Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 8

Chapter 8

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,220 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ci da sha kai har sutura in Allah ya hore mai, sai ka nuna bacin rai don yana son auren Uwarmu? Abun farinciki ne Abba" cikin聽 tsawa yace"dama ba danAllah yake kula damu ba, bana son wannan Auren, Umma danAllah karki aureshi, bana son ki aura kowa, duk munfukai ne, ni zan kula dake har k'arshen rayuwata, zanyi kudi Umma" ba dan tanaso ba tace "dama ba na son Auren kowa, Mallam shine Mijina na farko kuma ma k'arshe, kune farinciki na, kun isheni" Abba yayi murmushi mun gode Umma, girgiza kai Sada yayi ya fita, da wannan aka bar batun Auren Hajjo. 聽 聽 Hajjo ta musu maganan fara Sana'a, itama zata fara danwake da shinkafa da mai da yajin sayarwa, Abba ya rufe Ido yace "sam bai yarda ba, ya zaayi ace mamarsu tana abincin saidawa, shi gaskia sam, kuma shi kar a takura mai da fara sana'a,zaiyi idan lokaci yayi" Sada yayi mamakin Hajjo da tace ta fasa, da kuma zuba mai ido da tayi. Burinshi yayi karatu kuma InshaAllah sai yayi, ya gaya musu cewa zai ba Mallam Iro gadonshi ya dinga juya mai, Abba yace kai wallahi baka da wayau nan ya kushe hakan, Sada be damu ba tunda Hajjo bata hanashi ba, haka ya kai ma Mallam Iro Gadonshi, Mallam iro ko ya kira shaidu yace "ko bayan ba raina wannan na Sada ne, zan dinga juya mai da ribar da uwar". Sada ya gaya mai yanason ya cigaba da makaranta, Mallam Iro yace "ya jira fitowar takardun shi kafin ya shiga jami'a zai tsaya mai InshaAllah" Mallam Iro ya shiga da Sada wurin Koyan Kayan katako (Carpentry work) da abunda yake samu a gun aikin koyan Kafintan ne ya ke siyo Omo,sugar, ashana, da cingam yana k'uk'k'ulawa a tray yana zagayawa, Allah ya dafa mai ya bude mai kasuwa nan da nan ya ke k'arewa yana siyan wasu, sai kuma ya hada tebiri a gun aiki, yazo yana jera kayan Sana'ar shi a kan tebirin k'ofar gida, Abba ko da kudin gadonshi,sai dai ya siya banza ya siya wofi yana kashe ma abokai kudi,ya zama dan fafa. 聽 聽 Haka Sada ya k'ware a harkan Kafinta, yana zuwa gidaje yana gyara musu kujeru da makammancin haka, tradern shi kuwa ta cika mak'il don yanzu ya bar tebiri ya buga Container duk da Abba na shiga na daukan abunda yake so,ko a jikin Sada don a ganinshi abunshi na Abba ne, ya zamana cikin Gida ma Sada ke ciyar dasu. Haka Rayuwa ta cigaba har Sada ya ja raayin Abba suka koma Karatu. 聽 聽 Ko da suke Jami'a ana garin Kano, Sada da kudinshi sosai, don shi yake hidimar makarantansu da ta gida, Abba k'arya ta k'are tunda gado ya k'are, Sada bai da ganin k'yashi ko mai Abba ke so zai mishi, haka suka dinga karatu ba tare da wata matsala ba, har yau Sada bai bar kafinta ba, don yanzu likafa ta ja har kujeru da gadaje yakeyi. 聽 聽 Bayan Shekaru biyu Ganin shi da kudi da kyaunshi Mairo 'yar mutanen katsinawa ta ganshi,Asalinsu 'yar kamaru ce, tana karatu itama a Kano,sosai take sonshi, ta sha kaimai kanta na ya sota, amma shi san bata mishi ba, ya bata hakuri, ashe idonshi ya k'yallo mai Yesmeen shu'aibu yar mutanen Yola, yarinya ce mai hankali itama nan take karatu fannin lafiya, a lokacin ba ko wani Uba yake barin diyarshi mace zuwa karatu wani gari ba, amma da yake Yesmeen na da kamun kai haka babanta ya barta tazo karatu Kano. Ajinsu daya da Mairo, duk yanda Mairo ta so ta shige ma Yesmeen amma ta k'i yarda, don yanayin Mairo da k'awayenta bai mata ba. Haka su Mairo suke jin haushinta don ta fiye girman kai a cewarsu. A lokacin da su Sada zasu gama Makaranta,har lokacin Mairo bata bar yi mai Wasik'u ba, don har gida take binshi, a lokacin ne ya baiyyana ma Yesmeen son ta da yakeyi,ba wuya ta amince mai. Wannan kenan. Ya kuka ga tuna Bayan? Wattpad : biebeeisa Please,Biko,donAllah dont forget to Vote, Comments and Share. #1love #ADAY #anatare #Bibiliciousfreakingfans #nagode BiebeeIsa [11:31, 25/09/2017] 鈥�+234 803 414 9368鈥�: 锟斤拷A DADE ANA YI....sai gaskia锟斤拷 NA BIEBEE ISA 庐NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA) Pg5鈨� 聽 聽 Ba 6ata lokaci Sada ya sanar ma Mallam Iro ya samu yarinyan da yake so yar mutan Yola ce, yana so ya Aureta kuma,Mallam Iro ya tattara Abokan Mallam Abu su uku suka tafi chan Yola neman aure, ganin Sada ya samu mata, hannu bibbiyu danginsu Yesmin suka karbi Mallam Iro, Baban Yesmin ma yace gwara ayi Auren ta karasa karatun gidan Mijinta, hankalin shi zaifi kwanciya, nan aka Ajiye maganan cewa idan zasu sake dawowa su dawo da Sadaki a daura Aure, Sosai Baba Abba shima ya baza rudun neman mata,Hajjo tace "Abba da ka bari ka fara tara abunda zaka rik'e matar dashi sai kayi auren" ai fa shikenan Hajjo ta gama dashi, don me zata cemai sai ya tara kudi zaiyi aure? Wato shi Sada baa ce mai komai ba da ya tashi Neman Aure, sai shi da ba'aso, dama ya san ta fi son Sada, in banda haka, don me k'aninshi Aure, nan da nan Hajjo ta rude, ta fara lallashin Abba, tace ya samo mata ko diyar wacece zata aura mai shi. 聽 聽聽 Soyyayar Sada da Yesmeen ya zagaye ko ina, da Mairo taji labarin dangin Sada sunje Yola neman auren Yesmin komai ya kwance mata, ta shiga damuwa sosai don sosai take son Sada, Abba ko Allah ya daura mai son Mairo, don Mairo na da kyan jiki, dirin ta na fizgar Maza, ya nuna mata So amma ta nuna mai ita Sada take so, kadan kadan yake jin kishin Sada, amma da yaga cewa bata gaban Sadan sai hankalinta ya dan kwanta, da Mairo taga ba sarki sai Allah, soyayyar Yesmin da Sada sai gaba yake k'arawa, ta maida wuk'aken Har Abba ya samu ya dinga chusa kanshi gunta har ta fara bashi hadin kai ba don ta hak'ura da Sada ba, sai dai don kar tayi biyu babu,a yanda take cema k'awayenta "gwara dan Abu daya, da ace na rasa su duka" har wa yau tsanar Yesmin dank'are a ranta. 聽 聽 聽 聽 Bayan Shekara 1 聽 聽聽 Wata 4 kenan da Aurensu duka, Sada na zaune da Yesmin a nan gidan Hajjo, inda ya buge Soro da dakinsa ya gina musu Ciki da Parlo wadattace, Abba ko Hayan ciki da parlo聽 Hajjo ta kama mai a sharadda, a cewar shi nan Gidansu ya musu kadan ga Sada sa Iyalinshi, amma a zahirin gaskia Mairo ce tace ita ba zata iya zama da Uwar Miji ba, da yake yana sonta sai ya biyo ma Hajjo ta haka. 聽 Duk hidima da shagalin da akayi da biki Sada ya dauki nauyin, harta lefen Mairo shi yayi, abunda ya ma Yesmeen, shi ya ma Mairo, be nuna bambancin ba. Hajjo suna zaune lafiya da Yesmin, yesmin tana girmamata don har wanki take mata, hakan kuwa na faranta ran Sada, yana son Mai kyautata ma Uwashi. 聽 A haka bayan sun gama Makarnata,k'offofukan Alherin Sada sai budewa sukeyi, Don yanzu Provision Stores dinshi Guda

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});