Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 71

Chapter 71

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

suke yi. Kullum mitar ya siya mata waya take, rannan da ya gaji, ya zaunar da ita yace "kinsan za ki dame ni mai yasa za ki sani karban filaye biyu? bani da kudin siya miki wayar da kike magana akanta, Ni kaina ban ri'ke ta ba". Ai kuwa zamansu ya dawo wani iri, saboda ta kudire a ranta da gaske yanmatan banzan yake yiwa hidima, ita ya barta ko oho, mussaman da ya ki yarda ya kaita ta ga filayen nasa. Ranar wata juma'ah sai ga shi da sabuwar plasma TV 32 inch, ga mamakinsa ba ta yi wani murna ba, lamarin da ya bata ransa sosai. Haka ya daure, ya kira mai gyara ya hada mata har da satellite. Kallonta kawai yake yi, a zatonsa siyan tv zaisa zamansu ya dawo normal, amma sai ya ga sabanin haka, saboda ta riga ta yi nisa a son Black berry, ta samu shedanun kawaye na mata famfo. Haka suke ta gungurawa, yau fari gobe tsumma, mussaman da ya tsaya akan ra'ayinsa na ba zai siyi waya ta makudan kudade ba. haka jarrabawar jamb ta fito, a lokacin da F.C.E. ta fidda jerin daliban da suka sami gurbin karatu har da ita, inda zata karanta primary care education jiran lokacin fara daukan darasi take yi nan da yan wattanni. Hakan bai sa ta sauko ba, saboda ita B.U.K. take so, Safina sai cewa take "mijinki is very smart Ya rantse ba zai kai ki makarantar da yake ba, dan kar agane yana da mata". Yau da gobe akace ta fi karfin wasa, ya gaji da zaman rashin walwalarsu, ya kukuta ya siyo musu Android shi da ita, a lokacin bata jima da fitowa ba, dan haka itama mai tsada ce, ga mamakinsa ko Na gode ta gagareta fa'da wadda ko kadan ba halayyar ta bace, ko abu bai yi mata ba zata yi godiya ko a gajarce ne. Amma wannan ajiyewa ta yi a inda ya bata ba tare da ta duba ba, ransa ya baci da ita, irin wadda bai taba ji ba. Ganin idan ya cigaba da zama kusa da ita, komai na iya faruwa a tsakaninsu na rashin jin dadi, yasa ya mike ya fita zuwa shagon sa, bai dawo ba, sai shadaya da ashirin da bakwai 11:27pm. Ya sake tarar da wani 'bacin rai fiye da na farko, wato rufe masa gida, bugu ka'dan ya yi, ya hakura dan kar makwabta su fahimci abin da ke faruwa, ya dinga kiran wayarta ba kakkautawa, tana shiga amma taki dauka, karshe ma sai ta kashe wayar gaba'daya. Haka ya kwana a gate a cikin mota, ya yi kwanan zafi, da sauro, barcin kansa rabi rabi ne, wannan daren yana cikin jerin dare masu tsayi da ya fuskanta a rayuwar sa. Duk juyin da zai yi, tunanin irin hukuncin da zai mata yake yi, ya gaji da wannan bala'in, zai nuna mata, neman zaman lafiya ba shine lasisin da zata dinga wulakanta shi ba. Koda asuba kin bude masa ta yi, dan iskanci kuma ta kunna wayar amma taki 'dagawa. Ya Mata text yafi sau goma, har kurarin zai fadawa Baffa ya yi, amma ko gezau. Har taran safiya, yana harabar gidan. Takaicin sa daya, ba ya ajiye kaya a mota. Mahmoud ya kira ya fada masa halin da yake ciki. Da kyar Mahmoud ya shawo kanta ta bude masa, domin kuwa cewa ta yi, ya koma ya dauwama a gurin Farida. Yana jin lokacin da ta zare sakata, amma ba'kin ciki ya hana shi tashi, ya jima yana addu'ar samun sau'kin zuciya kafin ya samu sassauci. ya shiga gidan kai tsaye dakinsa ya shiga, ya yi wanka, ya fito ya shiga kicin, ya hadawa kansa Abu mai sauki, ya koma dakinsa ya rufe, yini guda bai fita ba, domin ramuwar barcin da bai samu ya yi ba. Itakuma tana zaune cikin shirin ko ta kwana, har sun yi waya da Halima ta fada mata abin da ta yi masa jiya, tace mata da kyau, gobe idan ya sake har gate din za ki rufe. Sai azahar ya tashi, ya fito da shirin fita masallaci, Jawad ya biyo shi, ya ri'ke hannun sa, suka tafi bayan ya masa alwala, suna dawowa, Jawad ya dinga Jan hannunsa, Yana cewa" Mami falo". Ya daka masa tsawa ya shige dakinsa ya daga murya yace "je ka wurinta kai, domin ita da babu duk daya ne a gurina" Jawad ya fashe da kuka saboda tsawar da bai saba da ita ba. Abin ya yiwa Sa'adah ciwo, a fili tace "Allah yasa yau ka sake yin dare, zaka san Ni da babu daya muke". Tsawon kwanaki biyu, zaman nasu ya sake yin tsami, domin shima fishi ya dauka sosai, ya dauke sabuwar wayar da ta bar masa a gurin, sannan ya karbe wadda take amfani da ita. Lamarin da yasa rikicin ya sake ta'azzara a tsakanin su. Ta dayan bangaren kuma sai shirin tafiya Abuja yake yi, saboda za su yi wata jarrabawar scholarship da gwamnatin tarayya zata tura malaman jami'oi karo ilimi a kasashen Birtaniya, Canada da kuma Rasha. Bai fada mata zai yi tafiya ba, har sai da ya kammala shirinsa, da zai tafi, ya tsaya daga bakin kofar falon yace " Zan yi tafiya, sai Allah ya dawo da Ni, ya bawa Jawad dubu uku yace "kai mata". Mamaki yasa ta kasa bude baki ta yi magana, ya juya ya tafi, Jawad na kukan zai bishi. A tunanin ta kwana daya zai yi ko biyu, amma sai da ya shafe kwanaki biyar ba shi ba alamun sa, a kwana na shida ne, idonta ya fara raina fata, mussaman da ta tabbatar da Mahmoud suka yi tafiyar, Amma shi ya dawo kwana biyu kawai ya yi. Kuka ta dinga yi, tamkar shine mafita, ga rashin waya dake addabar ta, ga rashin sa. Sai da yayi sati guda ya dawo, kallo daya ya mata yasan ta ji jiki, sakonsa ya daketa sosai, amma saboda Halinta na taurin rai, ko kallo bai isheta ba. Washagari da ya fita, sai da ya kai 11pm kafin ya dawo, domin ya jarrabata ya gani. A bangaren ta tana son rufe masa gida amma ta kasa, kwanakin da ya yi baya gida, sune mafi tsauri a dukkan rayuwar ta, tunda suka yi aure bai ta'ba yin tafiyar da ya kwana ba tare da ita ba. tasan rufe masa gidan da ta yi ne, yasa yayi tafiya mai tsayi ba tare da ita ba, ba magana mai dadi, ko na zai yi missing dinta. Ya dawo ya tarar da gida a bude, ya yi murmushi, yauma 'dakinsa ya zarce, wannan abin ya dameta, amma bata ji zata bashi ha'kuri ba, tunda ai ita ya zalunta. Washagari yana shirin fita, ta fito ta tsaya a tsakar gida, sai da ya fito sannan tace " Ina son zanje gida". Ba tare da ya kalleta ba, yace " Ba za ki je ba". Ya sa kai zai fita, taja tsakin da yasa shi juyowa da sauri, kafin yayi magana tace "dama idan mutum na cin amanar matarsa, sai ya yi ta boyeta a cikin gida, mai za'a yi da auren likitan mata, da mai koyarwa a Jami'a, aiki ne na yan iskan maza,

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});