Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 88

Chapter 88

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

cikin sanyin jiki ta kalli yadda ta ke kuka jikinta har 'bari yake yi, ga wata irin rama ta yi, har ba'ki ta ga ta sake yi mata sosai. A hankali ta;ce "kin tasa ni a gaba kina irin wannan kukan mai tayar da hankali, amma kin 'ki bu'de baki ki fa'da min mai ya same ki, ba Kya jin tsoron ciwo ya kada ni, kinsan fargaba da zullumin da nake ciki?" **** Mk na zaune a shago, amma jinsa yake tamkar a cikin rijiya saboda tsananin yadda ya takura ga wani irin matsanancin kishi ya matse kofofin numfashinsa, ya sababa masa azabben ciwon kai mai tsananin. Yawun bakinsa ya kafe sai daci yake ji har makoshinsa! ya ciro wayarsa ya kira Mahmoud ya sanar da shi, yana cikin matsala ya zo gidan Hajiyan Bichi ya same shi. Ya fito kai tsaye ya tari mai acaba(A lokacin ba a hana ba) ya kai shi gidansu, dan bashi da sukunin da zai iya tu'ki, domin al'amarin na nisa damuwar sa na 'kara girmama, wani abu ne mai tsananin ciwo ya tokare a 'kahon zuciyarsa mai azabtarwa. Yana isa kai tsaye can cikin dakin Hajiya ya shige ya wuce ta a falo tana yanka kankana. Mamaki ya kamata, ba zata iya tuna yaushe rabon da ya shigo ya ganta a falo amma ya zarce uwar daki ba. Ta yi jim, tana sauraronsa ganin fitowarsa, amma abin mamaki mintina fiye da goma sun shude bai fito ba, dan haka sai ta mike ta bi bayansa dan jin ba'asin wannan sabuwar dabi'a. Yanayin da ta tarar da shi ya tabbatar mata akwai matsala, da azama ta isa gareshi tana cewa lafiyar ka kuwa? A hankali ya ce"kaina tamkar zai fashe Hajiya" Da jimami ta ce "Ai da Abbas ko Akil ka kira wani ya raka ka asibiti, a kwanta da ciwo ne ba a sha magani ba?" Dai dai lokacin Mahmoud ya iso suka gaisa da Hajiya da ta fito falo tana masa iso. "Shiga! yau zuwa ya yi ya mini sake sake a gado da sunan ciwon kai". Mahmoud na dariya ya mike yana cewa " Hajiya ai gara ya kwanta ya more da zarar kunga mun yi aure shikenan sai ku dora mana dukkan girma alhalin matu'kar kuna raye mu yara ne 'kananu". Ya shige cikin dakin. Kallon Aminin nasa ya yi ya tabbatar yana cikin tashin hankali babba. Yasan karfin zuciyar Mk duk abin da ya bayyana a jikinsa tabbas ya yi tsamari ne. Da gaggawa ya shiga ya zauna a gefen gadon, ya na fadin "me ya ke faruwa ne?" Cikin rawar murya Mk ya dinga yunkurin magana amma ya kasa yi, ga mamakin Mahmoud sai ganin kwalla na gangarowa ta gefen idon Mk. Take hankalin Mahmoud ya yi tashin gauron zabi, murya kasa kasa cike da tsantsar aminci da kulawa, ya ru'ko hannuwansa ya ce "Yi hakuri Mukhtar! Fada mini damuwarka in sha Allah I will stand for you". Da rawar murya Mk ya dinga ambaton Sa'adah, Sa'adah". A hanzarce Mahmoud ya ce" me ya same ta, me ta yi?" Da 'kyar ya bude baki ya ce "mun rabu, na saketa Mahmoud"! ya karasa da murya mai cike da tashin hankali. Wani irin zabura Mahmoud ya yi ya mike yana cewa"How comes, akan me? subhanllah!" Shiru ya ratsa dakin! kowa tunani, na katantanwa da shi. A kasan makoshi Mk ya ce " ka fa'dawa Hajiya, tashin hankali na yadda zan fa'da mata, da yadda za ta karbi lamarin". Mahmoud ya zuba masa ido, yana kallon irin yadda Aminin nasa ke zu'ko numfashi da 'kyar tamkar mai fama da cutar asma. A hankali ya koma ya zauna yana jin tashin hankali shima na ziyaryartar sa. Tausayin Mk ya ratsa shi ya sake ru'ko hannuwansa a karo na biyu ya sassauta murya ya ce," Ina fatan sakin sunna ka yi, ina fatan mu gyara wannan matsalar kafin su Hajiya su ji, yanzu ina ita Sa'adah ta ke?" Cike da rashin kuzari ainun ya ce "Na kaita gidansu, saki daya na yi mata, abin da nake so ka fahimta, da abin zai gyaru da ko kai ba zan raba 'bacin ran da kai ba". A hankali Mahmoud ya muskuta ya ce "Kar ka yi haka, ka yi hakuri mana, da wanne irin ido za ka kalli dattijon arziki irin Baffah?" Wannan karon Mk ne ya tamke hannun Mahmoud ya zarce da cewa "shine babban tashin hankali na, fiye ma da yadda nake jin fargabar da Hajiya za ta shiga, amma kuma bana jin zan iya cigaba da zaman mu tare, iya adadin zaman da 'kaddara ta hukunta za mu yi kenan, ka fa'dawa Hajiya sai muje ka raka ni wurin Baffah, duk da bana jin dadin jikina". Ya fada a sanyaye cike da yankewar Buri. "Mukhtar Nima ba zan iya fa'da mata ba, da wanne baki zan fadi wannan 'bakin labarin?" "Cike da rauni ya ce " daurewa za ka yi Mahmoud". Shiru ta ratsa dakin a karo na biyu, nazari soasai Mahmoud ya ke, yana tunanin wacce irin 'kaddara ce mai zafi ta raba Mk da Matar da ya shaida yafi sonta akan kansa? Yana son jin menene ummul aba'isin wannan matsalar, amma kuma tunda Mk bai bu'da masa ba, shikuma ya yi al'kawarin ba zai tambayi komai ba, zai kuma yi dukkan mai yiyuwa dan ya sulhunta tsakanin su. A dabarance Mahmoud ya 'daga murya ya ce "Sam bazan iya fadawa Hajiya wannan tashin hankalin ba, kai da ka yi, kaine mai fa'da ba Ni ba". Ai kuwa wannan kalamin na Mahmoud ya janyo hankali Hajiya, da azama ta fa'da 'dakin tana fadin " menene ba za ka iya fada mini ba Mahmoud! wanne tashin hankalin ya rakito?" Dukkansu suka yi shiru aka rasa mai bakin magana, ta zauna da'bas a 'kasa tana salati, da fatan ba wani rashin gaskiya Mk ya aikata ba. Ganin irin damuwar da ta shiga yasa Mahmoud yin 'kundunbalar fadin "Hajiya ki yafe mu, ina ba'kin cikin sanar da ke yau Allah ya 'karar da zamansa da Sa'adatu". Salati mai 'karfi Hajiya ta rafka, tana cewa "Kar ka jinginawa Allah'karar zamansu, jingina masa, dama ya da'de yana fatan rabuwar, ganin ya kasa samun damar shine yanzu ya murde zaman da 'karfin tsiya." "Oh ni Rabi'atu ina ganin tasku, da wanne 'bakin ciki zan ji? da wadda yan'uwanka suke guma mini, ko da naka? Alhaji da Hajiya Babba sun mutu sun barni da ku, kuna neman kashe ni da ba'kin ciki". Ta fara hawaye, tana gogewa da hannun zaninta . Da ga Mk har Mahmoud sun yi laushi tubus da jin kukan Hajiya, hankalin su kuma ya sake tashi matu'ka, da rawar murya Mk ya ce "Na roke ki, ki daina zubar da hawayen nan dafi ne a rayuwa ta, da kinsan azabar da nake 'dan'dana na tabbatar da sai kin sassauta mini, ki yi hakuri Hajiya ba yadda zan yi ne, abin ne ya fi karfina, ki mana addua ki kuma yafe mini". "Yanzu ina Sa'a din ta ke?" Mahmoud ya ce "tana gidansu, yanzu ma komawa zamu yi dan bamu sami Baffan ba". Hajiya ta sake sa salati tana tafa hannu, tare da cewa "yanzu idon ku, idon tsohon nan ku iya fa'da masa

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});