Chapter 94
Chapter 94
Cikin kukan sosai ta ce "ina fatan ciwon ya shige ni da 'karfi irin 'karfin guguwar iska, idan na yi sa'a ya dangana ni da kusheweta, wata'kila na huta da azabar da nake 'dan'dana da raina a cikin wannan duniyar". Kuka sosai take yi, wadda ya matu'kar dukan zuciyarsa sosai. Ya nisa ya ce "Zan tambaye ki, kinsan na san ki tamkar tafin hannu na, kar ki mini 'karya dan kuwa zan gane ki". Ta tsagaita da kukan, kafin ta bashi amsa ya ce "wa ya baki waya da agogo da kayayyaki a Jawad?". Zuciyarta ta buga ta 'barke da kuka tana cewa "Dan Allah ka fahimce ni, ba fa yadda ka ke zato bane". Ya busar da iskar 'bacin rai ya ce " ok to fahimtar da Ni! ina sauraron ki, warware mini". Da rawar murya ta ce "Tsakani na da Allah! Saurayin Safina ya siyo mata, ita kuma already tana da ita, shine ta bani, akan na bata rabin ku'din ". Ya yi murmushi mai sauti ya ce "Ina jin ki! A ina kika samo ku'din?" "Zobena 'daya na gold na bata, a hankali kuma zan cika mata sauran ku'din da suka rage tunda ba yawa". Ya yi shiru yana nazarin anya Sa'a za ta shiryu, yanzun nan ta tsara labari tamkar a wasan kwaikwayo ko a littafi? A kausashe ya ce "kuma ya aka yi naga ba sunanta bane akan rasit din siyan wayar?". "Malam! baka lura bane domin kuwa SB aka saka ma'ana Safina Bunkure". "Hmmmm" ya furta kawai ya yi shiru. "Gaskiya na fa'da maka Malam". Yace " idan kina ganin na gamsu ba Sa'adatu Bashir ake nufi ba. to ki fa'da mini, ta ina kika mallaki agogo mai daraja haka tunda English gold ne". Duka na Safina ne, kayan da ka gani kuma siyawa Jawad ta yi tunda Alheri ta samu ba ka'dan ba". Ya ce "alheri irin na 'yantattun Mata?" Jikinta ya hau ' bari ita kam tam ta shige su, kalma 'daya tak da ta fa'da ta wanke ta a zuciyar Mk! ta janyo Mata tashin hankali mai yawa, ta yi amanna har da wannan kalamin suka 'kara fusata shi, ya yi irin fushin da bata ta'ba hararowa zai yi ba, hakanan kalaman sun janyo ya kasa gasgata ta. A daren ta gane tuntu'ben harshe yafi zafi fiye da wadda za'a yi da 'kafa ta fashe. Jin ta yi shiru ya ce "Sa'adatu har yanzu ba ki shirya fa'da mini gaskiyar magana ba, bare na auna naga zan iya miki afuwa ko bazan iya yafe miki ba! Abin da nake son ki fahimta shine, ki daina yaudarar kanki cewar wannan laifin zai wanku a gurina da kwaskwarimar 'karya. matu'kar kin san ba zaki fa'da mini gaskiyar lamari ba to ki daina tunanin maganar zata bi ruwa da sau'ki." "Gaskiya na fa'da maka Malam! ka zafafa ne, ya kamata ace kasan abin da zan iya da wadda ba zan iya ba! ko ban tsira da komai ba, ka gaskata ni mana". "Ki mini adalci! wacce maganar zan 'dauka na gasgata ki akanta, alhalin tunda abin nan ya faru, kike ta canja magana, kin ce Sumayya ta baki, kin ce ta Halimace, kin ce ta Safinace shin wacce zan 'dauka na gasgata ki akanta?". Shiru ya ratsa amma zukatansu sai bugawa suke yi tamkar ana lugude, ya nisa ya ce "ki kwantar da hankalin ki, duk sadda kika yi nufin fa'da mini gaskiya, Ni kuma na miki al'kawarin zan saurare ki, nasan kuma zan sami nutsuwa a zuciyata tunda gaskiya a bayyane take bata bu'katar ado". "Malam na kusa kammala iddah fa, dan Allah " sai ta fashe da kuka fiye da na farko. Yace "Na sani! yau kika fara period 'din ki na uku, me kike jin tsoro?" Ta kasa yin magana, ya ce "Ni ya kamata na yi fargaba, Ni ya kamata na koka, domin zan rasa damata, sai dai na shiga sahun zawarawa, ke kuwa ai baki da damuwa idan har kina sona ai za'bin a hannun ki aka dam'ka shi". Cikin kukan ta ce "Ban son muje ga haka, Ni ka zo ka dauke ni mu koma gidan mu, na yarda kar ka ci abinci na, kar ka kula ni har sai ka gamsu kamin abin da ka huce". Ya ce "matu'kar muna tare kin san ba zan iya wannan jarumtar ba". Ya sassauta ya ce "ki dinga addu'a sannan ki bar komai a hannun Ubangiji. Abin da nake so ki fahimta, wallahi na fiki shiga damuwa da tasku, kawai ni jarumta na fiki saboda kasancewata Namiji! Sannan ba zan ta'ba sauya hukuncin da na yi mana ba, har sai kin fa'da mini gaskiya koda hakan na nufin rushewar farin-ciki na gaba'daya, duk lokacin da kika shirya fa'da mini gaskiyar magana, ki mini magana". Da haka ya kashe wayar gaba'daya. Ta yi sororo da waya a kunnen ta, tana kallon agogo da ya nuna uku da rabi da minti biyu. ' Har aka fara 'kiraye 'kirayen sallah barci bai iya surarta ba, tana ta tufka da warwara, ta yaya zata iya fa'da masa Khalil ne ya bata wadannan kayan? To akan wanne dalilin zai mata kyautar su ta karba? zuciyarta ta shiga harbawa, bare da ta tuno waccan kato'barar maganar da ta yi. Ta yi amanna har da wancan laifin ya sake girmama wannan laifin a zuciyar Mk, sai ta yi kamar ta fa'da masa gaskiya sai ta tsorata, a yadda tasan ya tsani Khalil zai iya 'kararsa ko dan ya ci mutuncin gidansu tunda mahaifin Khalil fittacen 'dan siyasa ne, ita kuma ta hadu da zubewar mutunci a idon dangi dama duniya gaba'daya tunda tasan suna chatting da shi, ha'kika Sa'a na cikin hali irin na canka ca kare. A fili ta dinga fa'din "Allah na tuba! na cuci kaina, son zuciya ya janyo mini 'bacin rai da damalmalewar lamura! Na keta alfarmar shari'a shiyasa na ke 'dan'danar 'bacin rai mai azabtarwa". Tamkar mahaukaciya take surutai, tana sake cewa "Na yi al'kawari idan har na koma 'dakina bazan sake yin wani abu na rashin gaskiya ta kowacce fuska ba, sai da nace wa su Halima ina jin tsoron abin da zai biyo baya ta mini ingiza mai kantu, na biyewa 'kawar zuciyata na gasgata su, waiyo waiyo! Lah ilah ha illah anta subhanaka inni kuntu minan zalimin". Duk akan kunnen Inna take wannan koke koken, da suratai duk da bata fahimci me take fa'da ba, da farko tsorata ta yi, ta 'dauka gwaiguna ne, sai daga baya ta fahimci daga 'dakin Iyah ne, a hankali ta fito, kasancewar Baffah yana Gogel. Har ta isa bakin 'kofar dakin, sai kuma ta fasa, ta juya a zuciyar ta kuma tausayin'diyarta ya fara kamata, ta dinga mata addu'ar samun sassauci a zuciya. Haka kwanaki suke ta shudewa, fargabar Sa'a na sake girmama, ba ta sake tuntunbar Mk ba, sai ana gobe za ta kammala iddarta, duk yadda ta kada billenta ta dinga ro'kon kar ya bari ta fita a matarsa bai ji ba, ya nan akan bakansa sai ta fadi gaskiyar lamari. Washagari ta tashi da zazzabi ga kuka ya ki yanke mata. Inna ta kasa jurewa yanayin da ta ganta a ciki, har 'dakinta ta shiga ta zauna kusa da ita,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157