Chapter 11
Chapter 11
wasa, da gudu ta dauko Zani ta nufo Zaid dashi, da yake itama sosai take son Zaid, cikin gwarancinta take cewa "Zaid, Zaid ka min babu" tashi yayi daga wasan da sukeyi da AbdulMajid, yace "Zo in goyaki" AbdulMajid yace "danAllah kazo mu cigaba da wasan mu, Zaineema kai ma Mama zanin ta goyaki" Ina Zaid beji ba, ya durk'usa ta hau ya zo daura zani kenan Zaineema ta subuce mishi ta fadi gwaram a k'asa, wani irin Ihu tayi wanda da ta ja ihun, sai da tayi seconds kafin ta sake shi, Zaid tuni ya kidime, nan da nan ya fara kuka, AbdulMajid yayi saurin zuwa ya dagota, yana cewa "sai da nace miki kije Mama ta goyaki,yi shiru" ina sam Yarinya ba tayi shiru ba, ihu takeyi sosai. Zaid ya kasa motsi, kuka yakeyi yana bin AbdulMajid a baya suka yi cikin Gida, daga ciki Mairo taji kukan Zaineema, da gudu ta fito, mai ya faru? AbdulMajid yace "Faduwa sukayi da Zaid" ba ta tsaya jin meye ba'asin ba ta hau Xaid da duka, duka bana wasa ba, dukan da ko kai babba akayi ma irinshi sai kaji jiki, balle yaro dan shekara 9, AbdulMajid ya dire Zaineema k'asa yaje yana kama hannun Mamanshi, saidai ta hankade shi, kuka sosai sukeyi duka su ukun, Zaid yana ta kuka har muryanshi ya dishe, kiyi hakuri "Mama, ba zan sake daukanta ba" ina Mairo bata bar dukanshi ba, duk fushi,kishi, jin zafi, hassada, da bak'incikin Yesmin da Sada da ta ke ta fa dashi fiye da shekaru goma, Mairo ta fanshe shi a jikin Zaid yau. "Kashe min ita zakayi? Eyi?in ta mutu ya zakayi? Zaka iya biyana? Ko an gaya maka juyar uwarka zata iya haifa man wata?(Tun bayan Zaid, Yesmeen ko 6atan wata bata sakeyi ba, Mairo ko kafin Zaineema, 6arinta 3, sa ma kanta damuwa da hassadar Yesmin ke barar da cikin). Kamar daga Sama, Allah ya jefo Alhaji Abba, da alamu duk maganganunta a kunenshi, da gudu yaje don ceton Zaid, harda Mari lafiyayye ya ba Mairo, a razane ta kalleshi, yace "ba tun yau ba na san kin tsana Zaid, ko me ya miki wannan dukan yafi k'arfin shi, Allah zai saka mai" ya dauki Zaid ya sa6eshi a kafada, yayi lamo jikin Baba Abba, yana kuka a hankali, AbdulMajid na kuka ya bi Babanshi a baya. Bakinciki ya turnik'e Mairo, itama daukar Zaineema tayi tana mulmula mata goshinta da ya dan kumbura, amma har yanzu bata daina kiran "Zaid ba". Gidan Hajjo Baba Abba ya wuce dasu don chan ya baro Yesmin, a Mota AbdulMajid ya gaya mai abunda ya faru, girgiza kai yayi yace "Mairo akwai Azzaluma, kayi hakuri Zaid Allah zai saka maka" yanda ya shiga da Zaid a hannu ne ya sa Yesmin faduwar Gaba, Alhaji Sada na nan shima zuwanshi kenan daukan Yesmin. A tsorace suke su duka 3, Hajjo tace "lafiya? Me ya samu Zaid din?" karaf AbdulMajid yace "Mamanmu ce ta dukeshi don sun fadi da Zaineema" Yesmin ta kawar da kai don jin ba'asin dukan, ba tun yau ba ta ke lallashin shi kan hakuri da daukan Zaineema sai ya girma, amma bayaji, rai a bace Hajjo tace "sai ta bugeshi? Da gangan zai kadata ne? Meyasa Mairo bata da tausayine? Anya kuwa Abba, anya nan gaba zaa je gidanka?". Zuciyar Sada duk ba dadi yace " Aa Umma, ai laifi yayi, don ta hukuntashi ba wani abu bane, shima ina shi ina daukan Zaineema" Alhaji Abba yace "Sada Maryam bata da kirki, hakuri na ya k'are, wallahi nagaji da ita, ta maidani sakaran Namiji, don taga ina mata shiru-shiru, zan sauwak'e mata gaskia". Hajjo tace " ka sawwak'e mata, tayi hankali" da Sauri Sada yace " Aa danAllah, hakurin zaka cigaba da yi, da Nasiha da lallami zata daina InshaAllah " Hajjo ta kumbura tayi fam ba tace komai ba. Sada ya da cigaba da bashi baki har ya hak'ura,聽 kafin yace da Yesmin "Ki shafe shi da Robb, ai sai ku tashi ku tafi kafin Maghrib yayi, AbdulMajid mu tafi gida" Abdul ya mak'e kafada Alhaji Abba ya gane nufinshi, cikin bacin rai yace"zaka zo mu wuce ko sai na sa6a ma" Alhaji Sada yace "kasan dai ba zai yarda ba ko, kai dai kawai ka tafi". Bayan komawarsu Gida, Yesmin ta dafa ruwan zafi, ta ma Zaid wanka dashi, lokaci zuwa lokaci yake sakin Ajiyar Zuciya, duk shattin hannuwan Mairo a jar fatarshi, muryarsa a dishe yace "Maama, ki haifa min jaririya kinji? Ba zan kada miki ita k'asa ba" wani kuka ya kubce mata, ta rungume danta, tana tausaya mai, tana tausaya ma kanta, ta son Mairo bata sonta bata son danta, Mairo na kishi da ita, Kishin Sauri wanda hausawa kece ma yafi Kishin kishoyoyi masu auren Miji daya Zafi (Kishin sauri:Kishin da Matan 'yanuwa{Matan Ya da Matan K'ani} ke yi da junansu). 聽 聽 聽 聽 聽 聽聽 BAYAN聽 SHEKARA DAYA Alhaji Sada Abu mutum ne mai Amana da Gaskia,ga aiki da kwazo ba Ha'inci, Alheririkan Allah sai samunshi suke tayi ta k'ofofi da dama,baya ganin k'yashi yake taimaka ma gajiyayyu, duk mai ya ta6a Allah na dafa mishi. Alhaji Abba na aiki a wani board na Trust fund wanda samun aiki a gurin sai kana da mai maka Alfarma, Alhaji Sada ya sama mishi aiki gun, don yana da connections da yawa. 聽Bayan聽 gama Primary dinsu Abdulmajid, Alhaji Sada ya saka su a secondary boarding, makaranta ce mai ji da kanshi kuma sai dan wane da wane ke ciki wato HASSAN IBRAHIM GWARZO, yanzu haka suna chan JSS1 komai dinsu daya. Cikin Abubuwan Alherin da Alhaji Sada ya samu a shekarar nan sun k'unsa da Tamfatsetsen gidanshi da ya gama ginawa a hotoro, Gida ne Wakeke, wanda zaa iya ginin gida uku ciki,randa ya gama Ginin, rannan Ya Mallaka ma Alhaji Abu gidan ya tashi daga ciki, bayan ya mai gyaregyare duk da ba wani abun da ya samu gidan don du du gidan be wuce shekara 6 ba. Sannan ya siya Shaguna 5 a bakin Titi ya rushe su ya Gina k'aton Shago inda zai zuba kayan Kafintoci, Shawara yayi da Abba na yana son Fita k'asar waje inda zai Siyo kayan aikin Kafinta, da kattakon su, ya zuba a shagon" nan da nan Abba ya bashi goyon baya na cewa ya tafi Italy su ke da irin kayyayakin nan, kuma ya bashi shawara ya tafi da Yesmin suna dawowa kawai sai su wuce sabon Gida, Sada ya Amince da batun Abba ko da ya gaya ma Hajjo ta sa ma abun Albarka, Yesmin ta ji dadi sosai, zata fita kasar waje, duk da tana zuwa Makka. A ranar da Mairo taji cewa Yesmin zata tafi k'asar waje, Ihu ta saka don ji take kamar tayi hauka, kasa boye bakincikinta yayi har Abba na mata dariar mugunta yace "ba yanda zakiyi uwar Hassada, haka zaki ta kallo har zuciyar ki ta fashe". 聽聽 Haka sukaje K'asar Italy sukayi sati biyu kafin sukayi sarin abubuwan da suka kaisu aka turo ta Ship, tsaraba sosai tayi ma Zaid da Abdul komai iri daya, daga Italy suka wuce Makka sukayi Umra kafin suka dawo Nigeria kai tsaye Sabon Gida suka tare. Washegari
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169