Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 148

Chapter 148

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

abu na ne, so da kuka dawo Kano, well wannan ma Gida na ne, da kaje Dubai neman aiki A Hilal Construction Company, ni na hana a daukeka aiki, da na ga ka dukufa wurin neman aiki sai na sa Nana ta dauko min Credentials dinka duka" AbdulMajeed ya dauko rinannun idanuwanshi ya kalli Zaid, yanzu abunshi ya bar bashi mamaki, tsoro ya fara bashi. Zaid ya taka har gaban Daddy yace "Baba Abba, kar kaga laifina, makancewa nayi da son daukan fansa, Furnishing Company dinka, ni na sa aka rushe, aka saida filin, wanda nine na siya, Bayan kun sayar da Gidan da muke zaune a ciki, wanda shima nine na siya ga hanyar turo muku Alhaji Labaran, kuma na sa aka tare ku a hanya da kuka karbo kudi a banki kai da AbdulMajeed a ka karben kudin, kumaburina na mallaki Gidan da na yi yarintana a ciki, kuma don na tada hankalin Hajia Mairo na kawo diyarta cikin Gidan da take ikirarin nata ne". Daddy kasa magana yayi kafin Zaid ya karasa gun Ziyada, wanda kwatakwata ta kasa nago ido ta kalleshi, ranta tafasa yakeyi, wanda take so kamar ranta ya yi duk wadannan abubuwan laifukan don daukar fansa, sanyin murya yace "Ziyaada, kamar yanda kika sani, da so nayi in chusa miki sona, in wulakantaki in sakeki, ko kuma in sa Yara na su miki fyade, kiyi ciki in koraki Gida, wannan zai sa hawan jini ya kama Mummynku, shine dalilin da Amjad ya fara nemanki da aure na tarwatsa maganar, amma along the way, komai ya chanza, ke kin sani". Kamar yanda be jiran amsar kowa ya taka ya isa gaban Zaineema, sai binshi ake da ido daga gun wannan zuwa gun wannan. "Zaineema, ke kadai zance nafi jin zafin abunda na miki, na miki sharri mafi muni, wanda zaiyi wahalar kankaruwa"Jikin Zaineema ya fara rawa, kamar ta ma san me ya mata, ta san sharrin me ya mata, kafin yayi magana ta juya ta kalli Mummy da Imani ya gama shiganta tace "Mummy kin gani ko? Kin ga abunda san zuciyanki ya ja ko? Mummy, abunda kikayi ya dawo garemu, mu da bamu san lokacin da kikayi abun ba, Mummy ina zaman lafiya da khalid, kinja Zaid ya rabamu" Kuka sosai ta fashe dashi Zaid ya dora da cewa "Ni na san lokacin da Khalid ya shigo Kaduna, a lokacin na tura Armstrong da yaje ya dasa zargi a cikin Zuciyar Mijinki, Ni--" be karashe maganar da yake shirin yi ba yaji lafiyayyun tagwayen mari a fuskarshi, dagowa yayi ya kalli me marin. ** Zuciyarta ke barazanar fasa k'irjinta ya fito, labarin da takeji kamar almara, bata taba tunanin duk girman laifukanshi zasu kai ga wannan Girma ba, hankalinta ya fi tashi data ji shine sanadiyar raba auren Zaineema, bata san me kuma yayi bayan wannan ba, ba ta san ko zata iya dauka ba, ba ta san me kunnenta zasu cigaba da jiye mata ba, da sauri ta fada gabanshi, ta katseshi ta hanyar bashi kyawawan Mari a fuska, dagowa yayi ya kalleta, idanunshi sun k'ek'eshe saboda ya gaji da kukan, juyowa yayi ya maida hankalinshi kanta yace "Maa, kiyi hakuri, Kiyi hakuri na ban zama dan da kike burin na zama ba, kiyi hakuri kin haifi Dan da ya saki kuka, ki yi hakuri kin haifi yaron da am you are disappointed in him, ki yi hakuri kan Yaron da shi burinshi ya dau fansar abunda aka Mahaifanshi, Maa, ki yafe min donAllah" da sauri ta gyada kai tace "Yafiya? ha, ai ban tunanin akwai wanda zai iya yafe ma, wani Mutum ne me tsoron Allah zaiyi abunda kayi Zaid? Wani mutum me mai Tauhidi da Ikhlas zai yi abunda kayi? To Meye Bambancinka da Mairon? You are even worse than her, Zaid kana Sallah ma kuwa? Wallahi ka ban kunya, ka bude baki sai fadin maganganu kake kamar wanda yayi abun arziki, mtss am disappointed in you, bansan me dukiya ya maidaka ba, bansan kalar tarbiyan da kasamu bayan rabuwar mu ba, abu daya na sani, i didnt born you to be a Monster, da na san haka zaka girma ka zama, wallahi da na barar da cikinka tun kan ka zama gudan Jini da na-- " cike da tashin hankali yace "Maa" katseshi tayi ta hanyar gwabe mai baki, tace "kar ka kuskura ka kirani da wannan sunan, tun lokacin da ka makance ka fara kauce hanya daga danan na daina zama Maamanka, tun daga lokacin, Zaid anya kuwa zaka samu rahamar Allah" a kausashe Daddy yace "Yesmin ki bari, kiyi shiru, kar ki ki mishi baki DonAllah" tsohuwa Hajjo da karfin hali ta tako don lallashin Yesmin, Paapa ko kasa magana yayi, jikinshi yayi matukar sanyi, Yaronsu yayi laifi babba, dole a hukuntashi, be taba ganin Yesmin dinshi haka ba, shiyasa ba zai shiga tsakanin hukuncin da ta tanadar ma Yaronta ba. Yesmin ta share hawayenta tace "Yaya ku rabu dashi Mutumin banza ne, meyasa zaiyi hakan? Ku me kuka mishi? Kanshi farau rabu da iyaye? Shi hukuma ne da zai dau hukunci a hannunshi? Meyasa be yi amfani da kudinshi yayi Sharia da Mairo ba? Meyasa ya hada da yaran da basu san komai ba? Meyasa?" kamar an tsunkuleta ta matsa kusa dashi "Anya Da na ne kai kuwa? Anya Zaidu na ne kai? Ta sa hannu ta yaga rigar da ke jikinshi, ya rage mai Ves, habarshi ta rike ta juya yanda zata ga gefen wuyanshi, tambarin da ta mishi na nan, ta sake ta kamo hannunshi ta duba, ta dai tabbatar shine, hankalin ta ya kara tashi ta tureshi, tace "tafi, you must never show yourself to my face again, in ka k'ara, zan Tsine maka, sai ka shiga Garin Porthacourt fa kyau" zubewa kasa yayi ya rik'o kafarta yana rokonta gafara, yana mata magiyan kar ta mishi haka, kafa ta sa ta hankadeshi, har sai da ya k'ume da bango. Najwa da take cikin tashin hankali ta rugo da gudu ta rungume yayanta da yakr durkushe k'asa, tace "Maama, dont do this, donAllah kar ki koreshi, Maama ki tausaya mana duka, muyi rayuwarmu mu kadai for once" Maama cikin bacin rai tace "Najwa, ki tashi ki shige ciki kafin ranki ya baci" taurin kai tayi, ganin Maama na shirin dukan Najwa ya sa Abdulmajeed yazo ya durkusa kusa da Zaid yace "DonAllah Maama ki yafe mai, kiyi hakuri, wallahi i reason with him, amma ta kan abunda Mummynmu ta muku duka, be kamata ace kina mishi mugun alkaba'i, kinsan bakin uwa, Maama shi me laifi ne, amma cikin rashin sani ne, nidai wallahi na yafe mishi, donAllah kiyi hakuri" Jikin Maama yayi sanyi tace "AbdulMajeed kar ya baka tausayi, tuban muzuru yayi, kuma ai ba kai kadai ya ma laifi ba" da sauri Ziyada ta durkusa tace "Maama wallahi nima na yafe mishi, kar ki manta duk abubuwan da Mummynmu ta muku kun yafe mata, mu su waye da ba zamu yafe mishi ba" Maama tace "Saboda kina son shi ko? Bayan wahalarshi da kika ci" kasa magana tayi sai girgiza kai da ta hau yi, Zaineema kam kasa motsi tayi, an fama mata mikin dake zuciyarta, Daddy yace "Duk abunda ya faru ba laifin

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});