Chapter 137
Chapter 137
bude ta kasa magana, be taba mata haka gaban yara ba, ga mamakinsu sai ganin Daddy ya fashe da kuka ya zube kasa "Kuyi hakuri ku yafe min Yarana, ban zaba muku uwa ta gari ba, ku yi hakuri, na zaba muku jahila cikin jahilai a matsayin Mahaifiyarku" Ziyada ta fashe da Kuka, Zaineema da sauran Yaran ma suka fashe da kuka, AbdulMajeed ya rik'e Daddy yace "Daddy donAllah in Laifi ta maka ku shirya kanku, ku mahaifanmu ne, muna son ku duka, kuyi hakuri ku shirya kanku" Daddy cikin dan tsawa yace "In shirya da wannan hatsabibiyar? Tsakanina da Maryama Allah ya isa, ta shiga da tsakanina da danuwana Sada, ta salwantar mun dasu" cikin Zafin Nama ya makuro Wuyanta "Ina kika kaimin Sada da Yesmin? Ina kika kai min su? Ina kikace su tafi? Ina Maryam?" a duk zatonta Zuciyarta ya fito daga Kirjinta, kasa motsi tayi, ganin komai take kamar a film, ta gama tsorata iyakan tsorata, karyarta ya kare, Asirinta ya tonu, Ajalinta yazo" Hajjo ta matso kusa dashi ta dafa tace "Haba Abba, me ya sameka haka? ina zata kai Sada? Ka manta Sada da Matarshi sun Mutu? Ka manta da hannunka ka rufesu? " da sauri yace "Wallahi basu mutu ba, basu bane, cikin makircinta ne tace sune, Wallahi ita ta salwantar dasu, Umurnin ta suka bi suka shiga dunia" Hajjo ta durkushe a gun tana kuka me tsuma rai, su Ziyada da Zaineema Kukan suke, Najwa da ta gama fahimtar komai ta fashe da wani irin dariyan da ya juyo hankalinsu, a baiyane tace "Alhamdulilah", duk da suna cikin tashin hankali kacokam suka bi ta da ido, da sauri ta isa gun Baba Abba ta rungumeshi tare da kwantawa kan kafadunshi, Baba Abba be da wani kuzari a kunne tace "Babana, kace Alhamdulilah" be san dalilin da ya sa ya biye mata yace "Alhamdulilah" daidai Sallaman Mutanen da ba zai taba Mance Mury 馃挱A DADE ANA YI....sai gaskia馃挱 NA Wattpad:@biebeeisa Pg3鈨�8鈨� Yaran Mairo gabaki daya sukayi kanta, Najwa tayi gun Maamanta a guje, Abba ya matso daf da danuwanshi ya ci burki a gabanshi, kallon kallo suka tsaya yi ma junansu, hawaye tuni ya wanke musu fuskoki, da sauri Sada ya karasa ya rungume Yayanshi, kuka suke a jikin junansu, Abba kamar zai shideta saboda kuka, Sadan ke bubbuga mai baya alamun rarrashi, har sai da ya tsagaita kukan, sake shi yayi ya karasa inda Hajjo ke tsaye tana ganin duk abunda ke faruwa kamar Mafarki, Sada ya tsaya a gabanta, yana hawayen farinciki, a tsorace ya sa hannunshi ya rik'o nata, lumshe idanuwa tayi hawaye na gangarowa kan kumatunta, shine, Sada ne, Autan ta ne, kafadunta ya rik'e, ya sa hannu ya share mata hawaye,聽 hannunta na rawa ta daga ta kai kan fuskarsa,聽 baki na rawa tace "Sada kai ne?" rike hannunta yayi da ke kan fuskanshi yana gyada mata kai,聽 "nine Umma,聽 nine Sadanki" "Allahu Akbar"cewar Hajjo, Maama ta matso kusa da ita ta rungumeta,聽 "Yesmeen,聽 ashe kuna raye?" wani kukan suka fashe dashi, sai lallashinsu Abba keyi. Tana cikin tashin hankali amma Kukan da Yaranta keyi ya na kara tada mata hankali, bata so ta bude ido taga ba mafarki takeyi ba,聽 bata so ta tashi daga mafarkin da take,聽 ta zata ta yarda kwallon Mangoro ta huta da k'uda,聽 in dawowan zasuyi Meyasa ba su dawo tuntuni ba sai yanzu da ta manta da shafinsu,聽 meke faruwane? Kukan da su Zaineema da Zinatu keyi na kara sata cikin damuwa,聽 so take ta bude ido ta lallashesu,聽 amma in ta bude ido hakan na nufin ta farka daga baccin da take.聽 Ruwa Ziyada ta yayyafa mata,聽 amma ko motsi batayi ba,聽 kukansu ya tsananta "Mummy please ki tashi" Daddy "please kace mata ta tashi" Daddy ya fincike hannunshi daga gun Ziyada,聽 nan hankalin yan India yayi kansu, Murmushi yayi ya matsa daf da ita,聽 don yaga idonta na motsi,聽 tsugunna wa yayi yace "Maman Yarona(kamar yanda ya kan ce mata a da=Abdulmajeed聽 yake nufi ) , na san kina jina,聽 ki tashi, kin tada hankalin yaranki" ba kunya ba tsoron Allah ta bude ido a hankali ta saukesu fes kan Sada. Bakin Miyau ta hadiya,聽 idonta ya ciko,聽 cikinta ya duri ruwa kamar zata fara gudawa,聽 a haka ta tashi tsaye tana raba ido,聽 Mijinta take kallo, Daddy ko kallon gefenta beyi ba, ta kasa kai dubanta gurin Yesmeen,聽 ta san ta cuci Bayin Allahn nan,聽 ta san ta ha'incesu,聽 ta san ta shiga tsakaninsu, Maama daga baya tana kallon Mummy cikin ido,聽 duk wasu abubuwan da suka faru suka soma kwaranyo mata,聽 kuka take sosai, da sauri Mummy ta sadda kanta kasa,聽 itama hawaye take,聽聽 tana me kunya hada idanuwa dasu, bata taba jin Nadama ya shigo mata lokaci guda聽 ba irin na yau,聽 da na sani k'eya ce,聽 amma tayi dana sanin duk wasu abubuwa da tayi,聽 kar su rabata da 'yayanta,聽 a hankali ta kai dubansu gunsu,聽 da gan kan Majeed... Zaineema.. Ziyada.. Zinatu da autanta Muhsin,聽 cirko cirko sukayi suna son jin bayanin Meke Faruwa, Hannu ta sa a fuska ta fashe da wani irin kukan Nadama, duk wani numfashi da take ja,聽 da da nasani take janshi,聽聽 a hankali suka yo kanta su duka a tare,聽 da baya da baya take ja,聽 suna binta,聽 tana baya,聽 suna binta har saida ta ci karo da bangon Kitchen, Abdulmajeed ya karasa gunta zai rungumeta, ya bata comfort,聽 ya gwada mata "koma me tayi,聽 suna tare da ita, dakatar dashi tayi da hannunta, girgiza mai kai tayi tare da zubewa a k'asa, kukan da yake ta kokarin boyewa ya fashe da, baki na rawa yace "Mummy.." sauran Yaran suka taya shi suna nufar inda Uwar take. A kan guiwowinta ta sauka,聽 duk yanda taso magana ta kasa,聽 sai taji harshenta ya mata nauyi, ba abinda take iya yi sai kuka,聽 nadama fal ranta,聽 Abdulmajeed ya firgita da yanayin da ya ganta,聽 takowa yayi kusa da ita ya sauka kan guiwowinshi,聽 bakinta yayi nauyi bata iya komai sai kuka da girgiza kai, ganin abunda ke faruwa yasa聽 Zaineema matsowa kusa dashi itama ta kai guiwowinta kasa,聽 Ziyada ma hakan tayi,聽 Zinatu da Muhsin ma sukayi hakan, duk abunda sukeyi kan idon Paapa da Maama, Abdulmajeed ya fara magana聽 yace "Mummynmu akwai taurin rai,聽 ba abu kadan ke daga mata聽 hankali ba, ba komai ke sata kuka ba, ba komai ke sata shiga yanayi ba,聽聽 bansan me ta muku ba,聽 bansan meke tsakaninku ba,聽 amma ina so ku sani,聽 tun da nake da ita, i've never seen her like this,聽 ban taba ganinta haka ba,聽 ban taba ganin regrets kwance a kan fuskarta ba, bansan me ta muku ba,聽 amma ina da tabbacin cewa聽 tayi nadama,聽 a kan fuskarta na karanta da tana da yanda zatayi,聽 da ta koma lokacin baya ta gyara kuskurenta,聽 donAllah, don Girmansa, kuyi hakuri,聽 ku yafe mata". Paapa da zuciyarshi ta gama karaya ya juya ya kalli Yesmin da kukan ta ya tsananta,聽 ta san bond din da ke tsakani Da da Uwa, ta san cewa聽 Mairo ce聽 sanadiar duk wani bakincikinta,聽 ta san cewa Mairo ta mata farraku da danta, bata tunanin zata iya mance abunda Mairo ta mata, a zatonta zata ji
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169