Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 57

Chapter 57

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Majeed yace "eh gashi ta bamu ma, dubu Dari ne" Daddy yace "Allah sarki Aynarh, harda dawainiya" haushi kamar ya kashe Mummy, wai yau Abba ke yaban wata, lallai tayi Sanyi, tana jinsu inda yake cema Majeed "Toh Allah ya saka da Alheri, sai kaje ka yi siyayyan Abincin Gida" yace "To Daddy" ya fita. Daddy be bi ta kan Mairo ba ya fice shima. * Add Vote Sahad ya fara zuwa ya kwaso Provisions kala kala, sai da ya cika booth da abinci, Duk yanda rayuwa ta zo musu ko ba komai ba zasuyi rashin Abinci ba na 'yan wattanin nan masu zuwa, yana tuk'i Najwa ta fado mai a rai, Salati yayi a zuciyarsa, cikin kwanakin nan tashin hankali ya hanashi tunano komai, reverse yayi ya dauki hanyar Rijiyar Zaki, jim kadan ya baiyana a k'ofar Gidan Hajjo. Sallama yayi tare da tura k'ofan, kutsa kai yayi, kamar ance ya daga kanshi daga gefe ya daga kai, gabanshi ya yanke ya fadi, idonshi kamar ya fado, tsoro ya mamaye zuciyarsa, abu kamar almara, da sauri ya k'arasa gindin Bishiyar Zogalen da ya ga Hajjo a kai inda take katso Zogale tana yaddawa a k'asa, murya na rawa yace "Hajjo, sauko donAllah, sauko" Najwa na jin Muryanshi ta fito da Murna, Hajjo bata so ganin Majeed ba a yanzu, saukowa tayi a hankali. Da farinciki Najwa tace "Ya Majeed" murmushi kadai yayi ya maida dubanshi ga Hajjo yace "Haba Hajjo, ya akayi kika iya hawa Bishiyan nan? Ba kya tsoron ki fadi? In Zogale kikeson ci da ba siyowa ya kamata kiyi ba? Kin kama kin hau bishiya, inta Allah ta kasance fa, tsautsayi da be wuce rana kika fado fa? DonAllah kar ki sake hawa Bishiyan, in Zogale ne kuka barin je Kasuwa in siyo miki daffafa ba sai kin sha wahalan dafawa ba" be jira amsarta ba ya juya. Hawaye suka gangaro ma Hajjo, Najwa tace "oh ashe besan ita ke saidawa ba" baki ta cire ta kira Majeed. "Ya Majeed" ba tare da ya juyo ba yace "Najwa ki tsaya yanzu zan dawo, barin siyo ma Hajjo Zogale da k'ulli" tace "to ina zakaje siya bayan ga Mai Zogalen nan ka bari a gida?" chak ya tsaya, ba wai don ya fahimci abunda take cewa ba, ya juyo a hankali yace "bangane ba" Hajjo ta mata alama da ido, Najwa ta tako har gabanshi tace "i mean, zakaje siyi Zogalen bayan me Zogalen gata ko dafawa batayi ba balle taje kasuwa ta saida" ganin be fahimtar abunda take cewa ya sa ta cewa "Hajjo mai Zogale sunan da Yan Kasuwa suka fi saninta dashi kenan, tunda nazo kusan 8days kenan, ban taba ganin taci wani abu ba sai Zogale kaga har ta koya min ci, wannan Tree din kullum sai ta hau ta tsinko Sai ta dafa, sai inga ta daka wani abu kamar dutse a turmi, what do they call it? Kuli? Yes kuli, sai na rakata Kasuwa ta saida, kullum fa sai mun fita, like every blessed Day". "Inalilahi wa ina ilaihir rajiun, Allahumma aajirni fi musibati wa akhlifni khairin minha" zuu ya zame k'asa ya dafe kanshi da hannunshi, Kuka yakeyi kamar ranshi zai fita, Hajjon ma Kuka takeyi, wai Kakarshi ke Tallan Zogale? Kullum sai tayi gangancin hawa Bishiya? Kakanshi? Maman Alhaji Abba Abu? "Ya Illahi" sai da ya ci kukanshi ya gaji, kafin ya rarrafa gabanta yana rokonta gafara kamar shi ya mata laifi, yana tausayin Babanshi, ya san yau Daddy ya mutu wuta zaije saboda yanda ya banzatar da rayuwar Mahaifiyarshi, rok'onta gafara yakeyi na ta yafe ma Babanshi, kuka takeyi sosai, Najwa na tayasu, da k'yar Hajjo ta tsagaita kukanta ta dago Majeed tace "Abdallah, kayi shiru, Babanka be min komai ba, tsakanina da Abba Addua ce kawai". "Wani d'an k'warai zai bar Mahaifiyarshi cikin wannan hali? Wani dan kwarai zai sharw Shekaru sama da biyar be ga Mahaifiyarshi ba kuma dukansu suna raye? Wani dan k'warai zai wofintar da Mahaifiyarshi?" Hajjo ta katseshi tace "kul Abdallah, ba yin Abba bane, ni na sani, wallahi ba yinshi bane, yanda na nuna ma Abba So fiye da danuwanshi, Wallahi ba yinshi bane kar ma ka zarge shi, na yafe ma Abba duniya da lahira Allah ya fiddashi daga halin da yake ciki". Majeed ya so ya gane me take nufi, amma zuciyarshi bata si ta aminta da zargin, yayi saurin kawar da tunanin a ranshi yace "Hajjo, kina da D'a kamar Abba Abu, kina da Jika kamar Abdulmajid, duk da muma Rayuwarmu na da dan targarda, amma kinfi k'arfin Tallar Zogale, kinfi karfin hawa bishiya, wannan Mutane suka san Asalin ki, Wallahi sai sun dinga la'anar Daddy, kuma wallahi Bakin mutane sai ya bishi, Hajjo ta faru ta k'are, kin gama Zaman Gidan nan, zaki koma gaban Danki, da Jikokin ki, Najwa Help me get her things". "Aa Abdallah kar ka min haka, ni da in taka k'afana gidan Abba, ka dai bari, barni a nan" Majeed yace "dagaske Hajjo ba zan barki nan ba, Wallahi Gida zamu tafi" Hajjo ta fashe da kuka tace "Mamarka da bakinta tace kar in sake zuwan mata gida, in dana ne, zai dinga zuwa yana gaishe ni, gaban Abba, Abba bece komai ba, Kar ka ja min Wulakanci donAllah" Majeed ranshi ya baci kwatakwata Mummy bata kyautawa yace "da da Yanzun ba daya bane, ba wanda ya isa ya wulakantaki, ko Mummy ce, ba zan bari ba, ki yarda dani" sai da sukayi mahawara kafin Hajjo ta amince zata bi Majeed da sharadin idan taga zaa mata Wulakanci zata dawo ya amince. Jikin Najwa yayi sanyi ganin zata koma Gidan Jiya, Majeed ya lura da ita yace "Dont worry, i got you both" Murmushi suka ma juna, Hajjo ta dauki kaya kala biyu ta sa a Jakka, don a cewarta ba zata kwashi kaya da yawa ba, in zama beyi dadi ba dawowa zatayi. * Har shi ma gabanshi faduwa yake don be son yanda Mummy zata karbesu ba, yayi parking, A tsorace suka shiga gidan a Parlor suka iske Muhsin na Kallo, Oyoyo ya tashi ya mai, ya bi su Hajjo da ido, Majeed yace "Muhsin ba ka gaida Hajjo ba" cikin hausanshi yace "Ina kwana" Hajjo hawaye ya ciko mata, wannan Jinin Abba ne, amma ko haihuwarshi bata sani ba ta shafa kanshi tace "Ina wuni dai ko?" ya gyada kai, Majeed yace "je ka kira min Zuzu da Zainee" da gudu yayi dakin Ziyada yana kwada masu kira "Ya Ziyada, Ya Zaineema, Yaa Majeed na kiranku". Nana na jin Muryan Majeed ta fito, tana yauk'i idonta ya sauka kan Najwa, Najwa gabanta ya fadi, Nana ta daure fuska, "My Majeed me wannan yarinyan ta dawo yi?" a tsaye ya kalleta yace "Zauna" jin muryanshi cike da seriousness ya sa ta zama, ba ta damu da Tsohuwar da ta gani ba. Ziyada ta shigo parlorn da Sallama, Murmushi kawai ta ma Najwa ba tare da tace komai ba, ba wai don ta san Hajjo ba ta gaisheta, Hajjo tace "Ziyada ce?" Majeed yace "eh itace" ya kalli Ziyada yace "Zuzu kinsan wannan?" ta girgiza kai alamun "Aa" ya jinjina kai yace "ta shiga ta kira Zaineema, Kafin tazo sai ga Zainee

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});