Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 159

Chapter 159

Adade Ana Yi Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

wallahi, ina ganin all these are not enough, meye amfanin Arzikina in ban maka ba? Meye amfanina? Nidai ina rokonka Alfarma daya kawai if theres anything you need, anything, kawai ka gaya min, kar aji nauyi, kar kaji kunya, ni da kai daya ne" AbdulMajeed yace "Nikam i want to work, ina son yin aiki, don Danuwana ne Gatan Marayu ba zan zauna a gida na tankwashe kafana ba, nasan me kake tunani, kana tunanin yanke mana duka ayyuka, in ka yanke ma Iyayenmu wannan is understandable, yaci ace sunyo retire, kuma mu mun kawo karfin da zamu dau dawainiyansu, amma ni gaskia i refuse to be relaxed, ba zan zauna zaman banza ba, i know kana da kudin da zaka ciyar damu ka biya mana bukatunmu da mu da yaranmu da jikokinmu, amma ina so na tsaya da kafafuna, ina so nima in ga na tara ince wannan zufa na ne, nima ina kwadayin Lada, ina so wata rana in baka ince ka zuba a ZSA foundation, ina so nima in shiga sahun masu taimakawa Marayu, da gajiyayyu, ina so inyi aiki saboda gaba, Please kama maganata kyakyawan fahimta" Zaid yayi dan jim kafin yace "Da ina ganin muna da komai, ba sai kayi--" AbdulMajeed yace "Please Brother" Zaid yace "Fine, shikenan, zan kira connection na Alhilal Construction Company Dubai, zasu dinga baka contracts, and nan Nigeria zan nemi audience da Babatunde Fashola, zan kirashi na roke shi Alfarma, ya dinga baka Contracts din Zanen Roads, Housing, Highways, kuma nima in na samu irin contract din, zan gaya musu ina da Architect da Quantity surveyer" Rungumeshi Abdulmajeed yayi yana da bubbugashi a baya, dadi ya rufeshi, yace " Nagode danuwana, Allah ya ida nufi". Zaid ya ba AbdulMajeed takkaddun Gidajen da ya bashi, da kuma Motoci, sun yanke hukuncin zama a Abuja, nan zasu za zauna da Iyalinsu, Gidajen a jone suke da juna a unguwan Maitama. Ziyada zata koma Baze University zata fara a fresh, Najwa kuwa WAEC zatayi tayi joining Ziyadan, dama ko a Indian bata gama HighSchool ba, nan suka tsara komai, kafin suka sanar da Mahaifansu, dadi sukaji sosai. Kwanan su 5 a Abuja Visa dinsu ya fito inda jirginsu zai tashi a k'arshen Sati, k'arshen Sati Jirginsu ya daga zuwa India. I N D I A Bayan Faisal yayi Changing Dollars to Rupees a money changer, Taxi Uku sukayi, kamar kullum, Mama, Papa, Hajjo da Daddy a mota daya, Zaid, Abdulmajeed, Najwa da Ziyada a mota daya, dayan kuma Idi sai Faisal da ya baro bauchi don kasancewa tare da Gatan Marayu. Daddy ya gaya ma Driver inda zasu, wato Saritar Vihar, Shubham Palace Hotel, kasancewar sun saida Gidansu kafin su tafi, dole a hotel zasu sauka, Dadi kamar ya kashe Najwa. Tafian Awa daya ya kawo su Birinin Delhi, suka iso har gaban hotel din, a reception suka tsaya, Faisal ya tambayi Zaid Daki nawa zaa kama Zaid yace a kama 5 ko? , hakan ko akayi, suka karbi room 102 to 106Ziyada da Najwa daki daya, Paapa da Daddy na du daban, sai Maama da Hajjo, sai Zaid da AbdulMajeed sai Faisal da Idi. Bayan sun huta ne suka shiga cikin Sarita Vihar, tun daga farkon Layi Najwa take haduwa da idon sani, har suka k'arasa Gidansu Kaveri, dama basu sanar da su zuwan ba saidai aka musu suprise. Kaveri ta rungume Najwa, suna ta murnan ganin juna, Maman Kaveri da indiyanci tace "Ina yaro me sa mamanshi kuka?" Najwa ta nuna shi, Indiyanci take tana ma Maama barka da azziki ta ga danta, Zaid be san me ake cewa ba, sai dai Murmushin dole, da Indiyanci Najwa ta gaya ma Kaveri ga Fiancee dinta, nan Kaveri tayi tsalle tayi kan Majeed ta riko hannunshi, Najwa ta buge hannunta tana cewa ta bar taba mata Miji, sun dade a Gidansu Kaveri kafin Najwa ta zare jiki tayi Wurin Vijhay Bhaiya. Tun daga center Unguwan take kwala mai kira a guje "Vijay Bhaiya main bapaas aa gaya hoon(Brother Vijay, i'm back)" kamar cikin bacci yaji muryarta a guje ya kwaso ya fito, durkusawa tayi ta shafi kafanshi, kamar yadda aladarsu take, ya dagota yana jin dadi suka fara gaishegaisge da firan bayan rabuwa. Haka su Maama suka iso wurin, suka gaiggaisa, Zaid ya ma Vijhay Alheri, don yaji labarin yanda ya kulan mai da kanwarsa, Vijhay ya rungumeshi yana cewa da Indiyanci"Kai ne ke sa mamanka kuka ko?" Najwa ke fassara mai, shidai sai yake yake tayi. Daga nan Najwa ta kaisu Gidan Aisha kawarta, wanda ta bata kwarin guiwa sosai wurin zuwa Nigeria, tayi mamakin ganinta, nan dai aka danyi fira kafin suka bar gunta. Haka suka dinga Yawo a India, sukaje TajMahal, Shi dai Zaid Kasar nan be mai ba, shiyasa duk yawanshi kasashen duniya be taba zuwa India ba. Bayan Five Days A kwana 5 dinnan, duk sun gama shirin yin Engagement Party din Najwa da AbdulMajeed, Daddy yace "shi kawai tafiya zasuyi ba za su tsaya ayi shirmen nan dasu ba,ai ba aladarsu bace da zaace sai anyi wani Party na Alaadar Hindi, Zaid dai lallabashi yake don kar ya hana ayi, burin kanwarshi kawai yake son cikawa, ganin Daddy sai kushe abun yake tayi Zaid ya tarkatasu ya sasu Jirgi suka wuce Makka don yin Umrah. Nan Najwa da Kaveri da Ziyada suka dinga zuwa gaiyyatan kawayensu bikin engagement dinsu, wanda zaayi a wani kayatacen wuri a cikin Delhi. Haka dai ranan Engagement sukayi shigan Indiawa gabaki dayansu, har Zaid, sosai sukayi kyau, nan dai a kayi shagali taro ya watse lafia. Kwana biyu kawai sukayi suka tattara suka dawo Dubai. Nan ma yawon buda idanuwa sukayi, kafin sukayi siyayya da yawa. Zaineema ana chan America da Khaleed ya gama exams, suma cikin Satin nan zasu wuce Makka inda zasu dawo tare da su Maama Nigeria, lokacim befi kwana 6 biki ba. Bayan Yan Kwanaki. Yan dubai suka fara dawowa kafin 'yan Saudi, a lokacin har an kammala Gidan Daddy anyi furnishing dinshi da kayan Katakai masu kyau da tsada, wanda a companyn Daddyn aka siyesu, nan suka sauka, dadi kamar ya kashe Daddy da Zaid yace mishi Gidanshi ne, ya rungumeshi yana Godia, Abdulmajeed ma murna ya taya babanshi don be san da shirin nan ba, a ranar Zaid yace "Daddy ina rokon Alfarma ka bamu izini muje maka bikon Mummyn mu, kaga kar a kawo maka Amarya Uwargida bata nan" yace "haka ne, da kai na zanje na maido Maryam dita" duk aka hau shewa, har zuciyan Abdulmajeed da Ziyada sunji dadin yanda Zaid yayi, shiko na ciki na ciki. A ranar suka dunguma Gidan Aunty Aynarh da Tsaraba Nik'i Nik'i, su Zinatu su ka rungume danginsu, Mairon ce a Parlo, Zaid dai yana daga chan bayabaya ba wanda zai kula yana bayan, nan dai bayan yan surutai, da neman yafiya Mairo zata bisu a yanzu. Dakin Aunty Aynarh ta isketa din yi mata Godia, duk tana mata wani ladabi da biyayya "Aunty Aynarh, nagode kwarai Allah kadai zai biyaki" Aunty Aynarh tace "na fa sha gaya miki, ba don ke nake abu ba, da don ke ne da baayi ba, kuma wannan nok'e nok'en da kikeyi, na san fa halinki sarai, so kike in saki

Table of Contents

Chapters

169 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});