Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 116

Chapter 116

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,196 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yi har dakinka nake iskancin". Ta nisa ta sake cewa "na tabbatar ita baka ta'ba dukanta ba, amma ni saboda rashin gata da 'kin da kake mini kanka tsaye kake duka na" Ta fa'da cikin kuka, maimakon hankalin Mk ya tashi sai ya ji wata irin nutsuwa ta zo masa domin kuwa ya gane da gaske 'Karfi ya ke da ya ce akwai soyayyarsa mai yawa a zuciyarta duk da bakinta na kirarin 'kinsa. Kishin Farida ke ya galgalata wannan kuwa ba yadda zata yi sai hakuri. Domin ya riga ya kudire ba zai ta'ba barin matsanancin son da yake yiwa Sa'a ya sa ya zalunci Farida ba, ba kuma zai yi kuskuren rabuwa da ita dan zai dawo da tsohuwar matarsa ba. Bashi da burin auren mata biyu, amma tunda kaddara ta zaba masa to kuwa zai yi iya kokarinsa bai bari soyayyar daya tasa ya danne daya ba. Cikin lallashi ya ce "sonki ne yake rufe mini ido shiyasa nake dukan ki, Amma ai kinsan iya bakinki nake duka dan shine mai dafi, amma ta yaya zan doki jikin ki alhalin shine abin hutawata. Na rantse miki banda tsoron ubangiji da a motar nan sai na shige, dan ki gane ba karamin kewar ki nake yi ba, har yau din nan 'kwarar Farida nake yi domin idan ina tarawa da ita bana samun nutsuwa, sai na ayyano ke ce a 'kasana amma kina fa'din wai ban miki komai ba sai zalinci". Kuka sosai Sa'adah ta fashe masa maimakon ta ji da'din kalamansa, ai sai ta ji tamkar cin fuskarta yake yi, yanzu ya murde mata baki Dan ta yi jam'u ta ce wasu samarin alhalin yasan shi ka'dai ta cirewa samartaka. Amma shi yana fa'da mata yana tarawa da wata kansa tsaye. A cikin kukan ta ce " in Sha Allah Babu sauran zama a tsakanin mu, zan yi dukkan kokarina naga ban jefa kaina a uku ba, a satin nan zan fitar da wadda zan aura, ba zan iya auren ka ba Mukhtar. Ka yiwa Allah ka rabu da ni bana sonka yanzu". Cikin rashin damuwa ya ce "Ban damu da ki so ni ba, domin son da nake miki ya isa ya ri'ke auren mu, idan kuma kin kafe ba zaki yarda mu yi auren ba, shikenan amma ki sani ban yi al'kawarin zan iya cigaba da jarumtar kawar da ido akan ki ba, kin sanni sarai! Billahillazi ki shirya yin jegon da babu sannu, domin kuwa ciki zan miki, ki haifarwa Innah, kafin a ankara zan sake dirka miki wani sai akaiwa Hajiyar Bichi". Gaban Sa'a ya buga da karfin gaske, mafarkin Innah ya Fa'do mata, amma sai ta waske ta daure fuska ta ce "saboda kana jin isa, ko dan ka raina gidanmu?" Ya make kafada ya ce " whatever". "Dan Allah Mukhtar ka bude min kofa zan fita na gaji da jin Wannan maganganun marasa azanci da kan gado". Ya yi dariya ya ce "inace dan kin san bana son kina gatsa sunana ne yasa kike ta fa'da, to idan kin so kina iya cewa Mukhtar Kabir Bichi. Zan amsa miki amma nan gaba ka'dan Billahillazi idan akace ki fa'da ba zaki iya ba, zan fa'da miki wallahi ba zan ta bin kanki akan ki dawo gareni ba. Kina so, Ina so to karmu wahalar da juna dan wallahi kika ce zaki ja ni a kasa, ba zan yarda ba, ki rabu da Alh Mamman ban son ganin ki da shi". Da guntun hawaye ta ce "sannu ubana, to shi nake so, domin kuwa kullum zai ta ganin yarinta ta ne, dama kuma ai tsofaffin sun fi dadiin harka. Sosai ransa ya baci, a fusace ya dinga kwankwasa gilashin har Mahmoud ya ankra ya iso ya ja motar har kofar gidan Suka kaita, Mahmoud Yana ta faman tsokanarta ya san ai anshirya sai maganar shan biki, duk yadda take jin nauyin 'Karfi yau haushin sa take ji dan haka har ta sauka kala bata ce masa ba. Da shigarta Sumayya ta dinga bin ba'asin kukan da take yi, bata boye mata ba, ta bata laabrin wula'kancin da Baffa ya janyo mata a wurin Mk na sawa ya kawota. Ran Sumayya ya baci sosai ta ce "ai sai dai ki dau dangana domin kuwa Baffah burinsa bai wuce ki komawa uban Jawad ba. Duk irin bacin ran da ya jefa mu, duk irin yadda ya jingine ki shekara da shekaru, yanzu kuma dan gata da rashin kishin naka, Dan ya dawo sai ka sake bashi aure?". Kwalla ta cika idon Sumayya tana ji a ranta Mk bai cancanci auren Iya ba, har ga Allah ta fi sonta da Anwar, amma ko ita ai ba karamin ba'kin cikin Mk ta hadiya ba. Amma sanin maganar mahaifin su gaba take da kowa, yasa ta hadiye maganganun a zuciyarta, sannan kuma tasan komin borin da Iyah zata yi ba wadda take so irin uban na Jawad. **** Sai bayan magariba ya isa gidansa, ya iske Farida cikin cotton din doguwar riga kirar Pakistan, kanta dauke da hular da ta dace da rigar, sai kamshi take yi, ta yi kyau sosai, amma saboda ba ita yake son gani a yanzu ba , sai yaji ba haka yake bu'katar ganin kirjinta ba, so yake ya kamo wadda zasu cika masa hannu kamar yadda dazu ya lalubo na Sa'a da nufin zai kamo bakinta. Ya zauna a kujera ta tashi ta kawo masa ruwa da lemon coke, da cake da ta yi a yammacin yau. Yana zaune ya rike kansa alamun yana cikin rashin sukuni. A hankali ta ce "halan baka jin da'di ne?" Dai-dai lokacin sai ya dinga jin muryar Sa'a na masa kuwwa tana fadin Alh Mamman take so, ai tsofaffi sun fi dadin harka. A fusace ya mike ya ce mata "A a asibiti ne a kaina ban son katsalandan wallahi". Sannan ya wuce ya haye sama. Jikin Farida ya yi mugun sanyi, ta zauna tana ambaton Allah. Ta jima tana nazarin me ya same shi, kaso mafi yawa tafi zaton Sa'adah ce ta zaunguro shi, kishi ya kamata sosai, domin ta lura duk sadda ta ganshi a burkice to ba shakka itace ta birkita mata miji. Haka ta yi ha'kuri ta kwashi abincin ta bishi da shi, abin mamaki kuma sai ya rungumeta yana fa'din ta kara hakuri da shi, Yana cikin wani irin al'amari ne da yake neman fin karfinsa Dan Allah ta kara hakuri, ta kuma yi masa uzziri. Matsananciyar sha'awar Sa'a da ya taho da ita tasa ya kasa fita sallar isha, domin akan Farida ya sauketa, sai da suka samu nutsuwa, suka yi wanka sannan suka yi jam'i tare. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 NA *SURAYYA DAHIRU*. •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ *_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai satar Dukiya._* _*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_ *Wannan shafin Tukuici ne ga* *Amina Mukhtar Nashe* *Bisa yaddda kike kaunar labarin, ki yi yadda so da shafin, Allah ya raya zuri'a* *SADAUKARWA GA*

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});