Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 51

Chapter 51

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,192 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

gamo, fira tayi dadi aka sako mulki, suna fira ne dan Hajiyar ya shigo, zaiyi tsaran Majeed, amma tafiya yake kamar dan shekara 15, Abun mamaki yaron nan be zame ko ina ba sai kan cinyan Mamarshi, ya daura kanshi a kan cinyarta ya fara zuba shagwaba. Wow Mairo ta shagala da kallonsu, duniya bata ga abun da ya burgeta ba kamar Hajia da danta, shagwaba yake ta zuba mata dai biye mishi take tayi, tace "Amjad ga wasu Mummies dinka nan, ka gaida su" sai a lokacin ya kallesu, da murmushi lan fuskarshi yace "My Mummies, ina Kwananku" Mairo baki har kunne ta amsa. Hajiya Balaraba tace "kun ganshi nan, shekararsa 29, amma ko budurwa be da ita" ya wani buga kafa kamar dan yaye yace "Mom nace miki ba zan yi aure ba, bana so inyi nesa dake, so na hakura da Auren" Hajia Balaraba tayi daria sosai, tace "kunji ko? Maganar kenan, bayan na gaya mishi in yayi aure a nan zai zauna yanda zau dinga ganinja kullum" ya wani mak'e kafada wai "uhm uhm". Haushi ya cika Hajiya Aliya, irin ya ma zaayi k'aton Gardi kamar wannan yayi ta sakata gaban su haka kamar me shan Nono, ita ko Mommy Mairo burgeta sukayi, ina ma Majeed zai dinga mata haka?. "Amjad" Mairo ta cire baki ta kirashi, ya kalleta, ta danyi jim kafin tace "ba zaka zauna haka ba aure ba, shekara 29 fa? Yaro na he's 28 amma har yayi aure, meyasa ba zakayi auren ba a kawo matar nan? Yanda ga Mom dinka ga Wife dinka? Uhm?" shiru yayi kafin yace "to, Mummy ki zaba min matar da kike so ta zama daughter inlaw dinki" Hajia Balaraba tace "really? Kai amma naji dadi, Hajia Mairo nagode da kika sa hankali a kanshi" . Mairo tace "haba Hajiya Balaraba, ai duk yi wa kaine, in ba damuwa ai ga 'yar wajena nan, Ziyada, na san zai sota" Mairo ta lalubo wayarta cikin jakka ta nemo hoton Ziyada ta mika ma Her Excellency" "MashaAllah, Amjad ka gani?" ta mika mai "Woww, ta yi Mom, ina so Wallahi" Hajia Mairo da takama tace "ai na san zata maka, saboda ta hadun ne" sukayi daria, yace "Mother Inlaw ina Matata? " dadi kamar ya shide Mairo tace "kar ka damu, Yayanta yaje daukota a Baze University, har nan zan kawo maka ita" Amjad ya girgixa kai yace "like every other princess, the prince go to her, itama ni zan zo gunta" . ya mike yace zamuyi magana da Mom, ku gaida gida, ya duka yayi pecking Mom dinshi ya fita daga dakin Mairo taji dadi har ranta. Hassadar Hajiya Aliya ya ki boyuwa a fuskarta, tafi shiri fa da Hajia Balaraba, amma Hajiya Mairo ta mata shigoshigo ba zurfi yanzu ya zatayi da diyarta da ta mata alkawarin auren Amjad? Mtsw, cewa tayi "Mairo tashi mu tafi Gida, lokacin dawowan yara yayi" Mairo tace "hakane, nasan su Zinatu ana hanya" Hajia Balaraba ta mike a dauko rafar dubu daya guda biyar ta basu, Mairo irin abunnan wai ki bari, ba zamu karban nan ba, tace donAllah ku karba, Mairo tace "Allah ya sauwake" ba tun yau ba Hajia Balaraba ta san Mairo da girman kan tsiya, Murmushi kawai tayi taba Hajia Aliya, Hajiya Aliya ta amsa tayi Godia, Hajia Balaraba tace "toh Hajia Mairo, sai munyi waya, Amjad zaizo" Mairo tayi Godia suka tafi. * Sai da Hajiya Aliya ta kawo Hajia Mairo har Gida, Hajia Mairo tana ta jiran Hajiya Aliya ta fiddo kasonta ta bata amma shiru, Mairo tace a ranta *kina karyan tsiya ne" hannu ta sa ta dauko Jakkar Hajia Aliya ta bude jakkarar, Hajia Aliya tayi saurin riko Jakkar tace "Yadai Hajia Mairo?" tace "kaso ma zan dauka" hajia Aliya da mamaki tace "kasonki kuma? Ba bakya bukata ba, ta baki kin ki karba" Hajia Mairo tayi tsaki tace "zancen kike so" ta dauka rafa uku, na ukun ta irga dubu hamsi ta hade da sauran ta maida mata sauran, ta rufe ta ajiye, ta kalli kawarta tace "kawas, mu yini lafiya ta bude murfin motar ta fita, hajia Aliya tace " Mairos, ba girman ki bane ba fa, kin fi karfin dubu dari biyu da hamsin" Mairo ba ta waigo ba balle ta amsata a ranta tace "ko dubu 10 aka bani yanzu hannu zan sa in karba". * Cikinta yayi kuka a karo na ba adadi, rabonta da abinci tun shekaran jiya da daddare, ruwa ma sai na toilet take sha, da ta fita sun dinga kyararta suna tsangwamanta, har rankwashinta Mummy tayi Jiya. Tana cikin yanayin nan sai ji tayi an banko k'ofar dakin da k'arfi, sosai ta firgita. Mummy ce da Nana ne shigowa sukayi, Mummy tace " Danubanki in ba dakin Uwarki bane fita, yau me daki zata dawo, ba zan yarda ku kwana runfa daya ba, bansan mugun abun da zaki mata ba" Najwa ta dago idanuwanta da suka soye saboda kuka tace "kiyi hakuri, ku bari Abdulmajeed ya dawo" Nana ta galla mata mari tana huci tace "Abdulmajeed din tsaranki ne da ubanki? Uban me kika ma Mijina da yake kwakwarki? Anki a barki din" Mummy tace ai darajarshi taci shiyasa ta kwana har 8 a gidan nan, kuma dai don kar in fuskanci fushinshi wallahi da na koreki daga gidan nan, amma dole ki koma boysquaters, shima yazo ayita ta k'are". "Zaki tashi ko ba zaki tashi ba?" shiru ta musu Ta riga ta galabaita, ta mika wuya suyi yanda zasuyi da ita, da sun san yanayin da take ciki da ko magana ba su sata ba, bata ankara ba sai ji tayi Mairo ta ja ta a kasa kamar wasu kayan wanki suka fita, ba ta bar janta ba, Azaba ma ya hanata kuka, sai dai ta lumshe idanuwanta. A ranta take cewa "Allah gani gareka, kila ma mutuwa zanyi, Allah ka sa Maama da Paapa su yafeni". Cikin hargowa taji ance "Mummy---" duk suka kalli Kofa, Majeed ne da Ziyada ne tsaye, da sauri Mummy ta saketa, Nana ta fara sosa k'eya, ba su taba zatan zasu iso da wuri haka ba, Majeed ya tako wurinsu yace "Mummy amanar da kika daukar mun kenan? Mummy ji yanda kike janta kamar wani abun da baaso? Haba Mummy, ina zaki kaita?" Mummy ko a jikinta tace "BQ zan kaita, Majeed saboda kai na barta ta yi tsawon kwanakin nan a gidan nan despite the fact that i dont like her, but na hakura saboda farincikinka, dont use your happiness to take me for granted, i wont take it anymore, Ziyada ta dawo dole ta bar mata dakinta". Daddy ya shigo gidan yace " Yadai meke faruwa? Ziyada sannunku da zuwa" Mummy tayi karaf tace "wanchan bakuwar nakeso ta koma BQ tunda yaro ya nace sai ta cigaba da zama a Gidan nan, ina laifi tunda nace ta koma BQ?" Daddy ya danyi Jim yace "Maryam Hakuri zakiyi, ba yanda zaayi ta koma chan ita kadai, mace ce fa? Yanzu zaki iya barin Ziyada ta koma BQ? Iyi Maryam?" Mairo bata amsa shi ba, ya cigaba da cewa "Kuma na tabbatar Ziyada bazata damu sharing daki da Bakuwa ba do you Mind Ziyada?" Girgiza kai tayi

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});