Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 10

Chapter 10

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,218 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yayi a gidanshi yana ma gidan danuwanshi, da Mahaifiyarshi. AbdulMajid kuwa kawai zaa ce Mairo ta haifeshi amma shi dan Yesmeen ne, don ko da yaushe yana gunta, Mairo ta bugeshi ta yi fadan ya bar zuwa amma ina, Alhaji Abba kance "ki rabu dashi kowa ya san AbdulMajid dan Yesmeen ne" zuciyarta sai tayi bak'i. Da doki Alhaji Abba ya shiga gidan shi yana k'walawa ma Hajia Mairo kira, da sauri ta fito da tulelen cikinta, tace "Abba Lafiya?" cikin Zumudi yace "daga Sharadda muke, baki ga gini ba, ba kiga Gidan Sada ba, yanda kika san gidan kansila, gida ya hadu wallahi" ya karashe cikin d'oki, "tsuut" ta buga tsaki, da mamaki ya kalleta yace "ya akayi?" tamau ta daure fuska tace "Ya fa? Kai yanzu baka jin kunya? Ace k'aninka na da gidan kanshi kai baka dashi?" shima fuskan ya daure yace "Wannan gidan naki ne?" tace "aa naka ne, amma waya siyan maka?" yace "Sada, kuma lokacin da ya siyan min ya zama mallakina ko shi bai da iko akanshi" "hmm, haka dai kace, amma abun kunya ne ace k'aninka shine Ja Gaba a kan komai, Sada ya maka Fintink'au, kai kana nan zaune gida kamar hoto sai an dauko an baka, kaine fa babba ya kamata ace kai ne Gaba yana bin ka baya, amma ya maida ka sakarai, sai abunda ya dauko ya baka, gashi da Manyan Shaguna har da na saida gwal, gashi da shagin kafintoci, ga Aikin gwamnati yanayi, kai ka k'are a teaching" ran Alhaji Abba yayi matuk'a gun baci, yace "Ke Mairam, ki fita ido na, ai Arzikki na Allah ne, kuma da ni da Sada duk daya ne, tunda Allah ya bashi, kamar ni yaba, ba wani abu kuma zan cigaba da gode mai, ai naga da Arzikkin Sadan ne muke takama ko? Naga har Makka ya kaiki, kuma yake kula da danki kamar nashi, to kinga bansan Sakarcin banza da na wofi, ina sane da duk abubuwan da kikeyi cikin gidan nan, ki kiyayeni, So kike ki samin bak'ar Hassadanku ta Mata, to Allah ya tsareni da yin hassadan danuwana" yana kaiwa nan ya wuce fuuuu ya barta ranta na k'una, kawai dai ta fashe da kuka bakin ciki, jin Zafi da kishin Yesmin ya turniketa, yanzu ya zatayi??.. Wattpad:biebeeisa Toh wannan pagen sai aslow, ban samu nayi editting ba, nevertheless Dont forget to Vote, Comment and Recommend. #1love #ADAY #anatare #Bibiliciousfreakingfans #nagode Biebee Isa [11:32, 25/09/2017] 鈥�+234 803 414 9368鈥�: 锟斤拷A DADE ANA YI....sai gaskia锟斤拷 NA BIEBEE ISA 庐NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA) Pg6鈨� 聽 聽 聽 Alhaji Sada ya dauki AbdulMajid da Zaid ya kai su wani IMAN Nursery and Primary School nan k'asan Sharrada phase 2, Makarantar mai hade da Islamiyya ne, a wurin interview "Whats your name?" Headmaster ya tambayesu, AbdulMajid yayi wuf yace "My name is AbdulMajid Sada Abu" Zaid ko yace "My name is Zaid Sada Abu" Headmaster yace "Wow ashe twins ne" shidai Alhaji Sada bece komai ba, don ba yau ya fara jin Abdul na amfani da Abdulmajid Sada ba, burgeshi yakeyi shiyasa yake sonshi kamar Zaid.聽 Makarantar mai hade da Islamiyya ne hazak'ar su da basirar su ya sa aka basu Aji biyu(Nursery 2), nan take Ya biya kudin makarantan duka, ya kwashe su ya zube su a Mota suka wuce gidan Baba Abba. Tijara sosai Mairo tayi, wai don me AbdulMajid zaiyi using sunan Sada bayan Ubanshi na da rai, ita sai taje ta chanza mai suna, Wulakanci Sosai Alhaji Abba ya mata, k'ila da ba don cikin da ke jikinta ba da ya maketa. Wannan Kenan. 聽 聽 聽 聽 聽 聽 聽 聽 Bayan wasu shekaru 聽 聽 聽聽 Kwanci tashi ba wuya gun Allah, yara suna ta zuwa Makaranta har sun kai Primary 5,idan Abdulmajid yazo na daya, Zaid zai zo na biyu, next term Zaid zai zo na daya AbdulMajid yazo an biyu, haka sukeyi. Hazak'arsu na ba mutane Mamaki,聽akwai wani rana da Zaid na kwance kan cinyar Mamanshi, kamar an tsunguleshi ya mike yace "Maa, wani abu kamar Y din da ke kasan wuyana ciwo ne?" tayi murmushi tace "aa Zaid ba ciwo bane, Y ne ni, na maka shi da razor" ya zaro ido, yace "Maa, kin kusa yankani?" tace "aa Zaiduna, akwai dalilin da ya sa na maka, kuma idan na haifa maka k'anne suma zan musu" da alamun tambaya yace "saboda mene?" tace "saboda duk inda aka ganku an san ku 'yanuwan juna ne" ya dan yi nazari yace "kamar in kanina ya bace,idan mun kai girman Baba da Baba Abba da mun hadu zamu gane juna ko?" mamaki ya bata sosai, kawai tayi murmushi ta gyada kai, yace "to Maa, bazai goge ba?" tace ba zai goge ba har tsufa, baka san ana zane a fuska ba? Ko a ma mutum bille ko a mai fashin goshi, har tsufa ba zai taba gogewa ba, kaima naka kamar haka ne, amma naka a gefen wuya ne na zana maka 'Y' a bayan hannunka kuma na zana ma 'S',da sauri ya juya bayan hannunshi,yace "ina 'S' din?bangani ba" tayi dariya ta cire mai riga ta nuna mai zanen 'S' dinshi a wurin da ake Allurar rigakafi, yace "lahh, ya akayi ban taba gani ba?" tace "ya akayi ka ga na wuyanka?" yace "rannan ina duba mudubi nagani" tace "wannan kuma saboda kana sa riga, kuma hankalinka be kawo akwai wani abu a gun ba shiyasa baka taba gani ba" yace "Eh Mami,idan kin haifa min k'anenna, i will take care of them" tayi daria ta saba jin haka daga bakin Zaid, tace "to Zaid kayi ta Addua, Allah ya kawo masu Albarka" Zaid yace "Ameen, Maa 'Y'&'S'na nufin ke da Baba ko?" tace eh Zaid, kana da kaifin basira, "Allah ya sa har girmanka" yace "Ameen" haka ya cigaba daa mata tambayoyi ita kuma tayi ta bashi amsa.聽聽 * A kullum burin Zaid be wuce yazo gidan Baba Abba ba,yana son Baba Abba, yana son聽 AbdulMajid,ba don komai yake son zuwa ba sai don k'anwar Abdul Zaineema da ke da shekaru 4, tun tana jaririyarta yake son ta, yana son yara, da yazo yake daukarta, in gaban Hajia Mairo ne sai ta daka mai tsawa, "Donubanka ka ajiyeta, kai yaushe aka gama daukan ka da kai zaka dauki wani? Salan ka kada min ita" dariya kawai zaiyi yace "Mama ai na iya daukanta, zainee bata da nauyi dagaske ba zan kada ta ba" Rankwashi take sake mai a kai, da sauri yake ajiyeta yana yak'e me kama da kuka, gobe hakan bazai hana shi daukan ta ba, baida zuciya ko kadan, so da yawa sai Abdulmajid yace "Zaid, donAllah聽 kar ka k'ara daukan Zaineema, bana so Mama na rankwashin ka akai, ka kyaleta, nima bana daukanta" Kamar Sakarai dariya kawai zaiyi bawai don yaji ba, abubuwan da Mairo ke mai, in wani ne ba zai sake marmarin zuwa Gidan ba, gabanshi zata kira AbdulMajid ta bashi wani abun marmari, ta hana Zaid, sai dai AbdulMajid ya bashi a bayan idonta, ko kadan abubuwan da take mai bai damun Zaid, ko don yarinta ne be san kanshi bane oho. 聽 聽聽 Watarana sun dawo Makaranta, Zaineema na tashi daga bacci ta gansu suna

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});