Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 134

Chapter 134

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kin nutsu ba. Mutari shi nake so ya zame miki miji a karo na biyu". Da rawar murya ta ce "To Baffah! Na ji, na kuma amince zan yi maka biyayya, zan yi ha'kuri na zauna lafiya da shi komai runtsi". Da murna Baffa ya ke cewa "Na gode miki in sha Allah ba zaki yi nadama ba, ubangiji ya miki Albarka, ya zaunar da ku lafiya, ya baku zuri'a mai albarka". Ya nisa ya ce " ku shirya gobe zamu je Gogel ki fa'dawa Yaya Ayuba kin amince ba dole na yi miki ba, Sannan ku samu lokaci ku gano Mutari domin yana jin jiki" Da sauri lya mike yana cewa "Bari na bi su Alhaji na fa'da musu wannan labarin mai da'di". Inna ta bi bayansa da ido har ya fice daga gidan, tana ayyana girman soyayyar da yake yiwa Mukhtar. Kai tsaye gidan Alh Isa ya dosa, a kofar gidan ys tarar da Dr 'Karfi zai shiga mota, ai kuwa ya ce "Mahmouda zo mu shiga, ba tafiya zaka yi ba". Baffa da murna yake fa'da musu "ai yanzun nan yarinya ta tabbatar masa ta amince, dan haka ku zama cikin shirin zuwa Gogel, a satin nan. Domin a son raina ku tafi da sadaki, a ranar da kuka je a daura auren a huta, kafin ta sake botsarewa saboda na lura kishin banza ta bari yake rinjayar ta". Daga Baba umaru har Baba Isa kowa ya yi shiru amma suma jinjina alherin bawan Allahn nan suke yi, da karfin son da yake yiwa 'dansu. Baba Isa ne ya yi karfin halin cewa "Malam Basiru ka dai matsa mata ta amince, gashi muma zamu sake yin son rai, mu amince da abin da ka zartar domin a samu lafiyar yaron nan ta dai-daita, bamu da bakin godiya, abin da zamu ce maka daya ne, da ikon Allah mu kabawa amanar yarinyar nan, mune iyayensa abin da ya faru a farko ba zai sake maimaituwa ba da ikon ubangiji. Kira mini yarinyar a waya" Baffa da ya san bashi da fargaba da azama ya fito da wayarsa. Bugu 'daya ta dauka, ya ce " Baban ku na Na'ibawa ne zai yi magana da ke". Kalaman kwantar da hankali tare da yabo da kuma girman mai hakuri Alh Isa ya dinga yi Mata, ya sake jaddada mata kar ta sake yin shiru har sai abu ya girmama, komai ya taso matu'kar yafi karfinta to ta sanar da shi zai magance mata da ikon Allah. Ya rufe maganar da cewa ko kina da korafi domin mun tsayar da kwanaki biyar masu zuwa na daurin auren ku". Zuciyarta ta buga sosai, cikin rishin kuka ta ce "Ba ni da matsala Baba! Amma zan ro'ke ka dan Allah a bari sai na kintsa sannan ayi tariya". Da sauri ya ce "Na miki Wannan laminin ki shirya a nutse, ai na san tutsiye Malam Basiru ya Miki ko na ce karfa-karfa, dan haka daga wata daya zuwa wattanni shida ki yi shirinki a hankali, bu'katar mu dama a daura auren hankalin kowa ya kwanta". A yammacin ranar suka je asibiti ita da Inna har da Sumayya. Har suka gama zamansu barci yake yi, wannan barcin shike daga hankalin kowa, ya rame kwarai da gaske. Har waje Hajiyar Bichi ta rako su, tana ta faman godiya, yayin da tausayin Hajiya ya lullube Sa'a, kallonta kawai take yi saboda yadda ta zabge ta yi zuru zuru tabbacin tare suke yin jinyar ita da Mk. Cike da rauni ta ce musu "Idan har zuwa gobe bai samu sassauci ba, zan tura Ahamad ya dauko Jawad ya zo ya ga ubansa don".. sai kuka ya kwace ta kasa karasawa. Jikin Inna ya mutu kwarai da gaske, ta dinga bata ha'kuri tare nuna cewa cuta ai ba mutuwa ba ce. Har suka isa gida ba mai cewa komai saboda ba su zaci haka jikin Mk ya yi tsanani ba. Washagari cikin ikon ubangiji jikin Mk ya yi sau'ki domin har cire masa oxygen aka yi, sannan ya yini idonsa biyu. Akan idonsa Inna da Sumayya suka iso, sosai ya ji da'din zuwan su tunda ya lura, sune kanwa uwar gamin wurin tunzura Iyah, sune suka hau dokin na ki, da tallafin su ta sami kwarin guiwar yi masa bore. Amma da ya tuna wai Sa'adah ya gani da Khalil sai ya ji wani irin kunci ya mamaye zuciyarsa! Tabbas ya yarda a duniyarsa bashi da wani kalubale irin Yaron nan, sannan yadda Khalil ya zama tsalelen saurayi na kerewa Sa'a ya sake tayar masa da hankali kwarai da gaske, domin kowacce mace ta ganshi zata so mallakarsa a matsayin miji. Ba komai ke nukurkusar Mk ba irin kishin Khalil, a sanadinsa ya rasa aurensa da matar da yake so fiye da kansa, gashi har yanzu basu rabu ba, ya tabbatar Khalil ne ke da nasara akansa, wani irin karfin zuciya ya shige shi, ya dinga kalubalantar kansa meyasa ya kasa mantar da shi a zuciyar Sa'a tamkar yadda ta mantar da shi soyayyar Farida a lokacin da suke tare. Ya saki ajiyar zuciya yana jin ciwo mai yawa a kirjinsa mafi girma a ciki haushin Sa'adah yake ji kwarai da gaske, a gaban kowa take fa'din bata sonsa, amma dan lalacewa tana soyayya da yaro sa'anta. Su Innah na zaune Farida ta iso dauke da kwandon zuba abinci. Tana kallon Sumayya ta gane sister din Gogel ce, duk kuwa da Sumayya fara ce tas. Har kasa ta tsugunna ta gaishe su. Hajiyar Bichi ta ce mata "Kakar Jawad ce da Yayar Mamansa" Da girmamawa ta sake gaishe su, a ranta sai take ganin Gogel da yayarta dan sun yi kyau ba zai zama abin mamaki ba, domin ko a yanzu da Inna take cikin shekarun tsufa, tana nan da kyaunta, mai kyakkawan jiki ce da yake boye tsufa. Wata'kila haka mahaifin su yake, dan ta lura ba kammanin Inna a tare da Gogel, Sumayya ta fi kama da ita, wanda hakan na alamta cewa mahaifinsu ma ba baya bane. Sumayya ta 'karewa Farida kallo tsab, takaicin Iyah na kamata da ta dinga kukan Mk ya auri Farida dan ta fita kyau ne, a yau da taga zahairin Farida ba hoto iya fuska ba, sai take ganin ba karamin kerewa Iyah ta yi mata ba. Kawai fararen mutane suna da kwarjini ne ta yadda ake ganin kyaunsu ko da kuwa masu 'karancin kyau ne. Farida bata dade da isowa ba, su Inna suka yi sallama suka tafi. Suna isa gida suka tarar da Sa'adah cikin kwalliya ta birgewa, amma tana kwance a falo tana kallo. Inna ko zama ba ta yi ba, ta hau ta da fa'da "Iyah cewa ki ka yi zaku tarad da mu a asibitin tare da Zainab, ashe karya kika yi mini?" Cikin rashin damuwa ta ce "na shirya jiranta nake yi". Kafin Inna ta sake magana Zainab ta kira wayarta, sannan suna jiyo horn dinta tabbacin ta fita, ba shigowa zata yi ba. Ta mike tana fa'din "gata nan ma, sai mun dawo". Sumayya ta ce Yanzu irin wannan kwalliya tamkar kin manta asibiti zaki ba gidan biki ba?". Dake Yan darun akusa suke ta ce "Anty ke kika manta cewa ni wannan ban

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});