Chapter 72
Chapter 72
"da sauki tunda ba su mishi komai ba, kaje ka ganshi ko?" Majeed yace "eh naje, daga chan nake yanzu" Mummy ta lula duniyar tunani kawai tace "Alhaji Nakowa ne ya turo mishi barayin nan" duk suka bita da ido tace "haba, ga abu a baiyane, Alhaji Nakowa ne, ya zaayi ace Armed Robbers su tare ka, su karbi wayanka suyi wiping komai? Su maida maka wayanka ba tare da ko dunguran ma kai sunyi ba? Wallahi they were after that recording" Daddy yace "Maryam, ki tsarkake tunaninki, kila ba haka bane, maybe they were after something else" Hmm Mairo tace, ita dai tana da tabbacin Alhaji Nakowa ne yayi aiken nan, saboda recording dinnan, su Daddy ba zasu gane ba, don ba su san wainar da ake toyawa ba, saboda an kai mai sammaci shiyasa yake neman hanyar salwantar da evidence dinsu ko? Dole tayi taka tsantsan, kawai dai su hadu Kotu, sunci nasarar kwace na hannun Aliyu, amma ita ba zata bari ba, bari ta kira Lawyer dinta ta tura mai, komai ta fanjama fanjam kawai. B A Y A N K W A N A B I Y U Kullum sai sunyi waya da su Maama, ta sa Kaveri ta nemo mata numbern Aisha, suna chatting sosai, ta bata labarin abubuwam da suka faru da ita bayan rabuwarsu, Aisha tace "i told you so ai, yanzu you need to be very careful, ki kula da kanki" nan ta sake bata shawarwari. kwana biyu ta na cikin walwala, ba ita kadai ba, duk Ilahirin Familyn Abba Abu, ba su da wata damuwa, kwana biyu, suna zaman su lafiya, ina ma wannan farinciikin dawamame ne? Ina ma su kasance haka har karshen rayuwansu, ba su da damuwa, ba su da wata matsala. Kullum Majeed ke kai Ziyada Makaranta ya daukota, da Muhsin ya dawo Makaranta, zai rugo da gudu wurin Najwa wai ta koya mai Homework, zata karba tayi guiding dinshi, in bata gane ba sai ta tura shi wurin Ziyada, ita kuwa Zinatu tafi k'arfin Najwa ta koya mata Homework, haka take damun Daddy ko Ya Majeed su koya mata, don ta san ko kallonta Ziyada baza tayi ba. ** Kamar mara gaskia, Mummy na fita da Mota yayi Sallama dakin Hajjo, Hajjo tace "Abdallah, har ka dawo daga kai Ziyadatun Makaranta? Yace " Eh Hajjo, jikarki zaki ara min, zamu dan fita" Hajjo na lura da Najwa, tunda Majeed ya shigo dakin bata da sauran sukuni, Hajjo ta murmusa irin yanda manya keyi, tace "a dawo lafiya" Najwa tayi kamar bata ji me suke cewa ba, sai da Majeed yace "Muje ko Pure Heart?" kanta a kasa ta tashi, dama akwai Hijab a jikinta, tace "naje" Hajjo tayi dariya tace "bahausa, kin tafi zakice ba naje ba" sukayi dariya. Kasancewar Daddy ya fita da dayan Motar ya sa Majeed tsaida musu keke Napep, ya dan kallota yace "kin ta6a hawa?" kai ta gyada mai, yace "Oh hakane ko? Tuptup kuke ce mai a India" murmushi kawai tayi, yace "PureHeart, ki dinga bude baki kina min magana kinji?" ta dan turo baki, yace "you look cute" ta sa Hannu a fuska ta rufe, yayi daria, yace da me adaidaita sahu, "Rijiyar Zaki zaka kaimu, ta wurin Islamiyan Mallam Sanda?" suka shiga suka fara tafiya, shiru shiru ba wanda yayi magana sai Majeed yace "baki ce ina zamu ba?" tayi shiru yace "Ehen Ina jinki" a hankali tace "i trust you" murmushin jin dadi yayi. Daidai Islamiyan suka tsaya, naira 500 ya ciro ya ba mai adaidaitan, yace "jirani ina zuwa" gyada mai kai tayi, yayi gaba ta bishi da ido. "Assalam Alaikum" Majeed yayi Sallama a gaban shago, Wani dan Dattijo mai sanye da Alkyabba fara da Charbi zungurere ya amsa mai da "Waalaikum Salam, Bismillah" Majeed ya dan sunkuyar da kanshi don K'ofar bata da tsayi ya shiga, bayan 'yan gaisuwa, Mallam Sanda yace "saidai ban ganeka ba" Majeed ya dan Murmusa yace "AbdulMajeed ne, na wurin Alhaji Abba Abu" Mallam Sanda ya fadada fararsa, "to to, AbdulMajid ne? Haka ka koma? Ka zama magidanci, rabona da kai tun randa kazo min bankwana zaka tafi Makaranta Turai" Majeed ya Murmusa yace "gaskiya ne, an kwan biyu" nan suka sake kwasar wani gaisuwan. "Allah gafarta Mallam, tare nake da wata a waje, Mahaifanta na tare da wani Matsala, haifaffun Nigeria ne, amma rana tsaka suka hada kayansu suka bar K'asar, yanzu ba su iya tuna komai game da Nigeria, ko Garin da suke ba zasu iya tunawa ba, kuma duk randa suka shirya zuwa Nigeria, InshaAllahu sai wani abu yayi sanadiyar rashin zuwan su, shine nake so in akwai taimakon da zaa iya yi?" Mallam Sanda ya danyi shiru, chan yace "Shigo min da yarinyan" Majeed ya tashi ya fita, tana nan rak'ube, yace "PureHeart, ki shigo, munzo wurin Mallam ne, zai miki tambayoyi, ki bashi amsa kinji? Trust me, everything will be fine". Ta bi bayanshi, suka shiga Shagon, kusa da AbdulMajeed ta zauna, ta gaishe shi, Mallam Sanda ya dinga mata tambayoyi tana bashi Amsa iya saninta, Mallam Sanda ya kalli Majeed yace "Kurciya ce aka musu" Majeed yace "Kurciya?" Mallam ya gyada kai alamun eh yace "Kurciya ce, ana yin shine a lokacin da ake so a nesanta mutum da wani wuri, ko a musu farakku, maana a musu katanga, an shiga tsakaninsu da Mahaifarsu, Yanuwa da Abokan Azziki, yana iya yiwuwa wani ke hassadarsu, ko k'yashinsu" kan Majeed yayi zafi, yana mamakin mutanenmu, how can someone be so heartless? Sai yaji ya k'yamaci hassada a zuciyarshi, ya kyamaci me hali irin na Hassada. Majeed yace "Mallam, yanzu me abun yi?". Mallam Sanda ya dan Muskuta yace "Addua, Addua zamu tayi, da Ikon Allah da yardan Allah Sihirin zai karye, kila ayi k'aik'ayi koma kan Mashekiya, maana abun ya koma kan wanda ya musu, ni da Dalibai na zamu sauke Alkurani Maigirma har lokacin da zasu baiyana, ba zamu bari ba, har sai randa suka iya tuna ko da sunan garinsu ne, Yayanta kuma, da Yardan Allah, indai yana cikin K'asa Nigeria, in har da ransa, da Izzar Allah zai baiyana kanshi a duk inda yake, kar ku sama zuciyoyinku komai, Ikon Allah ya wuce tunaninku, da Ikon Allah zai baiyana Yayanta, a Mace ko a Raye". Ya k'ara da fadin suma su dage da Addua, k'arfin Addua zai bayanasu duka, Majeed ya hau Godia, ya ciro 5000 ya ba Mallam, Mallam ya girgiza kai yace "aa Abdul, dauki kudinka, taimako ne, aka ma wasu bare kai?" Majeed ya girgiza kai yace "Aa kar muyi haka da kai Mallam, Sadaka ne, a sai ma masu Sauka ruwan Sanyi" Mallam yayi Murmushi yace "Allah ya saka da Alheri Allah ya sa a dace, Najwanatu Allah ya Baiyana miki Yayanki, Allah ya sa Mahaifinki suci galaba kan masu son ganin bayansu" duk a tare suka amsa da "Ameen". A lokutta da dama, Allah na daura ma bayinsa Soyayyahn junansu, balle ma in suka maka abunda ba zaka taba mancewa ba, zakaji duniya ba wanda kake so sosai matuk'a kamarsu, hakan takasance da Najwa, tana jin AbdulMajeed Abba har cikin ranta, tun kafin ya furta mata So, bayan ya furta mata kuma sai soyayyarsa ta ninku a Zuciyarta,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169