Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 74

Chapter 74

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,193 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Ido, Keke Napep ya tsaida yayi magana, ya ciro 1k ya bada akan idonta, ya dawo wurin Motar ya bude mata ta fito, jiki ba kwari, ya rakata har gaban Mai Napep yace "Ka tuk'ata a hankali, kar ka dauki kowa" Mai Keke Napep yace "Angama Oga" ya juya gareta, ya sakar mata murmushin da ya san yana tasiri a Zuciyar 'yanmata yace "Stay Safe My Forever, sai na kiraki, I love you so much". Tunani dubu dari a Zuciyar Ziyada ta rasa tunanin me zatayi, ita dai kawai ta san tana son ZSA, haka har suka iso har kofan Gida, tayi mamakin yanda mai Napep din ya kawota har Gida, sai kuma batayi mamaki ba, don Zaid din ya mai bayani, shi da ya bar PH yazo dominta, dadi kamar ya kasheta, ta shiga gida baki kamar gonan Auduga. Da daddare ya kirata, chan daki ta kulle Kanta, suka sha Soyayya, tana mamakin kanta, tana da wuyan sabo, bata san mutane, amma itace nan ta zage take waya da wani wai Saurayi, ashe haka abun yake? Cikin Wayan Awa Biyun da sukayi, Ziyada taji a ranta cewa bata da Miji sai Zaid, tana jin shi cikin Jinin Jikinta, cikin Bargo da duk wani tsoka na jikinta. Washegari da Majeed ya sauketa a School, har ya juya zai tafi ta tsaidashi, tace mishi " YaMaji, kar ka damu, yau ma zan hau Keke Napep, i know you are committed, tend to other things" Majeed ya dan nazareta, ya lura tun jiya take ta walwala, yace "Zuzu, is there anything you are not telling me?" da sauri tace "No, ofcourse not YaMaji" yanda tayi magana ya san cewa k'arya take mai, ya gyara zama jikin Mota yace "tun yaushe kika fara min k'arya? Zuzu are you inlove?" Fuskarta ta bashi amsa, saboda nan da nan yayi ja, da sauri tace "Bye YaMaji, kar nayi lattin lectures" ta juya ya dakatar da ita ta hanyar cewa "Zuzu" ta juyo yace "I'd like to see him" kasa boye murmushinta tayi, tace "Bye Ya Maji" da sauri ta wuce yayi Murmushi yace "Yara Sun Girma". K O T U A tunaninta k'aramin case ne tunda sunada all evidences, za kawai a ba Nakowa Rashin gaskia, a hukuntasu, Nana ta mayar musu da Credentials din Majeed a wuce wurin, shiyasa taga gwara taje tayi representing Family dinta, taje Kotun ba tare da ta sanar da kowa ba a gida. Kotu ta cika Mak'il, Nakowa da Iyalanshi sun hallarta, a ka karanto Sunan Shari'ar, Alk'ali ya buk'aci da a kira Mijin Nana ya fito gaban Kotu, Lawyern Mummy ya sanar dashi cewa Hajiya Mairo kadai ta Hallara a Kotun, Alk'ali ya tambayi ina Mijin Nanan? Mairo tayi karya tace baya k'asar, nan da nan Alk'ali yayi watsi da lamarin yace, an daga Sauraron Kotun har sai Mijin Nana ya dawo, tace Sati me zuwa zai dawo, Kotu ta daga Sauraron case din sai bayan Sati Biyu, aka Sallamesu, Hajiya Mairo ta gama wurgansu Hajia Sayluba da Nana da bak'aken maganganu kan Nana, wai Karuwar Babanta, ta ja Motarta ta wuce, Alhaji Nakowa ya Murmusa yace " kina da sauran baki har na sati biyu, Bayan Sati Biyu bakinki zai mutu Murus". * * * * Yau Laraba yayi dropping Ziyada a Makaranta, ya bi ta Rijiyar Zaki gun Mallam Sanda, Mallam Sanda ya nuna mai ba wata Matsala, ana ta Addua da saukar Kurani, InshaAllah akwai Nasara, Iyayen zasu dawo Hayyacinsu, Yayan kuma zai bayyana gaban k'anwarshi in dai yana da rai, Godia Sosai Majeed ya sakeyi, ya ja Motarshi ya tafi, be san ya akayi ba be ankara ba sai gani yayi wata ta zube a gaban shi, k'ii ya ci burki don kar ya takata, da saurinshi ya fito waje, titin Rijiyar Zakin be da kyau, ya tsugunna gabanta yace "Baiwar Allah? Tashi a hanya? Baki da lafiya ne?" dago Fuskarta tayi, budurwa ce da ba za ta wuce du Ziyada ba, yana hango boyyayen kyaunta da wahalar rayuwa ya boye a fuskarta, kayan jikinta kwandala biyar ba zaka siyesu ba, bakinta ma rawa tace "Kayi wa Darajan Manzon Allah tsira da Amincin Allah ka taimakeni" Majeed Sarkin tausayi ya sa hannu cikin Aljihu, dubun biyun da ya rage mishi ya ciro ya bata" yarinyan tayi murmushi me ciwo tace "ina ma kudi zasu magance min damuwata?" ya tsura mata ido, yana tausayinta har ranshi, yace "taso mu shiga mota" ba gardama ta bi bayanshi suka shiga Mota. "Baiwar Allah Meye damuwanki?" Sunana Na'ila Shehu, ni Marainiya ce, Ina da Yaya daya Nura, Kurma ne, be jin magana be iya maidawa, sai dai ya mayar da nuni da hannu, Rayuwanmu ya chanza tun randa Mahaifanmu suka rasu, Yayana be da wani mamora, gidan da muke haya yau da Asuba aka mana koran karnunka, bamu san inda zamu dosa ba, ka taimakeni, kamar yanda Allah ke taimakonka, ka rufa min Asiri, yanda Allah ke rufa ma Asiri, na san baka sanni ba, ka bami masauki, zan nemi Aikatau, InshaAllah ko zuwa nan da Sati daya zuwa Biyu, zan samu yanda zanyi don Girman Allah". Jikin Majeed ya gama sanyi, shi yasan shima yana da bukatan Taimakon, Babban Gida da Motan da aka ga ya na hawa, ana mishi zaton Shi wani Hamshakin maikudi ne, to hamshakin ne, amma a da ko? Tausayi Na'ila ta bashi, duk da shima yana da bukatan taimakon, zai taimaka mata ita da Yayanta, ko a boysquaters su zauna, kafin su samu yanda zasuyi, Allah ya bashi ladan, ya kalleta da tausayi yace "Ina Yayanki?" M ajina ta ja, tace " yana Ja'en" Majeed yace "ki nuna min hanya" tace "toh". Ya ja Mota, sun danyi tafiya me nisa kafin suka iso Ja'en, da kwatance suka iso wani Unguwa, Unguwan dai sai a hankali, da hannu ta nuna wani wuri tace "ga Yayana chan". Majeed ya kai dubanshi ga inda take nune, wani ya gani a tsugunne, yara sun zagayeshi suna waka, "Kurma ne, Bebe ne, bai da amfani" Na'ela ta fashe da kuka tace "hantarar mu sukeyi kullum, haka muke fama" da sauri Majeed ya fita daga Motan yayi inda yaran suke, takalmanshi ya cire yayi kamar zai buge yaran, da gudu suka ware suna mai gwalo. Majeed ya matsa kusa dashi, ya hade kai da guiwa, Majeed ya sa hannu, bai kyamace shi ba, ya dago shi tsaye, karaf idanuwansu ya gwaraya, sunyi kusan Sakwan Goma suna kallon Juna ido cikin ido, wani kallo ne da ba su san na meye ba, kafin shi Nuran ya juya kallonshi ya koma mai Kallon Rashin sani, Na'ela ta karaso gun, da hannu Nura ya mata alama da waye wannan? Ta mayar mishi da hannu kan ya kwantar da hankalinshi, Majeed yace "kuzo mu tafi Gida". Naeela ta ja hannun Yayanta Nura ta tura shi a bayan Mota, ita kuma ta shiga gaba, Majeed yayi starting Mota yayi Hanyar Gidansu Gabanshi na dukan Ukuuku, be san yanda zasu kwashe da Mummy ba. Yana Mamaki, mutane da yawa in zasuyi abu sai dai su nemi Izinin Mahaifinsu, amma su gidansu ya sha Banbam, Mummy ce ke da gida, harta Daddyn in zaiyi abu, sai ya tambayi Izininta, wannan wani irin rayuwa ne?. Ta

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});