Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 41

Chapter 41

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

juyo kan motar, ga ta ita ce a gefen hannunsu, ma'ana tana bude kofa dole kowa ya gan ta. A tsarin mahaifinta ba ma MK kawai ba, bai kamata mutanen gurin su gan ta ta fito a motar saurayi a irin wannan lokacin ba. Ta rasa yadda za ta yi ta fita, musamman yadda kayan jikinta suka kamata sosai duk da mayafin babba ne. Sai dai shara-shara ne, hijabi ta saka da za ta fito, saboda Inna ba za ta barta ta fita da wannan dinkin ba wanda anko ne telan Safina ya dinka musu, da ma nufinta tana isa zaure ta maka Hijabinta baki alaikum. Kunya da tozarci iri-iri suka dinga bin ilahirin jikinta, ganin yadda ta kasa fita a motar ya sanya Khalil fita ya zaga, ido biyu su ka yi da MK ya hura hanci ya dauke kai, ya bude gaban motar yana fadin fito, da kyar ta fito fuskarta a kasa ta kuma ja mayafin har kanta aka bita da ido, mazan da suke gun dukkansu a ransu yaba surarta suke yi har daya a cikin su wanda dan kwaya ne ya kasa hakuri, a fili ya furta "Kai waccan baby an zuba mata halitta Billahillazi da ina da kudi da na yi kerwa da ita." Tun tsayuwar motar MK ya ji zuciyarsa ta tsinke musamman da ya ga mace a gaban motar ta kare fuskarta, haka kawai ya dinga fatan kar ta kasance Sa'adah ce, ya san zai yi wahalar gaske ta zama ita ce, amma sai ya kasa nutsuwa, a lokacin da ya ga Khalil ya fito da gadara sai ya tabbatar Sa'adatu ce, take ya ji wani irin matsanancin kishi ya kama shi, irin kishin da yake danne soyayya. Maganar da wannan saurayin ya yi na yabon surar ta sai ya sake ninka bacin ransa wanda bai taba Jin irin sa a tsawon rayuwarsa ba. Zuciyarsa ta yi zafi, take ya ji yawun bakinsa ya kafe makogaronsa ya bushe, kansa ya sara da wani irin ciwo mai tsananin gaske. Ashe Sa'adah da Khalil ta fita, ashe shi yasa ta kashe wayarta, don ta nuna masa tana tare da wanda ya fi shi, ta kuma yarda ya kawo ta har titin da take da tabbacin zai iya ganin su a tare, karo na farko da ya ji ya yi kuskuren barin Farida saboda Sa'adah. Ya tabbatar ta fi ta son sa kawai dai shi Sa'adah ce ta fi shiga zuciyarsa, kuma ta fi daukar hankalinsa. Ko ta kan gyaran mashin din bai tsaya ba, ya tari abin hawa ya nufi gidansu, kafin ya isa wani irin zazzabi da azababben ciwon kai sun masa mugun kamu. Alkalamin *SURAYYA DAHIRU* ✍️✍️. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._* *A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*. *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. *TALLAH*. _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ 45-46 Tana shiga zauren gidan ta fito da hijab ta sanya, sukuku ta shiga gidan. A tsakar gidan ta sami iyayenta. Tsoron da ke cikin zuciyarta ya sake bayyana a fuskarta da jikinta. Baffa ne kawai ya amsa sallamar, da 'kyar ta tsugunna ta gaishe shi, ya amsa ba sakin fuska, ya kalle ta fuska ba wasa ya ce, "Daga ina ki ke?" Cikin rawar murya irin ta rashin gaskiya ta ce, "Zainab na raka gidan yayarta kuma sai da na tambayi Inna." A kufule Inna ta ce, "Tabbas kin tambaye ni amma ce mini kika yi ba za ku dade ba, don haka na gode miki da cika al'kawari." Ganin yadda ran Inna ya baci sosai sai shi kuma ya sassauta, ya mata nasiha tare da cewa, "yarinyar kirki in dai ta san kanta, killace kanta take yi a gida, bai kamata dare ya riske ta a waje ba." Har ya sallame ta sai kuma ya ce, "Yawwa dama zan fada miki, aurenki bayan sallah za a yi, nan da wata uku kenan. Bayan haka kuma na sanar da iyayen yaron cewar kar ya yi lefe, ni ma kuma ba zan wahalar da kaina wurin saya masa kayan daki ba, ke zan ba shi ina kuma da yakinin na miki tarbiyar da zai sami nutsuwa da ke. Uwarki kuma ta koya miki yadda zai yi alfahari da ke a matsayin uwar yayansa. Haka na yi wa Sumayya har yau din nan da ta kai shekaru goma a dakinta ban taba jin ance mini ga wani abu na kaico daga gare ta ba, mijinta kullum kara girmama mu yake yi, Ina fatan ki yi koyi da ita, Tashi ki je." Ta mike ta wuce dakinta cikin wani irin yanayi, tana zuwa ta fadi kasa ta fara kuka kasa-kasa, tana jin karshen tozarci an yi mata. Ta ya ya za a dinga hada Sumayya da ita, ai ba lokacin su daya ba, sannan ba iyayen mijinsu daya ba, a wannan zamanin ma an kai yarinya da kayan daki idan ba na alfarma ba ne, dangin miji suna yi wa yarinyar izgili da habaici, to ina kuma ita da za a kai ta tsurarta? Wanne irin raini da kaskanci za a janyo mata? Ba'kin cikinta ya ninku ta rasa inda za ta tsoma ranta. Ashe shi yasa MK yake mata gadara da isa, saboda an nuna masa sadaka za a ba shi an dauke masa lefe? Shima kuma kar ya sa rai za a je a yi masa jere. Ba ta san lokacin da ta bude murya ta dinga zunduma ihu ba. Daga Inna har Baffa a kidime suka mike suna rige-rigen isa dakinta a tuninsu wani abin tsoro ne a dakin, ko maciji ko kunama ta harbeta. Sai dai ganin ta ras illah kukan da ta bare baki tana yin sa tamkar yarinya yar karama yasa suka yi cirko-cirko! Baffa ne ya ce, "Mene ne ya saki wannan ihun sai ka ce wacce ba ta zuwa Islamiyya, ba za ki ambaci Allah ba! Sai ki cika mana kunne da kuka har da ihu?" Cikin kuka sosai ta ce, "Ka taimake ni Baffa! kar ka kai ni ba kayan

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});