shi? Hannu biyu ya daga sama yana rok'on Allah sauki a lamarinsu, kafin ya tashi ya dauro Alwala don zuwa Sallahr laasar. A gajiye ta shigo Gidan, ranta a bace, kafin ta dawo gida sai da ta biya Gidan Hajiya Aliya kawarta, tarban da ta saba mata ba irin shi tayi mata ba, ta gaya mata yanda sukayi da Matar SSG Hajiya Aliya bata yi mamaki ba, Mairo ta bukaci dubu dari biyar gun Hajia Aliya don ta koma gun Bokansu don ya mata maganin damuwarta duka, Hajia Aliya ta juya mata baya, nan suka hau sama sukayi zage zage tare da tona ma junan su Asiri, karshe dai yaran Hajia Aliya suka ma Hajiya Mairo rashin kunya da wulakanci suka wurgota waje, Daki ta wuce straight tana zuwa ta zube kan Gado, komai ya juye mata, bata da kowa, bata da Mafita, bakin cikinta a saida tangamemen Gidan nan, anya ba zata kira Alhaji Nakowa ta nemi sauki gunsa ba? Kar dai ya ga gajiyawarta ya rainata, Tsaki tayi ta fada toilet da tunani dubu dari da chasa'in a kwanyar kanta. Na'eelah ta zagaya baya don kiran Zaid a waya, tun jiya ba su hadu ba, Ringing daya ya dauka, a lokacin ya koma makeup wurin Rita Phillips, kamar bazai dauka ba yayi excusing kanshi ya dauka, cikin yanayinshi yace "Eelah" tace "akwai Matsala, Dad dina ya gano ina Kano, ranshi ya baci, yace in dawo Gida, kar ma in sake inje PH, already ya min Booking ticket,yana expecting dina a Abuja by 8, i'm scared, he sound soo serious, kana ina Z?" cikin rashin damuwa yace "then ki koma, just write them a note, tell them zaki je Kauye dubo Danginki, in kin ganesu, zaki dawo ki tafi da Nura, su taimaka su kular miki dashi kafin lokacin dawowarki" tace "nagane, so yanzu yaushe zaka dawo Gidan, ina ganin Sun rasa case dinsu na Court, Majeed ya dawo hankali a tashe, yanzu ma Mom din ta dawo, daga gani Plans dinka are in place, I want to see you kafin na tafi please" ya danyi guntun tsaki, yace "makeup ake min, kinsan ana daukan atleast 5hours anayi, i'll come see you a Abuja As soon as Possible" cike da kwantar da murya tace "Please, let me see you before i go" dan shiru yayi, ya ga ta taimaka mishi sosai, kuma tana sonshi, bawai don tausayinta ba, sai don ya rama mata halacin da ta mai, don shi beson zama indebted to others, yafi so in ka mishi abi ya rama maka, yace "Ki rubuta wasikar, ki aje inda zasu gani, i will send Arm to pick you up" be jira cewarta ba ya kashe waya. Wayar ta bi da ido, tana ba kanta tausayi, a fili tace "Ina sonka Z, sonla ya makantar dani, ina abubuwa marasa kyau don kai, har cutar da bayin Allahn nan mukayi wanda zuciyoyinsu ba komai sai tausayi, Allah ka yaye min son Z, Allah ka yafe min, da sauri ta chusa wayar tsakanin ta, ta waiga baya taga ba kowa ta wuce ciki don rubuta wasikar. Najwa ta fito daga maboyanta, tunda taga Naeela ta zo baya ta biyota, zarginta ya tabbata gaskia, Naeela da Nura ba abunda sukace sune ba, Iphone 6 ke hannun Naeela, aiko ba karamar mutum bace, kalamanta na waya tayi amanna da Nura take, saboda tayi amanna be gidan, kuma ta dan fahimci wani abu, Nura shine ke son wani abu da Familyn su Majeed, ita Naeelah kawai tana taimaka mai ne saboda tana sonshi, ta jinjina kai, InshaAllah ba zasu ci nasara kan Majeed dinta ba, zatayi protecting dinsu InshaAllah, da taimakon Allah zatayi exposing Nura Kirikiri, a fili tace "Allah ka taimakeni". I N D I A Tunda ya dawo aiki, kanshi ke sarawa, zama yayi kan sofa ya dafe kanshi da duka hanayenshi, yana so tunano wani abu,tunanika kala kala suka shiga dawo mai a hankali, amma ba zaice ga abu daya k'wak'wara ba, ya dan gano wani abu, shi dai ya san yana da Danuwa daya da kuma Mahaifiya amma sam kamaninsu sun bace mai, haka kurum yaji yana son zuwa Nigeria gun Matarshi da Yayanshi, bayan nan ba zai iya baiyana me yake ji ba, haka Maama ta iske shi, itama duk wani sukuku take, "Sannu da Zuwa Papi" cikin yanayi yace "Yesmeenah, ina so naje Nigeria" ta numfasa tace "wallahi ,tun da na tashi nake jina wani iri, sai tunanin Gida nake, Ko Umma na

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});