Chapter 68
Chapter 68
fadin "kice cin fuska ya miki? banga laifin ki ba, dole ki guji magani, ko nice haka zan yi". Shi dai Mk ya zama tamkar gunki, yana kallon shari'ar son rai a wurin Hajiya. Ba zato Hajiya ta ce yaje ya siyo wasu maganin. Ya ce " Bafa su bane, tunda take wannan bala'in na zubar da su, na siyo masa wasu, amma ta "ki bashi" Da rawar murya ta ce "Billahillazi, baka canjo wasu ba, duk abin da ya fito ta hannunta, na tsane shi, zan kuma gane". Jin haka yasa Hajiya fadin "Bar Wannan gadddamar je ka siyo wasu a bashi ya dan sami sauki" Bai q musa ba, ya mike, ya dauki ledar maganin, ya fita. Sai da ya fita Hajiya ta dinga mata nasiha, tare da cewa "ki rage nuna masa kishinki a fili, sai ya samu dalilin da zai dinga musguna miki". Ta kalleta tace "tunda da wuta jona ruwan zafi kuyi wanka". Ta mike ta cika buta ta jona, mintina kalilan ta kashe kanta, ta juye, ta sake maida wani, kafin ta fito, Hajiya ta wanki Jawad a bandakin tsakar gida. Ta dama musu kunu, ta juye a flask din shayi, ta zubawa Jawad a kofi, ta bashi, ya shanye tas har da kari, ta tabbatar shima har da yunwa ta sake gigita shi. Sa'adah ta fito sanye da riga da zani na atamfa, dinkin ya zauna sosai, mussaman da bata cika daura zani ba. Ta mikawa Hajiya kayansa, sai da ya koshi ta koge masa baki sannan ta saka masa kaya, dai dai lokacin kuma, Mk ya dawo dauke da magungunan, leda biyu, ya mikawa Hajiya, sai da Sa'adah taga na wurin Farida, ga kuma wadda ya sake siyowa, sannan ta saki ranta, a ransa fadi yake masifaffiya kawai. Take Hajiya ta bude ta bashi, ta shafa masa na shafawa, barci ya dauke shi mai nauyi. Sosai Hajiya ta musu fada, kuma duk na Mk yafi yawa, jan kunne 'daya, ta yiwa Sa'adah, kar ta sake saka Jawad a cikin fa'dansu, ta ki cin abinci, shi akan mai zata hana shi? Ta cika kofi, da kunu ta mika wa Sa'adah tace "Shanye ki bani kofin". Ta karba, ta fara sha, ya mata dadi sai kamshin kayan yaji yake yi. Shi dai Mk yana kallon ikon Allah, anbawa Jawad, da Sa'a, shi ko oho. Sai da Sa'adah ta shanye sannan Hajiya ta mike ta ce "zan tafi nasan ki da jin magana, na kashe wannan magana kar a kuma tada ta" Da sauri ta amsa da "in sha Allah ta wuce". "Na gode Miki Sa'a, Allah ya miki albarka". Sa'adah ta amsa da "Ameen Allah ya kara girma" ta tashi tana mata rakiya hanyar waje. Tare suka fita da Mk zai kaita, a hanya tana sake masa fa'dan, lallai ya kiyayi zungurar Sa'a, ta dora da cewa "Kana ganin irin yadda take mutunta ni, tana haba haba da yan'uwanka, iyayenta mutanan kirki, lallai ba zamu shirya da kai ba, idan kace zaka wulakanta ta, mussaman ma akan wacce bata zo hannun ka ba". Har ya kaita gida, kashedi take masa iri iri. Da za ta sauka ya ce "kin basu kunu, amma Ni baki bani ba". "Ina sane, kai Sa'a ce mai ba ka". Murmushi ya yi, tare da cewa "Hajiya kar kisa na fara kishin yarinyar nan, naga tana neman zarta ni a gunki". Ta yi murmushi tace " maza ka juya ka sake rarrashin ta, ka tsaya a hanya ka siya musu dan wani abin, kunu kadai bazai ri'ke ta ba, ta tara yunwa". Haka kuwa, ya biyo ta titin Hausawa bawo road ya siyi wainar shinkafa da ake yi mai dadin gaske, a falo ya tarar da ita, tana zaune tana kallo. Bata dago ta kalle shi ba, ta amsa sallamar sa, daga haka bata kara magana ba. Ya tsaya ya ce "Ba ki mini sannu da zuwa ba fa". Ba tare da ta kalleshi ba, ta ce "inace ka ce kowa ya yi harkarsa?" "Na fa'da! amma dai Hajiya ta kashe maganar, ta ce kar a kuma tada ta". "Ita maganar maganin Jawad ta kashe". Ya zauna, yana cewa "ga waina na siyo miki, tashi ki zubo mana". Kanta a kasa ta ce" ci abinka". Ya kai kicin ya adana, ya zubo wadda zai iya cinyewa, tare da kunu a kofi, yaso ya shiga dakinsa, sai kuma yafi zumudin zama kusa da ita. Ya zauna yana fadin "dan Allah sauko ki taya ni ci". "Ba zan sake cin abinci da kai ba, tunda muka yi aure, baka taba kaini restaurant munci abinci ba, amma ka dauki wacce kake so kun je! ba ruwana da sabgarka". Ta fa'da hawaye na balle mata, ya yi shiru, yana jin sabon tashin hankali, ya rasa da bakin da zai kare kansa. Ya yi shiru, ya kasa cin abinci, ko kaffara ba zai yi ba, su Safina ne suka kawo mata wannan labarin. "Ki yi hakuri kin ji Sa'adan Uncle". Kamar ya watsa mata garwashi, ta zunkudo ta ce " ta Ina ka zama kawuna?" Kai ba 'kanin Baffa bane, bare na Inna, daga jiya ba zaka sake jin bakina ya kiraka da Uncle ba, ita dai da kuka hada dangi, sai tayi ta fa'da na bar mata" "Ashe lokacin da kace min dole kayi kishin mace, idan ka ganta a gaban motar wani da ba Muharraminta ba, 'karya ka fada tsagwaronta? To ita mai kuka hada daka dauketa a gaban motarka?" Kansa ya kulle, ya kalleta ya ce "Na yarda ban kyauta ba, ki yi hakuri, ki bani wata damar, ko banci albarkacin komai a gunki ba, naci albarka cin mahaifiyata da tazo ta baki ha'kuri, ta kashe maganar". Jikinta ya yi sanyi, ta ce shikenan na ha'kura". Da'di ya kama shi, ya matsar da kwanon abincin kusa da ita, ya ce to sauko muci". Ta girgiza kai, "Na hakura, amma ba zanci da kai ba". Ya tura mata, "to ci wannan, bari na zubo wani," ya mike ya fita da sauri. Cikin sa'a ranar bashi da lakca sai 'karfe daya, dan haka, bai fita ko ina ba, yan tare da ita, yana ta kokarin wanke mata zuciya, shi da kansa ya tabbatar a duniya ba abin da yake so sama da Sa'adah da 'danta, idan aka cire Hajiya. Sai dai duk nacinsa bata yarda da shi ba, kan dole ya 'kyale ta. Kwana biyu tana mai yawo da hankali, kafin ta ha'kura ta sallama masa kanta, cikin rawar jiki yake komai, yana ayyana distance fa yana da amfani, domin ji yayi ta dawo masa sabuwa. Yana samun kudi kuwa, ya dauke su ita da Jawad suka je restaurant din Royal Tropicana suka ci abinci, suka yi hotuna, irin wadda ake wankewa a take, take & wash, suka zarce country mall, ta zabi abin da take so. A hanya ya ce "shikenan yanzu na dawo Uncle?" "Hmm! magana ta wuce ka daina dawo mini da ita". Ya shagwabe fuska ya ce " idan har da gaske ta wuce, then called me Uncle". Ta fara dariya, tana cewa "ashe son girma ne da kai ban fahimta ba?" Shima ya taya ta dariyar sannan yace "tsakanin ki da Allah! Idan nace Miki Sa'adatu ba kya jin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157