Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 165

Chapter 165

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

na san zaka kula ka sauke duk wasu hak'k'unan dake rataye a wuyanka, Abdulmajeed na san ka da Hakuri, na sanka da kawaici da kau da kai, nasan ba zaka bani kunya ba, nasan zaka tayani k'arafafa zumuncina da na danuwana, nasan ba zaka bari ta dalilinka zumuncinmu ya ruguje ba, Abdulmajeed ka kula da Najwa, Abdulmajeed ku zauna lafiya, zaman lafiyanku shine namu kana jina?" Ya dago ya kalleshi yace "Eh Daddy, naji, kuma InshaAllah ba zaku sameni da wani abun da ba daidai ba" Daddy ya maida hankalinshi kan Najwa yace "Najwa, a sanin da na miki ke yarinya ce me kirki da son yanuwanta, na fuskanci kina da hakuri Paapanku ya tabbatar min da haka, amma NAJWA ki sani, aure ya sha bamban da abubuwan da kike gani a talabijin, aure ya wuce soyayyar da kike gani na India, Aure dan zo mu zauna, zo mu saba ne, shauki da soyayyar da kuke ma junanku, ba wai ya na nufin ba zaku sabu sabani ba, aa zaku samu sabani, zaku bata ran junanku, amma hakan be nufin ki dauki waya ki kira maamanki ko mumnynku ki gaya musu, ki rike sirrin gidanki, dana Mijinki, in kun samu sabani ku shirya kanku, kiyi hakuri kinji Najwa? Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a Dayyiba". "Ameen suka amsa gabaki daya, Daddy yace "Sada ko zaka k'ara wani abu?" Paapa yace "Yaya ka fadi komai, sai dai ince ba wai Abdulmajeed da Najwa ake ma nasihan nan ba, harda kai Zaid da ke Ziyada, kuma ai amaren ne, nasan lokacin Aurenku an muku, amma ina so kuyi amfani ds abunda Daddynku ya fafa muku, Allah ya muku Albarka gabaki dayanku" da Ameen suka amsa,"Yesmeenah zaki kara wani abu?" tace "ai Papi kunce komai, Allah ya mudu Albarka, ya kwabe fitina, Mummynsu ki musu Nasiha" Mummy ta kasa magana don hankalinta tashe yake in ta tuna, Ziyada zata tafi, Abdulmajeed zai tafi, Zaineema zaa tafi, girgiza kai tayi tace "ai kun gama cewa komai" Daddy yayi murmushi ya kalli Aunty Ayanrh yace "Amarya fa? Me zakice da yaranki?" ta murmusa tace "Yanmaza ku ji tsoron Allah, ku kula da matayenku, kar ku ga kamar kuna gabansu ku tauye musu hakki, kuyi supporting dinsu, yanmatana kuma, ku tashi kuzo muje daki" akayi daria, ta mik'e ta dago Najwa da Ziyada ta yi gaba dasu, ta juyo ta kalli Zaineema ace "Oya, kema zo" Zainee ta mike ta bi bayansu" nan su Daddy sukayi daria. Mummy ta mike tayi dakinta don hawaye yazo mata, Maama ma ta tashi tabi bayanta. ** Aunty Aynarh ta cigaba dacewa "Ehen, ba wai don kunga kuna da komai ba, ba wai don akwai masu aiki birjiki a gidanku ba, zaku lankwashe kafafu kuyi folding arms kuce komai masu aiki zasuyi, no ban yarda ba, masu aiki suyi muku komai amma banda Gyaran dakin Miji, banda dafa Abincin Miji, kunga abubuwan nan biyu? Ku zage kuyi da kanku, kar ku bari wata me aiki ko wani me aiki ya dafa ma Mijinku abinci, kunga gyaran dakin Miji? Ku yi da kanku, ku gyara turakar mijinku, zaku ga ribar haka, kuna jina?" kai suka gyada, tace "yauwa good girls" irin abun da taba Zaineema da zata America ta kara daukowa, tace "ku dinga shan wannan, zan ba Hajia Karima, in kun isa Abuja ta ba ko wacce nata kunji? ku tashi ku tafi". Parlo suka koma, Daddy yace kuje kuyi sallama da Mummynku, Abdulmajeed ya tashi a tare suka shiga suka isketa bakin Gado, Zaineema ta zauna a gefenta ta dora kanta kan kafadunta , Ziyada ta zauna a dayan gefen itama tayi hakan, Abdulmajeed ya tsugunna a gabanta ya dora kanshi shima a kan cinyarta, hakan ya karya zuciyanta, hawayen da take boye suka fara sunturi a idanunta, ta dora hannunta kan Kan Abdulmajeed tace "Dama ba zamu dauwama tare ba, dama dole wata rana na aurar daku, kuyi nesa dani, Aure Ibada ne, da banga abunda zai sa na rabu da ku ba, ku sani ina sonku fiye da rayuwa da kanta, ina matukar kaunarku, and babu abunda ba zan iya ba dominku, ina sonku 'Yaya na" dukkansu hawaye suke, Abdulmajeed yace "Mummy, muna tare, ba abunda zai rabamu, duk randa kika so ganina, ki kirani ki gaya min, InshaAllah duk abunda nake a Abuja zan bari nazo kiranki, i promise" shafashi tayi tace "I'm proud of you, take care ofNajwa kaji?" kai ya gyada mata, ta rungume yayanta mata tace "Allah ya muku Albarka" suka amsa da "Amin". Zaid da Najwa suma a dayan Dakin Mummy, Najwa sai kuka take tayi, Zaid na ta lallashinta yace "Haba Baby, ba wai nace miki ga gida ga gida zamu zauna ba? Meyasa kike kuka? Kina so ki tada hankalina ne? Maa DonAllah kice tayi shiru, zata sani kuka nima" Maa dai ta kasa magana don itama hawayenta na gab da digowa, chan dai tace "Kya huwa Najwa? Share hawayenki, zan dinga zuwa Abuja ganinki, kuma Bhaiy dinki zai kula dake, ga Mijinki me so da kaunarki, ga yaruwarki Ziyada, ba zakiyi kadaici ba, kiyi hakuri kinji?" "Maama ke kadai a gida akwai kadaici" tace "kar ki damu, baffa haruna ya bani Umaimah yace Aure ya rabanu, so wont be alone, zan sata makaranta ta tashi gabana" Najwa ta rungumeta tana gyada kai, nan Maama ta musu nasiha me ratsa zuciya kafin sukayi group hug. Yan Yola Zaid ya sa aka dauko daga Gidan Paapa, sunyi sallama dasu Maama, a cewarsu daga dakin Amarya zasu wuce Yola ba zasu biyo ta kano ba, itama Kaveri, da Mamanta da Vijhay bhaiyya sunyi sallama daga Abujan zasu koma India, Zaineema daga Abuja zata koma Gidanta, ba wanda zai dawo Kano dai a takaice, nan akayi Sallama dasu Daddy, suka musu fatan sauka lafia. Amarya aka dauka a Mota, mota yafi Ashirin akayi convoy zuwa Abuja. Sai Goma saura na dare suka iso Maitama, GidanAbdulmajeed na jikin Gidan Zaid, rabawa akayi, wasu zasu kwana Gidan Najwa, wasu zasu kwana Gidan Ziyada. *WasheGari* Da Safe Zaid ya sa aka kai Yan Yola Airport inda zasu koma Gida bayan ya musu Alheri me dumbin yawa, ya kuma rokesu da in suna bukatar wani abu su gaya mai" Kaveri ma da Mamanta an kaisu Airport inda zasu wuce India, Zaineema ma sun wuce Kaduna da khalid, Gidan ya rage Maauratan su kadai. *A GIDAN ZAID* Zaune suke suna kallon juna Zaid yace"My Forever, kinsan da Bansan meye love ba? Kinsan ni banda lokacin love, ko da Na'ila kece min tana sona kallonta kawai nake, banson me take nufi da tana so na ba, bansan me takeji ba, Ziyaa akanki na san meye So, duk wata soyayya da kika ga na nuna miki a da, in gaya miki gaskia words din Armstrong ne, amma yanzu i dont need Armstrong to tell me what to say to you my Forever, yanzu na san Sonki a jinina yake, my Forever, ina sonki sosai, i want to be with you.. No i need to be with you for the rest of my life" blinking idanunta tayi so biyu, tace "kaine best thing da ya taba faruwa dani, Allah ya bar mu tare" dagota yayi ya maidota jikinshi yana mata

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});