Chapter 20
Chapter 20
ma kaji?" kai kawai Zaid ya gyad. Mutumin ya fita ya bar Zaid da tunani kalakala. * BAYANI; Alhaji Sadam Abdulbasit wanda aka fi sani bda (Alhaji Sadam Audu)dan asalin k'asar Sudan ne mai shekaru 58, Alhaji Sadam mutum ne mai tarin dukiya, Attajiri ne, tun yana da Shekaru 30 yayi Hijira zuwa Nigeria saboda wasu dalilai nashi, ba ya zama da Mata, a shekarun shi na 58 yayi Aure kusan 20 amma ba wacce ke yin聽 sati daya a gidan ta ke neman Saki a gunshi, wacce ta dade itace wacce tayi kwana 5, Alhaji Sadam na da wani larura, Maza-Mata ne(hermophrodite) yana da hallitun Maza da Mata. Dalilin da ya sa ya baro Mahaifanshi kenan don Aurenshi biyu suna rabuwa da matan, ba dama ya wuce sai a nuna shi ana yada mai maganganu kamar shi yayi kanshi, kasancewar baida kowa聽 yasa ya tattaro inashi inashi yazo Nigeria. Haka ma a Nigeria ya yi aure na farko, a ranar ta nemi saki, so da yawa yana biyan mata kudi don su aureshi su haifa mai Yara, wasu saidai su amsa kudi su gudu, wasu kuma da anyi auren su kwashi rabonsu su gudu, Yana matukar son Yara, ya tara Azziki bai da wani burin da ya wuce ace yanzu yana da dan cikinsa, yanason Magaji amma ba alamun zai taba haihuwa. Wasu na ikirarin Kudinshi na tsafi ne, shi yasa da yawa mutane na hana Yaransu rabarshi, duk yanda yake kyautata musu, a cewarsu yana son yara ne don yayi garkuwan kudi dasu. So da yawa in ya ga yaro a waje zai ce "zo ka amsa yaro" yaro sai yace "aa babana yace indaina zuwa gurinka, kai dan yankan kai ne shiyasa kake son Yara" Alhaji Sadam kanyi kuka yana kai ma Allah kukanshi, ya dukufa da zuwa Gidan Marayu yana kula dasu, cinsu da shansu da suturunsu, haka kuma ya hakura da Aure, ya cigaba da kyautata ma mutanen da ke tare dashi, ya kuma maida hankali ga Siyasa don ana damawa da shi a k'asar. * 聽 聽 Zaid be nemi komai ya rasa ba, amma yini kuka kwana kuka, jiya Alhaji Sadam ya mai Sallam ya tafi Abuja aiki, zai dawo ranar Laraba InshaAllah. Zaid yayi bak'i ya rame, damuwa ta mai yawa, har yanzu yana kukan rashin Mahaifa, kadaici kamar ya kasheshi, ga TV, ga TV game amma ba su ta6a burgeshi ba, rayuwar shi duk ta zama wani kala, Abinci sai cookcook ya matsa mai yaci, kuma be fi yayi cokali biyu ba, wani irin Zuciya Allah ya dora mai Allah shi kyauta. 聽聽 KANO 聽聽 Har sun hak'ura dai da neman Zaid, don yau kwana 4 kenan da bacewarshi, damuwar Mairo daya, yanda Abdulmajid ke damuwa sosai, duk yayi bak'i ya rame. 聽 聽聽 * Daga Abuja Kano ya wuce, Unguwar da aka mai kwatance ya nufa, yana zuwa ya ga wasu buzaye na shan shayi kasancewar bayan Maghrib ne, Sallama ya musu, kamshin turarenshi ya tabbatar musu da babban mutum ne, da wuri suka bashi wurin zama. Cikin gurbatacciyar hausarsu suke cewa "Alhaji tambaya kakeyi?" yayi murmushi "ba ku min tayin shayin ku ba" da sauri suka tura mai gabanshi, ba kyama ya kurba yace "wai ni shin me zakuce da mutuwar Mak'ocinku Sada Abu?" dayan buzu yace "ai yanzu daka ganmu haka firan Marigayin mukeyi, munji mutuwan bayin Allahn nan, al'umma gabaki daya, munyi rashi babba" Alhaji Sadam yace "haka ne" amma ya kuka ga mutuwar? Dama tafiya sukayi?" wani daga cikin buzun yace "ai ga Maigadinsu nan" Alhaji Sadam ya maida dubanshi ga Maigadin yace "Allah sarki, Allah ya gafarta musu" "Amin, kaga ranar Wata Asabar da safe, bayan Alhaji Abba da Matarshi sun zo, jim kadan naji hajiya na daga murya, abunda ba halinta ba, nayi mamaki sosai--" Alhaji Sadam ya katseshi yace "wace hajiyar kenan?" yace "Hajia Marigayiya, matar marigayi Alhaji Sada" Alhaji Sadam ya gyada kai yace ina jinka yace "saura kiris in shiga inji ko lafia, sai kuma dai na share don ba hurumina bane, bayan wasu lokkutta sai ga Alhaji da Matarshi dauke da kaya, sun fito zasu bar gidan, Fuskar Hajia yayi Ja alamun tayi kuka, hankalina be ba ni ba, na bude musu k'ofa na musu fatan dawowa lafiya, kuma abun da ya ban mamaki basu dauka Mota ba, a k'asa suka fita" Alhaji Sadam yace "toufa, to sai akayi Yaya?" sai yace "wai sai washegari Hajia Mairo tace sunyi hadari sun k'one kurmus, haka dai aka rufesu, sai kuma wannan Asabar din aka nemi Zaid ko sama ko k'asa ya bace bat, abun ban mamaki kamar almara" Alhaji Sadam ya nisa cikin tunani yace "ina sauran 'yanuwan Zaid?" "shikadai suka haifa ba shi da k'anne" "yanzu Gadon Alhaji Sada fa?" wani Gado? Ai tun kan Alhaji ya mutu ya maida duk wata kaddarar shi kan sunan Yayanshi, komai ya mallaka ma Yayanshi, gidan nan ne kadai nashi, dashi kadai ya tsira, shima tun ran da suka bar gidan Alhaji Abba da Matarshi sukayi parking suka dawo nan, Alhaji Sada be bar ma Zaid komai ba, komai ya Mallaka ma Yayanshi, nidai nace ban yarda da hakan ba, akwai wata mak'arkashiya" "kamar me fa?" inji Alhaji Sadam, Maigadi yace "nidai bansani ba, amma waye zai sadakas da dukiyar sa gabaki daya? Nifa ko mutuwar nan tsakani ga Allah bana tunanin ta Allah da Annabi ce, nace maka a kafa suka fita, sai cewa akayi sun mutu cikin Mota kuma shi ke tuk'i?" Alhaji Sadam yayi shiru yana tunani yace "Matar Alhaji Abba fa?" maigadi yace "hmm, wannan sai a hankali, tun marigayiya na da rai take kuntata mata, Marigayiya akwai hakuri wallahi, ina sane da komai, bandai chusa kai ne cikin lamarinsu, kuma har ga Allah ina zargin harda sa hannunta a bacewar Zaid, don inaji sunayi da ita, har yana ce mata ita ta kashe Mahaifanshi shima sai ya kasheta, Wallahi duk inaji, abun ban tausayi wai kuma sai ga Alhaji Abba yazo tambaya na ko naga fitar Zaid, nikuma tsakani ga Allah banga fitar shi ba, nan har aka ci nemanshi aka gaji, in kaga Hajia Mairo ba zakace tana da wata damuwar ba, kuma dududu bacewar be kai Sati daya ba, Allah ya sa Zaid na hannun nagari, in zanga wanda ya tsince shi wallahi shawara zan bashi da ya tafi da Zaid ya nesantar dashi daga Hajia". Nan maigadin ya ta zubo zance, yana basu labarin zargin da yakeyi. Alhaji Sadam ya jinjina kai, ya fahimci komai, ya gano bakin zaren. Nan ya musu Alheri sukayi Sallama washegari ya koma Kaduna. KADUNA Gabaki daya Ma'aikatan Gidan ya tara a Parlon k'asa, kama daga Mai shara, mai wankewanke, mai dafa abinci, direba, Maigadi, mai ba fulawa ruwa, d.s,hawa sama yayi dakin Zaid, yana zaune kan Window yana kallon lambun dake bayan Gidan, ya cire baki yace "Zaid, kazo muje k'asa akwai Sanarwan da zanyi" ba tare da cewa komai ba Zaid ya sauki ya bi bayanshi suk sauk'a kasa, bayan an nutsu Alhaji Sadam ya fara magana kamar haka ; "Na san kuna da tambayoyin da kuke son yi min game da yaron nan" ya fada tare da nuna Zaid da yatsa yace "a tak'aice Wannan yaron Yaro
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169