Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 162

Chapter 162

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tayi watsi dasu a baya ta nemi numbersu daga wajen wata kawarta, ta dinga kiransu tana gayyatarsu, badai ta kira Hajia Aleeyah ba, don sun raba Jaha. Zaineema ta shigo Parlorn sanye cikin doguwar riga ta Alfarma, tace "Mummy zanje Gidan Paapa, Aunty Karima zata min lalle" Mummy ta danyi wani tubani kafin tace "bari in kira Daddynku in tambayeshi sai muje tare k'ila akwai Aikin da zaayi a Gidan Paapanku" Zaineema tayi murmushi a ranta tace "gaskia Mommy ta chanza, da da ne fitar ta take ba tare da izinin kowa ba, Zaineema tace "Mummy ina waje ina jiranki" kai kawai ta gyada mata, cike da kissa ta kira Daddy ta lankwashe murya tace "Sweet Daddyn Yara" daga bangarenshi ya murmusa har ranshi yaji sabon sunan da Maryam ta lak'a mai yace "Sweet Mummyn Yara" ta lumshe idanuwa tace "ina neman izini zuwa Gidan Sada, zanje na gansu da shiryeshirye" Daddy yaji dadi, Maryam bata taba nemin izininshi ba in zata fita, amma yau itace da neman izini, tabbas yaji dadin sauyawarta, kuma ya lura tun da ta dawo take k'okarin faranta mai rai yace "A dawo lafiya, nima mun fita da Sada" "Allah ya maido min kai lafiya Masoyina" Daddy har ranshi ya ji dadi, yana ta murmushi gaban Paapa, Paapa yace "Allah ya ja da ran Mijin Maryam Angon Aynarh" Daddy yace "fadi ka k'ara" Hajjo tayo daria. Mummy ta yafa gyalenta ta fito inda Zaineema take waya da khaleed, Baya suka shiga Driver ya ja su, suka nufi tarauni Gidan Paapa, a hanya ne Driver yayi tuning zuwa Meela FM suka ji wata zazzakar murya na sanarwa. *Hajia Mairo Abba Abu na farincikin Gayyatar 'yanuwa da Abokan Arziki zuwa yinin Bikin Danku Abdulmajeed Abba Abu, da kuma walimar tarewar Amaryarta Hajia Aina'u Mustapha da zaayi ranar Lahadi da k'arfe 3 na rana a Gidan Alhaji Abba Abu da ke Nassarawa lowcost, wannan na matsayin katin gayyatar ga duk wanda be samu Kati ba, Allah ya bada ikon hallarta Ameen, Sanarwa Hajia Mairo Abba Abu*. Zaineema ta hau tafi tana cewa "Wooo Mommynmu, wallahi kin burgeni, Allah ya kwabe fitina tsakaninku da Aunty Aynarh" Mairo tayi daria tace "Zainee, ance miki mu na yau ne? Da na bi bokaye, amma ina neman yafiyan Allah, Allah ya yafe min, yanzu kuwa, kishin Matayen Annabawa zanyi, kuma dan farincikin Mijina, Ke dai muje zuwa, ba zakuji wata matsala daga gareni ba" Zaineema ta rungumeta tace "Thank You Mom" shafa kanta tayi, tace "Khaleed zaizo daurin Aure ko?" Zaineema tace "Gobe yace zasu taho harda Hajiarsu" Mairo tace "Allah shi kaimu, ya kawo su lafiya" Zaineema tace "Ameen" kafin su isa sai da aka sake sanarwa a gidan Radio. ***** Abdulmajeed yayi tsaki a karo na uku yace "wai don me zaa ce bazan ga Pure Heart ba? Don me?" Zaid dai dariya yake yace "nikam zauna in baka Goodnews dina" tsaki yayi ya zauna yana fuskantar Zaid yace "Ina jinka" Zaid yace "My Forever is Pregnant" Farinciki ya baiyana a fuskan Abdulmajeed yace "MashaAllah, ikon Allah, howcomes?" Zaid yayi rage girman idonshi yace "tambayana kake? To barin gaya ma, ni da Ziyaa--" Abdulmajeed ya wawuro wani pillow ya jefe Zaid dashi yace "You Marapoka, ba haka nake nufi ba" Zaid ya fashe da daria ya mike yace "tashi muje muga Kayan da Idi ya siyo" Abdulmajeed ya tashi yace "wani kaya?" "Maama tace a yi ma su Mummy lefe ita da amaryarta" Abdulmajeed ya dafe kai yace "Ohh Mata, muje Gidan ni Allah duk yanda zanyi naga PureHeart sai nayi ehe" yayi gaba Zaid na binshi a baya. Akwatuna 6 saiti biyu wanda kala kadai ya bambanta cike mak'il da kaya, ko wani akwati da abunda ke ciki, Abdulmajeed yace "kai ni banda lokacin kallon wadannan abubuwan" Idi ya kalli Zaid yace "baka kalla ba, Ummu Sudais ta hada, ka dai duba abunda babu sai a kara" Zaid yace "i trust you, and i trust Ummu Sudais,ba sai nagani ba, kawai ka sa yaranka su kai chan Gidan Hajjo, su Daddy na chan, in sun gama a kawoshi chan Gidan Paapa, yanda Maama tace su zasu kaima Aunty Aynarh ku ksi motocin da zasu kai su chan, kasan shaani na mata" Idi yayi Daria, yace "Angama Oga" suka wuce kafin Idi ya kira yaransa suka kwahi kayan suka nufa Gidan Hajjo. **** Hajia Mairo ta ware a Gidan Maama ana ta fira da ita, nan tace ma Aunty Karima in an gama ma yara gyaran jiki itama sai an mata, don itama amaryarce, shewa ake tayi. Su Zaid da Abdulmajeed sukayi Sallama a Parlorn, amsawa akayi, suka sake gaisawa, Zaid ya dan kalli Hajia Mairo yace "Mummy ina wuni" da fararta dukda ta na kunyanshi tace "lafiya lau Zaid, ya akaji da hidima?" dan dariya yayi ya danyi gaba yace "Aunty Karima. Ina Baby wannan yace sai yaga matarshi zai bar gidan nan yau" Abdulmajeed yace "lahh, karya yake, wallahi cewa yayi na rakoshi wurin Zuzu, wai yana missing dinta" Mummy ta watsa mai hannu alamun dak'uwa tace "baka da kunya ko? Oya zo ka fice, kar ka sake ka shiga dakin yanmatan nan, ba su kadai bane" Zaid yayi kamar be jita ba, yayi gaba, burinshi yaga matarshi, yaji muryan Mummy na cewa "harda kai Zaid, zo ka wuce, oya out both of you" Zaid ya turo baki ya fasa shuga dakinsu Najwan ya zo ya dungure Majeed ya tusa k'eyarshi suka fita suna mitan an hanasu ganin matayensu". Maama ta sa daria tace da Mummy "ai kece daidai su, dazun wai ina dakin Paapansu Zaid yake ta wani fi'ili wai matarshi na dauke da juna biyu, kamar kanshi farau" nan fa Mata suka fara tofa alabarkacin bakinsu "Ahh MashaAllah, su Ziyadatu har an harbu? Allah ya inganta" Mummy dai tayi ta murmushi. Idi yayi Sallama a bakin kofar Parlorn, wata diyar Baba hussaini da ake ce ma Cutielurv ta lek'a, suka gaisa yace "kice ma Maman gatan marayu ga sak'o nan" Cutielurv ta koma ta sanar da Maama, tashi tayi ta nufa waje, har kasa ya durkusa ya gaidata kafin yace "ga Sak'o nan, inji Gatan Marayu" a ranta tace "Allah ya kara budi na Alheri Gatan Marayu, tace ku shigo dashi, Yaran Idi suka dinga shigowa da Akwatun nan, yan parlo sai kallo suke dai. Maama tace ga Lefe nan "Yara sunyi wa Iyayensu" ko bata fada ba, sun san Zaid take nufi, "Hajia Mairo saiti guda, Amaryarta saiti guda" Guda aka sa, Mairo tace "MashaAllah, Allah ya biyashi da Gidan Aljanna" suka amsa da Ameen, nan suka kwantar da Akwatunan suka shiga budewa dayan bayan daya, sutura guda hamsin Harda dinkakku ready made, da kayan shafa, da mayafai, da yankune da sarka Zinari. Maama tace "Hajia, ki dau wanda kikeso sai akai ma Amarya nata ko?" Hajia Mairo tace "na dau wannan" na farkon kenan, na aka hau guda. Tace "Toh, ku tashi mu dinguma muje Mukai ma Amarya lefen nata". Haka ko akayi, Mata su ka cika motocin da aka tanada dominsu gaban Gida, aka loda akwatunnan Aunty Aynarh aka nufi Gidan Amarya, Yanmatan aka bari a gida. Hajia Aunty Aynarh zaune cikin Kawayenta, yanuwa da abokan arziki, wanda kallo daya zaka musu kasan

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});