Chapter 147
Chapter 147
saka na aikata Sabo da Zunubai, saboda ita na sha Giya, duk na zabure saboda son daukan Fansa, saboda ita nayi hurting dukanku ba tare da saninku ba, daga kai Baba Abba, Abdulmajeed, Zaineema, Ziyada even innocent Zinatu, ba wanda cikinku be dandani Azabata ba, saboda tsananin Mugunta na, har a matsayin Kurma na zo musu ina kuntata musu ba tare da saninsu ba" durkushewa yayi yana kuka me ban tausayi yayin da dakin yayi shiru kamar ba kowa cikin Dakin, kowa da tunanin da yake a ranshi, barin ma Abdulmajeed da Nura Kurma ya fado mishi. Gaban Maama ya fadi, jikin ta yayi sanyi sakamakon jin kalaman da suka gama fitowa daga bakin Zaid, gabanta ya fadi, me yaronta ya Zama? Me daukar fansa ya maida mata Yaro? Me ya zama? Duk yanda take son share ma danta hawaye, duk yanda take son rungumarshi ta shafa bayanshi ta gaya mishi komai zai wuce yayi kamar ba ayi ba, duk yanda take son tabbatar mishi da she's here, ba zatayi ba, sai ta tabbatar da ya wanke zunubanshi ta hanyar tuba, sai ya nemi yafiyan duk wanda ya k'untatawa, sai ya gyara laifikanshi, in ba haka ba, shi da Mairo duk daya suke, ta san da wuya ta iya abun da take tunanin yi, amma Allah zai bata iko, don har ranta bata son Danta ya kasance cikin marasa Rungumar k'addara" A hankali ta taka gunshi ta sha mur wanda har ranta zuciyarta karyewa take, a kausashe tace "Zaid" da sauri ya dago daga durkuson da yayi, nan da nan bakincikin fuskarshi ta sauya zuwa farinciki, Murmushi ya darsu a fuskarshi da sauri ya mik'e yana kokarin rungumarta tare da fadin "Maaa" ja baya tayi kamar wanda dodo ya tunkaro, da mamaki suka bita da ido, banda shi da be damu ba k'ara nufarta yake, ita ko sai baya take kamar wanda abun tsoro ke bin ta daga k'arshe ta daga mai hannu tare da fadin "dakata Zaid, kar ka tabani" gabanshi kamar zai fadi k'asa, tsoro ya cika kirjinshi, hawaye dama ba su tsaya ba, baki na rawa yace "Maaa" duk binsu ake da kallo, Najwa ta karasa gun Maama, ta riko hannunta tace "Maama, me kikeyi haka? Baki ganeshi bane? Your Zaid? Wanda kike kuka kullum saboda rashinshi a India, Maama meyasa kike mishi haka, donAllah ki bari" kamar ta fashe da kuka haka takeji amma sai tace "Haka ne Najwa, amma nayi asarar hawayen da na zubda sabo dashi, bansan yana nan Nigeria yana zubda tarbiyan da na mai, bansan yana nan yana cutar 'Yanuwanshi na jini ba" Zaid ya zube k'asa kan guiwowinshi yana kuka kamar ba namiji ba yace "Kiyi Hakuri, Maaa, banda wani Zabi da ya wuce aikata hakan, tun ina karami na k'uddurta Niyyan tarwatsa Gidan Baba Abba don a ganina da saninshi aka kasheku, na san nayi laifi, amma wallahi dana san kuna da rai, da banyi abubuwan da nayi ba, da na bi ku India munyi zaman mu, Maa, kar kiyi fushi Dani" be tsaya jin wank magana ba, kamar me tabin kwakwalwa ya bude hanayenshi biyu yace *Wani Dan Halak zai ki yin komai in ya ji an kashe mai Mahaifa, an hau kan dukiarshi kuma shima ana neman hanyan kasheshi? Wani dan halak zai folding hanayenshi ya zuba ma Matar da tayi sanadiyar hakan idanuwa? Balle kuma Danhalak din na da Wadatan maida zaune tsaye a duk lokacin da ya so, wallahi ko da talaka ne ni sai na bi duk hanyar da zanbi na dau fansa, balle da kudina*. Da alama kwakwalwar Zaid ya tabu, tunda ga Mahaifanshi ga kuma kanwarshi ba ya bukatar kowa da komai, he's got Nothing to lose, indai zai kasance tare dasu, be damu ya rasa kowa da komai ba, su kadai ne Farincikinshi, zai gaya musu komai, be damu da abunda abun zai haifar ba, shi dai yana so a gama komai a gurin nan once and for all. Kujera ya samu ya zauna don basu labarinshi, farawa yayi daga randa ya gudu daga Gida, da haduwanshi da Alhaji Sadam Audu, da gajeren Tarihin Gatan marayu, da yanda ya nuna mai so kamar dan Cikinshi, da yanda ya ke kaunarshi, da yanda ya maida komai kan sunanshi, da yanda yake mai nasiha kan shan giya da daukar fansa da yake cewa zaiyi, da yanda yake shiga damuwa in yaga ranshi ya baci, komai ya gaya musu har bayan rasuwan shi. Kuka kowa keyi, sun tausaya ma Zaid matuka, Maama kuwa ji take kamar taje ta lallashe shi, ta bashi hakuri kan komai da ya faru, amma ta kasa, sai ta gama jin komai, Mairo kuwa, kunyar abubuwan da tayi takeyi, tayi nadama matuka, ina ma zata iya dawowa da lokaci baya ta gyara kurenta, amma kash, Bakin Alkalami ya bushe, Ya Cigaba da cewa; "Tun da na mallaki hankali na, na ke da labarin Gidan Baba Abba a tafin hannuna, na san shige da ficen kowannensu, na sa da suwa sukeyin Bussiness, nasan Alakar su da mutane, sannan abunda na sani shine, Matar Baba Abba bata hada Yayanta da kowa ba, daga son Yaya, sai son Kudi, a Porthacourt na girma, na son lungu da sakon bullo ma lamura, a nan na gane cewa, in kana so ka ga tashin hankalin Hajia Mairo to ka taba mata abubuwa biyu da suka fi komai mahimmanci a rayuwarta 'YA'YA, da KUDI, a hankali na fara taba Dukiyarta wanda ba nata ba da kuma Yaranta a lokaci guda, da Babban na fara". Karasawa inda Abdulmajeed ke tsaye yayi, Kuka Abdulmajeed yakeyi sosai yace "Ka tuna Yarintar mu?bana tunanin zaka tuna, ina dai so ka sani, Na tsani kaina da na sa k'afa na shure abubuwan yawa dake tsakanin mu a da, na tsani kaina da na cutar da kai don son ganin Mummynku cikin bakinciki, kana tunanin ta ina na cuceka? Bari in gaya ma, A hanyarka ta zuwa Abuja daga Kano a motarka Mercedez Benz akwai Ownership Documents na Abba Abu&Sons Furnishing Company, da wasu signed contracts na other shareholders, daidai Zuba akwai Yarana da suka tareka, suka kwace maka Mota wanda duk wani abu me amfani na cikin Motar wanda yayi causing dinku asarar almost 20%, in har zan tuna da kyau, harta kayan da ke jikinka sai da ka tube musu". Da mamaki suke kallonshi, AbdulMajeed ya bude baki, Daddy ko jinjina kanshi yayi, Mummy ta tuna bakincikin da ta shiga a lokacin ashe Zaid ne. Zaid ya dan dafa Abdulmajeed yace "dont be shocked bro, wannan ba komai bane. A hanyar dawowan Zinatu da Muhsin daga Makaranta, na sa an dauke min Zinatu, wanda akayi requesting 10mil, har mukayi waya" ya juya ya kallesu yace "kun tuna? Ya kalli Ziyada yace, "Har nace miki Ziyaa i'm coming for you?" Well lokacin ne dai, sannan kun tuna Nana Nakowa ai?" be jira amsa ba ya cigaba "Ni na azalzala mata ta hura wuta akayi aurenku, ranar auren Yarana suka je Gidanku, duk wani abu masu amfani suka kwashe, wannan shine Karayar Arzikin ku na farko, wanda sai da kuka saida Gidanku na Abuja wanda ni na siya ba tare da saninku ba don a ganina Gidan Baba na ne, kawai na karbi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169