Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 120

Chapter 120

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

A falonsa na waje ya tarar da shi bisa al'adar sa na zama ya gana da iyali, baya tashi sai 8 sai ya shiga ya kwanta zuwa goma sai ya tashi ya karya. Ganin da Alh yayi Mk na bu'katar yin magana da shi ya sa ya sallami iyalinshi, ya ce su basu wuri. Bayan sun sake gaisuwa. Mk ya sunkuyar da kansa kasa ya ce "Dama zuwa na yi, na fa'da maka, ina son kaje wurin Baffah ka tambayar mini auren Sa'adatu". Alh Isa ya yi shiru, yana jin wani irin bacin rai na taso masa. Mk ya sake yin kasa da kansa yana sauraronsa, amma tsawon lokaci bai ji Baban ya yi magana ba. Ya dago sai ya ga Alh yana goge hawaye a idonsa. A sanyaye Mk ya ce "lafiya kuwa Baba? Subhanllah! Ban san a cikin damuwa kake ba dana bari har ka samu nutsuwa". Sai lokacin Alh ya nisa cikin rawar murya ya ce "Takaicin yadda wannan ranar ta riske ni ne, Ni ka'dai babu mahaifinka, domin da yana da rai da bulala zansa na zane maka jiki don in tabbatar maka har yau din nan ina maka kallon yaro dan karami da bai kai yaronka Kabiru ba! na kuma ganar da kai irin isar da na yi da kai, don na lura ka manta. Amma tunda bashi da rai ai dole na yi ta ha'kuri da duk cin kashin da kuke mini tunda na san idan shine na mutu na barshi ba zai fita a cikin sha'anin ahalina ba". Hankalin Mk ya tashi, ya rasa inda zai tsoma ransa ya rarrafa jikin dattijon da girma ya sake kama shi ainun. Ya ce " Dan Allah Baba yanzu ma doke ni indai zaka huce! Ai komin girman da zanyi har gobe Ni yaro ne a gabanka dole na jira abin da zaka zartar". Hawaye ya sake zubowa Alh ya ce "Ai yanzu idan na dake ka kana iya daina zuwa wurina dan ka nuna mini abota ce kawai ta hada ni da ubanku ba jini ba, yau shekaru bakwai ina kwankwa'dar bacin ran jingine yarinyar dattijon arziki irin Malam Basiru, Ina fama da kunya da nauyinsa iri iri. Amma saboda Ubangiji ya zuba alheri mai yawa a zuciyarsa tunda nake jinyar nan da bana iya fita sosai duk juma'ah sai ya zo ya gaishe ni, ba tare da tunanin ina da halin da zan mayar masa da yarinyarsa dakin miji amma banyi ba. Ni kuma na san isane kawai ban yi ba, ka zo yin aure ka saka ni a maganar tsundum tare kuma da uban 'yar da ka saketa. Dan ya gane zan iya nemo maka sabon aure, na yarinyarsa ne ba zan gyara ba, Abin da baka sani ba na shiga lamarin aurenka ne dan kar na ji kunyar kushewa ne kawai! Sai yanzu kuma ka zo ka ce wai naje na nemar maka auranta, saboda kawai ka nuna mini amfanina a gurinka sai sadda ka so Abu akaran kanka, idan baka so ba kuwa da ni da wadda baka sani ba duk daya". Maganganun Dattijon ba karamin rikita Mk suka yi ba, ba karamin tayar masa da hankali suka yi ba. Ya kasa bude baki ya masa magana, sai ya hado kalmomi sai ya ga sun yi kadan su wakilci ba da nufin hakan ya yi ba, tsawon lokaci yana gurfane yana ta goge zufar da take yanko masa. Ya ciro wayarsa ya dinga lalubo lambar'karfi amma ya kasa saboda yadda kalaman Baba suka kassara shi, da kyar ya tsaida hankalinsa, ya samo lambar, Mahmoud! Ya na dagawa ya fara masa sababi ya dauka akan Sa'adah ne zai kira shi da sassfe, har yana cewa " Lokacin da ka rabu da ita menene ba'a fa'da maka ba akan ka yi hakuri amma baka ji ba". Murya a dusashe ya ce " Ina cikin masifa 'Karfi taimake ni ka zo ka same ni a gidan Baban Na'ibawa". A sukwane 'Karfi ya ce menene, ko jikinsa ne ya tashi?" A sanyaye sosai Mk ya ce"ka bar komai ka zo yanzu Dan Allah" sannan ya kashe wayar yana ta faman fadin innalillahi. Mintina biyar Mk ya kasa ha'kuri ya ce "Ka dubi girman Allah ka yafe mini Baba wallahi ba haka bane a Raina, amma na gamsu na yi laifi ban kyauta ba! ka mini afuwa fishin ka dafi ne. Baba abota babban al'amarine da ya wuce a kira shi da kawai, domin sai da Annabi ya jaddada mana mu ri'ke Aminan iyayen mu, mu sadar da ZUMUNTA da su domin ya nuna mana suma suna da Hakki akan mu, ina ba'kin cikin cewar da ka yi baka isa da ni ba". Alh baice komai ba, illah ajiyar zuciya alamun ya dade da abin yana cinsa a zuciya. Ya nisa ya ce "Idan ban yi hakuri ba yaya zan yi Muhammadu?" Dai-dai lokacin Mahmoud ya iso cikin tashin hankali, ya gaida Baba cikin girmamawa. Mk ya ce 'karfi laifi na yiwa Baba tsawon shekaru bakwai yake ta kallona da abin, Amma ya ce " takaicinsa daya da Baban Samira baya raye domin da a gabansa zai zane ni tamkar yadda za'a zane Jawad, shine nake so ka kawo masa dorinirka ta cikin motarka ka zane masa ni domin yanzu shi ko ya dake ni ma sai ya ji a jikinsa, tunda lafiyar lallabata ake yi, ka cire tausayi ka zane ni har sai ya ce ya isa haka". Da sauri 'Karfi ya juya mota ya dauko wata irin sharbebiyar dorina ta dukan dokinsa ce da ya mutu, shine yake ta ajiye da dorinar yana yiwa yaransa barazana da ita. Daga shigowarsa, yasa iyakacin karfinsa ya shammaci Alhaji ya zamba'dawa Mk dorinar nan, a kidime Mk ya zabura domin kuwa ba karamin kidima shi bulalar nan ta yi ba Ba dan tsananin jarumtar da ya saka a zuciyar sa ba, ba abin da zai hana ya zunduma ihun neman agaji. Alhaji ya ce "Ashha Mahmuda ai ba umarninsa zaka bi ba, ni zaka jira na baka damar yin hakan, maida bulalar ka dawo ka ji mai zance muku". 'Karfi ya fita, sai da ya ci dariyarsa mai isarsa ko banza ya rage zafin dukan da Mk ya yi wa zuciyar sa tunda amincin da ke tsakanin su ne ya haramta masa samun abin da yake so, da ya zurfafa tunani sai ya gane abotarsu ta yi karfin da zabin zuciyoyinsu ya zama iri daya. Duk da idan anbashi gida da mota akan a bashi Farida ba zai karba ba, kyan fuskarta da farinta bai zama abin burgewa a gunsa ba. Da alhini a fuskar sa ya koma falo ya gurfana a gaban Baba yana cewa "Ina rokawa Abokina afuwarka Baba, ni shaida ne akan yadda Mukhtar ya ke girmama lamarin ka". Dattijon ya miskuta ya ce " aminci na da mahaifin wannan yaron ya zarta karfin naku zumuncin domin ku da hankalin ku, kuka hadu amma ga shi nan kun zama tamkar cikinku guda! Ni kuwa tsakanin mu abota ne tun bamu wuce shekaru bakwai ba, da aka kaimu gabas almajiranci har zuwa yau din nan". Ya yi tari ya cigaba da cewa "saboda giraman abotarmu iyayen mu sai da suka zama tamkar shakikai ne duk

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});