Chapter 147
Chapter 147
ya dinga rarrashinta ya samu ta daina kukan. A hankali ta ce "Akan me zaka mini dariya bayan abin da ka janyo mini?" Da sauri ya ce "me na yi miki? "Abin da ka yi mini a Sokoto mana". "Oh sorry Sa'adah! na dauka abin ya wuce ai". "Ina ya wuce tunda kullum yini nake da yawu a bakina, ga idan Innah na girki sai dai na rufe daki, na yi ta amai ban son ta gane mai nake ciki." "Ya waske, da cewa to ana boye ciwo ne? Tashi muje ki ga likita". Ya kalleta gaba'daya ta yi laushi, ya san laushin da ta yi dan ta samu yadda take so ne. "Ni ba inda zani". Ya kuwa mike da sauri ya ce "shikenan na fita hakkin ki, mu yini lafiya". Tana daga zaune tasa hannu ta ru'ko rigar farar shaddar jikinsa. Ya juyo suka ha'da ido suka dinga kallon juna, suna jin wani irin tsumin soyayya yana tsuma su. Sa'adah ce ta yi saurin dauke kai. A hankali ta ce "da gaske na gama". Ya juyo ga'ba daya ya ce " Sa'a ba zai yiwu na tare da ke a hakan ba, kina musguna mini, ban isa ki mini yadda nake so ba, ban isa na ce ga yaddda zaki yi, ki ce to ba, haka kawai fa kika ce ba zaki tare ba, sanin kanki maganar ba a hannuna take ba, tunda Baba Kika fadawa, shine kuma ya bani umarnin na lamince miki ki kammala shirin ki, yanzu kuma cewa zai yi na nuna bai isa da ni a karo na biyu ba". Ta tura baki gaba ta ce "Amma ai da ka ro'ke ni akan ka kira shi , na fa'da masa zan tare da bakina". "Eh na fa'da amma sai na ga bai kamata na matsa miki ba, shekaru bakwai na yi ina kuakan rashin ki, Kinga kuwa duk dadewar da zaki yi kina shirin ba zaki kai irin wannan lokacin ba. Ki Bari ko wata uku ne, nan gaba sai mu san yadda za'a tunkare shi. Kuka ta fara tana cewa" ba wannan maganar, wallahi ba zan yarda Innah ta fahimci Ina da ciki ba, tunda ba za su gane da bada son raina hakan ya faru ba". Ya zauana ya fuskanceta sosai, sai kuma ya tafi ya yi sujjud shukur, ya dago yana cewa "Alhamdulillah, ubangiji ya raba ku lafiya, na dade ban ji farin-ciki irin na yau ba". "Tashi muje ki siyi abin da kike so a matsayin tukuici". "Ni ba inda zani". Ido kawai ya zuba mata, jikinta ya yi sanyi ta sunkuyar da kanta kasa. Ta mi'ke tsaye, tana tura baki gaba, irin wadda take yi masa a shekarun baya, mai ha'de da wani irin ta'bara da shi kawai take yiwa irinsa. Nan da nan jikinsa ya hau tsuma da sauri, ya matsa kusa da ita, ya rungumeta sosai, dukkansu sun shiga wani irin yanayi mai tsuma jiki da gangar jiki gaba'daya. A kidime Mk ya saketa ya shiga waiwayen inda zai ga hijabinta, can ya hango wani a ninke akan akwati. Da kansa ya ware ya fara kicinyar saka Mata. Tmda taimkonta hijabin ya daidaita. Ya kalleta sosai ya ce "Bari na fita, sai ki fito muje asibitin a duba ki, daga Nan sai ki raka ni unguwa". Ta kasa yi masa musu, tana tsaye tana jin yana yiwa Inna sallama, ya fice ya barta tana faman tauna maganar da zata fa'dawa Innah. Haka ta fito rataye da yar 'karamar Jakarta, ta kalli Inna da take kofar kicin a tsaye, ta ce "Inna zanje asibiti, daga nan kuma zan wuce gidan Maman Khalifa". Ido Innah ta bita da shi tabbas tana ganin kasala a tare da ita, kuma ba kasafai take cin abinci ba. Ta ce "wanne asibitin zaki je?" "Ban san wadda zai kai ni ba, Ni ba dan ya dage bama, da ba wani asibitin da zani, na san zazzabin cizon sauro ne". "To sai kin dawo, amma kar ki kwana gidan su Khalifa, Baffan ku baya gari, gara ki dawo mu kwana tare". Sa'adah ta amsa da cewa "To Innah". Innah ta sake cewa "ki kula da kanki, ki lalla'ba shi, kar ki yi abin da zai ja hankalinsa akan ki, har sai anyi tariya. Ni ba gaskiya ba zaki mini wata uku a gidan nan da auren ki ba, wanan watan da wani watan ya isa, koma kudin bai isa ba, kina dakinki sai ki dinga siyan abin da kike so, tunda dai ai ansan mu masu karamin karfi ne". A sanyaye Sa'a ta ce "Hakane Innah! Ni idan kin ce ma a wannan watan na tare zan yi biyayya ba dan Ina so ba, sai dan na nuna miki na fi girmama ra'ayin ki akan nawa". Sosai Innah ta zuba mata ido tana son ta gasgata maganar Iyah, amma bata san meyasa take ganin tamkar akwai wani abu da yasa ta sauko haka da wuri akan tariyar ba. Ta tafi, Inna ta bita da addu'ar dawowa lafiya. Suna tafe yana ta yawo da su akan titi, shi kansa tunanin inda zai kaita yake yi. Can ya kalleta ya ce "wanne asibitin kike zuwa yanzu?" A hankali ta ce "Ni fa na je asibitin an duba ni, ta butde jakarta ta fito da magungunan da aka bata tana nuna masa. Ya ce "To sannu My Sa'adah". "Yanzu bari ki raka ni unguwa" Basu zame ko ina ba sai gidansa na rijiyar zaki. *Ina ta shan korafi daga makaranta cewar yanzu yanga nake yi, ko kadan ba wannan maganar, a farkon fara posting Ina da pages masu yawa a 'kasa, a yanzu kuma babu, sai na yi typing kafin na turo, kowa ya san akwai hidimomi irin na yau da gobe akan kowanne bawa.* *Ni Kuma har da ciwon idon da yake sani rauni a typing din, Ina fatan za'a yi hakuri, saura kiris ma mu kammala, ban yi tsammani labarin zai yi tsayi haka ba* *Zan sanar da cewa ba kullum zaku ga update ba, amma ba zai dinga daukan lokaci ba* *Na gode sosai da yabawar ku kan rubutuna*. Surayya Dahiru ✍️✍️. *HALIN YAU*! *NA* *SURAYYA DAHIRU*. *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ *TAIMIYYAH*❤️ Ina kuke ne masoya kuma makaranta littafan Hausa,me kuke jira baku afka cikin wannan tafiya ba? ko kuna da labarin cewa shahararriyar marubuciyan wato Ayshat Ɗansabo Lemu,marubuciyan👇🏻 *LAIFIN ƁOYE* *HAMAL* *HURAYYAH* *BURIN ZUCIYA* *ƘALUBALE* *NAILAH* *INA DA HUJJA* ta sake yinƙurawa domin tazo muku da zazzafan labarin ta me suna asama,domin faɗakar da ku da kuma nishaɗantar da ku,haɗi da koyar da ku dibarun girkunan zamani da gwangwaje ku da salon soyayya me tsayawa a zuci,duk acikin wannan shahararran labarin nata me suna *TAIMIYYAH!* Labarin da yazo da wani irin salo me cike da ban tausayi do motsa zuciyan me karatu,duka wannan zai zo muku akan farashi me sauƙi,da kuɗin ki 500 kacal zaki mallaki naki don gujewa shiga hakkin marubuciyan,zaku biya kuɗinku ta wannan asusun kamar haka👇🏻 *0504192664 Aisha Ibrahim Dansabo GTbank.Sai ku aiko da shaidan biyanku ta wannan layin 08167768704.* *Masu turo katin waya zaku
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157