Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 18

Chapter 18

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,214 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

all" ya ruga da gudu cikin dakinshi ya danna Jamlock ya fada gado yana kuka mai tsuma rai "Maamaaa, Baaabaa, ku dawo, Allah ka dawo dasu, Allah ka dawo musu da ransu, Allah ba zan iya rayuwa ba su ba, Allah nima ka kasheni" haka yake ta fada har bacci mai nauyi ya dauke shi. Hankalin Mairo yayi k'ololuwa gun tashi, ta rasa ya zatayi, nan da nan ta kira Hajia Aliya ta landline din gidan, tace mata akwai Matsala, Hajia Aliya ta sanar da ita zata zo bayan Laasar. 聽聽 Ba zaman lafiya cikin gidan, gida kamar gidan rainon yara, Kuka Zaineema, da Abdulmajid keyi, tunda suka ga Zaid na kuka suma suke ta kuka,Hankalin Abdulmajid ya tashi, Allah ya daura mai son Zaid, haka ya k'i cin Abinci gashi yana jin yunwa, shi sai an bude kofa ya shiga gurin Zaid, kuka Sosai suke tayi da abun ya ma Mairo yawa sai ta sa chazar fanka ta zane Zaineema da AbdulMajid kafin sukayi shiru, sukayi baccin dole. 聽 聽 Tunda ya tashi bacci yake jin yunwa, rabonshi da Abinci tun wanda yaci a School karfe 9 na safe, gashu yanzu past 4, bude k'ofar dakin yayi zaije kitchen yaji magana K'asa k'asa dakin Mamanshi, cikin sando ya karasa yaji me ake cewa, "Yanda Allah ya rufa min Asiri, don uban yaron nan so yake ya tona min Asiri, inshaAllah I got rid of Yesmin and Sada for good, sun tafi kenan" Aliya tace "Amma da mamaki, wai haka kurum ya tambayeki ke kika kashesu? Ko kin taba gwada kashesun ne a gabanshi?" "Wallahi Aliya, yanda kikaji haka, nima haka naji, ban taba ba, nima ya ban mamaki" Aliya tace "gaskia akwai matsala, yaron nan zai baki matsala nan gaba,tunda kinji ya fara claiming in ya girma zai kasheku, nan Gidan Babanshi ne,waye-waye, wata rana Allura zai tono garma, gwara tun wuri ki san nayi" Mairo tace "Wallahi na tsorata,yaro ya hargitsa min gida, sai da na zane su Abdul kafin suka shafa min lafiya sukayi bacvin dole, Abba ko tausayin yaron ya sashi fita, bansan ya zanyi ba, Aliya ya zanyi?" tace kawai "ki murkushe shege cikin dare, ko kuma muje gun Mallam ya baki maganin da zai shek'eshi" Be tsaya karasa jin me suke cewa ba ya fara ja da baya-baya, duk da wasu kalmomin sun mai girma, hakan be hana shi fahintar komai ba, wato sun kashe Iyayenshi, shima zasu kashe shi ko, dile ya ceci kanshi?" a hankali ya shiga dakin Baba Abba, ya ko ci saa Wallet dinshi na kan dressing mirror, budewa yayi ya cire kudin da ke ciki duka ya sa a Aljihu, da sauri ya fice daga gidan a guje, yana gudu yana waigen Bayanshi, Yanayin unguwan shiru, kowa na cikin gidanshi sai da yayi gudu mai nisa kafin ya samu machine, mai machine ya kalleshi yace "ina zaka?" inda zan bar gari, Mai machine din Yace kana da kudi? Zaid ya bude Aljihunshi yace "gasu nan" ganin yawan kudin ne mai machine ya waiga gefe ya ga ba me kallonshi ya fizge duk kudin ya burka machine dinshi yace "yaro koma Gida" Zaid na kallo mai machine ya gudu, Zaid ya sake fashewa da kuka, mutane ba Imani, haka ya cigaba da tafia yana kuka, be sanin inda yake jefa kafanshi, ga Wani Uban yunwa yanaji,har ya fito bakin titi har bayan Sallahn Maghrib, Zaid na tafia, da yaga jiri na dibanshi ya samu wuri ya zauna, daga nesa ya hangi wani Mutum mai kama da Babanshi, ya fito daga wani Supermarket din da a zahiri na Babanshi ne, sai yanzu ya ga nisan tafiar da yayi, cikin zafin nama ya tunkari Mutumin da ke k'okarin sa Ledoji cikin Mota, Zaid ya fada kan K'afan Mutumin, a firgice Mutumin ya dago yana cewa "lafiya yaro?" baki bushe Zaid yace "Babana.." daidai da digowar hawayen mutumin, a ranshi ya maimaita kalmar 'Babana', Zaid ya karasa maganar da ta sark'e mai a baki "ka taimakeni" luuu jiri ya dibi Zaid ya fadi k'asa sumamme.... Wanene wannan Mutumin? One word for Mairo, And Zaid's journey begins... Hello lovers show some love, Vote, Comment and share.. #1love #ADAY #bibiliciousfreakingfans #anatare #nagode Biebee Isa [12:01, 25/09/2017] 鈥�+234 803 414 9368鈥�: 锟斤拷A DADE ANA YI....sai gaskia锟斤拷 NA BIEBEE ISA 庐NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA) Pg9鈨� Da sauri Mutumin ya k'araso gun Zaid tare da fadin "Ya Salam" waigawa yayi gefe ya ga kowa na ta kanshi don dare ya soma yi, da sauri ya cicibe Zaid ya saka a mota, ya shiga ya Motar shi sai wani Asibiti mai suna Garkuwa Clinic. Nurses suka shiga da Zaid, nan da nan aka soma taimaka mai,bayan wasu lokkutta, Dr ya fito ya samu Mutumin zaune daga waje, yace "ka kwantar da hankalin ka, stress ne ya ma yaron yawa, mun saka mishi drip. Alhajin ya sauke naunayar Ajiyar zuciya, yace "Alhamdulilah". * Lura yayi da Wallet dinshi a bude kuma a k'asa, da mamaki ya karasa ya dauka, wayam ba ko sisi, yana da tabbacin akwai kudi a cikin Wallet dinnan, kudi ne ko da suka zarce dubu bakwai, abun da mamaki,gun Mairo ya nufa yace "Maryam, waya shigo min daki? Banga kudina ba" tace "ka dai duba, wa zai shigar maka daki? Duk muna nan" sharewa kawai yayi, don ya san kudin na cikin wallet, definitely daukan kudin akayi, to wa ya dauka? Share magaanar kawai yayi. AbdulMajid zaune kamar dan maraya, ba uhm ba uhm uhm, Abba ya dan rausayar da kai yace "Maryam,wai har yanzu Zaid na cikin dakin nan, ya ki fitowa?" baki ta ya6e tace "Yo ya fito? Tunda mu din ne bai san gani? Ga dai Abdul nan yanda kasan ni na mutu be da wani walwala saboda Zaid" Baba Abbs ya mike ya nufi k'ofar yana mita "Haan anyi yaro da taurin kan tsiya, ya fi awa hudu ciki fa, ni yunwan nan nake jiye mai kar ta mai lahani" cikin hali na ko in kula, Mairo tace "Yo ai Yunwa ba k'anwar uwa bace bare na uba, da yaji yunwa zai fito yaci Abinci". Alhaji Abba yace "bari dai inje in gani, ya shiga k'wank'wasa dakin, ji yayi kamar k'ofar bude take, yana turawa kuwa kofa ta bude, da sauri ya kutsa kai, ya na neman Zaid, shiru, haka ya lalube har toilet ba Zaid ba alamunshi, da sauri ya fito, yace " Mairo be ciki, wallahi baya nan" Dam gabanta ya fadi, to ina yaron nan zaije? Kar dai ya tafi tona mata asiri ne?" da sauri ta mik'e suka shiga nemanshi duk gidan ba shi ba alamunshi, hankalin Baba Abba ya tashi matuk'a, Mairo ma ta dan tsorata, Baba Abba ya fita k'ofar Gida yana tambayar masu Gadin gidaje ko sunga gilmawar Zaid, duk sukace ba su ganshi ba, Da sauri ya tari taxi yayi gidan Hajjo yana mai rok'on Allah ya sa yana chan. Hajjo ta ji zance bambarak'wai, "Abba ba kai kace min yau zaka dauko su a Makaranta ba?name zaka zo kana tambaya na in Zaid yazo" Cikin rudewa yace "ba a ganshi bane, ba wanda ya san da fitar shi" zumbur ta mik'e tana tafa hannu gami da salati, tun daga nan suke ta baza

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});