Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 38

Chapter 38

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

zama ne na wani dan lokaci " Hajia Aliya tace "toufa, karayar Azziki kukayi? Don na tuna kince ke da Kano sai hutu" Mairo ta dan daburce "habadai karayar Azziki, kawai yara ne suke son Zaman nan, na Majeed yace Zaman barikin ya ishe shi haka, kuma kinsan zan iya komai don Yara na". Hajia Aliyah ta gyada kai bawai don ta yarda da bayanin Mairo ba, da Mairo taga shirun yayi yawa sai tace "Kawata, donAllah taya zanyi in karkato zuciyan Yaron wani k'usa a k'asar nan zuwa ga Ziyada da Zaineema?" Hajia Aliyah ta katse ta da cewan "Zaineema ta fito ne?" Mairo tace "Aa, Mijinta ya rasu ne" "Ayyah, Allah ji k'anshi". Mairo ba ta son raini, bata son abunda zaayi ta surutu dashi a kanta da kuma yaranta, Balle In Hajiya Aliya Kunnen gari tahi, to kowa ma sai yaji, haka zata zama abun zunde da nune cikin kawayensu. " Ai abu mai sauk'i ne Hajia, kudi zaki sake Sosai, na kaiki gun Na kan tundu, wanu sabon shigowa ne ya na nan, aikinshi kamar yankan wuk'a", "Allah ko Kawata? Suka chafe, Hajiya Aliya tace " Amma fa yana da Tsadar aiki, don daga aikin Miliyan daya sama yakeyi" gaban Mairo ya fadi, ina zata samo kudadden nan? Muryan Hajiya Aliya taji tana cewa "Aff! Na manta ku manya ne, ba ku da matsalar kudi". Yak'e dai Hajia Mairo keyi tace "idan ta shirya zatayi mata magana ta rakata". * "Mummy, ko shekara dari zanyi a matsayin bazawara, ba zan aura kowa ba, zan jira Khaleed ya dawo min, zan jira shi ya dawo gareni, i'll wait forever for him". Hajia Mairo ta girgiza kai, tace "Zaineema, please" Zaineema ta katse Mummy da cewa "Wallahi idan kika matsa min da Zancen Auren wani to Wallahi zan shiga duniya, Jahilci ne ma wannan ina Iddah ki fara min zancen Aure" Mairo tayi saurin cewa yi hakuri Zaineema abun be kai nan ba". Sum sum ta tashi ta fice ta bar Zaineema a daki. Mairo ta shiga damuwa sosai,ta hade kai da guiwa tana tunanin yanda duk abunda ta Gina ke falling apart,bata ankara ba sai ganin Nana tayi ta fito daga dakinsu janye da dan trolly, ta sa mukulli ta rufe dakin tare da jefa mukullin Jaka, Sanye cikin wasu riga da skirt damammu, sai gyalen da be wuce girman Jallabiya ba, Mairo da murmushi tace "Nana,kin fito?" ba tare da gaisuwa ba tace "Eh Mummy, Jigawa zanje tare da friends dina, my Majeed baya nan, i dont want to miss him, shiyasa zanje in dan huta kafin ya dawo daga Abuja" bata jira cewar Mummy ba ta wuceta, ita ko Mairo ta bita da ido, tayi amanna AbdulMajid be san da tafiyar nan ba, ya san da ya sani da jiya kafin su wuce Abuja da Ziyada da ya sanar da ita tafiyan Nana,mamakin Shiga irin ta Nana takeyi, ita tasan ba ta damu da shigar kowa ba, amma wannan Shiga ta Nana sam bata yi kama da ta ma su aure ba, wannan shiga ta nana yafi kama da na Goggagun 'yan bariki. meke samun su ne haka? A baiyane tace "Meke faruwa da Rayuwar mu?". PH Ng "Zaid please, ya kake so inyi? Son ka zai kasheni, meyasa ka za6i ka wulak'anta ni, da kyauna da ajina da kudina? Tun France nake ta bibiyarka, saboda kai na dawo PH uni don kawai na kasance tare da kai, na watsar da rayuwar daulan da nake ciki don kai, Zaid meyasa kake min haka?". In Bangon dake jikin dakin ya amsa maganar da Nadiya tayi to Zaid ya amsa, kamar Allah beyi hallita a wurin ba, sam ko kallonta baya yi, harkan gabanshi kawai yakeyi,yana latsa Laptop inda yake karanta reports din da aka turo mai a Kano da Abuja, inda ya ga Majeed ya dawo da Ziyada Makaranta zata zauna a hostel har su gama exams next upper week,sai kuma Ganinshi da akayi a Dubai Embassy, Sannan tafiyar da Nana tayi Jigawa, Kallo daya Zaid ya ma Nana ya buga tsaki da k'arfi yace "yarinyar nan zata rusa min shiri fa" Nadiya rai 6ace ta rufe Laptop din, tace "haba Zaid, ina nan tsaye ina maka magana, hankalin ka na wuri wata 'yariska?" ran Zaid ya 6aci, shiyasa baya son mata, ba su iya komai ba sai distraction, ba ya son ayi distracting dinshi, rai a 6ace ya kalleta yace "bana son ana distracting dina, tunda kika zo kike distracting dina, i dont remember inviting you, banason warin jikinki, bana son kallon fuskanki" ido cike da hawaye tace "Zaid, me kake nufi?" a tak'aice yace "a sauk'ak'e-- Fita" tace "What?" a dakile yace "i wont repeat myself" fizgar jakkanta tayi hanyar k'ofa tana a"You'll regret this" murmushin gefen baki yayi ya bude laptop din yana tunanin yanda zai 6ullo ma Nana, don in bebi sannu ba, Asirin Nana zai tonu, Majeed ya saketa, ita kuma bata mai aikin da yake so tayi ba, wanda shine dalilin da ya sa yayi sandaiyar Auren Nana da Majeed, to wai me Majeed yaje yi a UAE Embassy? Ko tafiya zaiyi? Yana son sanin ina zaije. Bari dai ya kira Nana nan, daga bakinta zaiji Komai, Wayarshi ya dauko ya latsa numbern Nana, sai da ya mata missed calls uku kafin ta dauka da tsawa "wai wani daniskan ne yake kirana" cikin muryan shi yace "daniskan da ya koya miki yanda zaki sa Majeed Aurenki" tsaf ta ganeshi, to me yake so kuma, tunda kwalliya ta biya kudin sabulu ai bata da sauran bussiness dashi, tace "to ya akayi ne?" ya murmusa yace "Me Majeed zai jeyi Dubai?" tace "huff, mesa zan gaya ma sirrin Mijina?" yace "saboda nace ki gaya min, kar ki manta ni nayi sanadiyar aurenku, lokaci daya zan rusashi" tsaki tayi tace "you are very stupid, ba kai ka sa ya Aureni ba, kar ka kara kirana, Stupid" ta kashe wayar tana huci, waye wannan? Me ya dauki kanshi da zai dinga kiranta yana sata abubuwa ko tambayarta abubuwa?. Wayarta ya sake kira, da tsawa ta dauka da niyyar cimai mutunci, muryan nan dai ne, yace "Nana Nakowa, you'll apologise to me,ba a min ihu, ba a daga min murya, ba a zagina,apologise for calling me stupid, and finally ki gaya min mai Majeed zaije yi Dubai, i wont ask again". Tayi daria tace " i like your confidence, so ka matseni ka sani in fada maka" yayi murmushi yace "ba zan matseki ba, da kanki zaki gaya min, or maybe zaki ba Nimcy ko Salim su fada min". A firgice Nana ta kalli Nimcy da Salim din dake kan Gado suna aikata Alfasha, baki na rawa tace "ina ka sansu?" yayi daria yace "kina nufin ina na san Kwarton ki? Da dadironki Nimcy, duk Kano be isheki ba ke da Salim sai da kukazo Jigawa wurin Nimcy?, what will happen if Majeed gets to know his Wife is a hypocritical b*itch Ehh?". Da sauri tace "No,No, donAllah kayi hakuri,don't tell him, Zan gaya ma all you want to know". "Good, ina jinki" tace "Majeed zaije yin wani Interview ne a HILAL Construction Company on Monday, shine yazo Abuja neman Visa" Zaid ya jinjina kai

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});