Chapter 131
Chapter 131
ta binta tunda mu muke nema, sannu a hankali har mu samu mu damketa". Mk ya nisa, ya ce" tunda na rabu da yarinyar nan wani abu mai tsananin nauyi ya tokare ni a kirji da makoshi, har yau din nan bai fada min ba, sai kara girmama da abin ya yi a yanzu da nake ganinta da wasu, wai ya zanyi ne? Wallahi na fara debe kauna da rayuwa domin Ni ka'dai nasan azabar da nake hadiya mussaman ace dare ya yi lokacin da zan samu na huta, a lokacin ne nafi shiga tasku bana iya barci, yanzu kuma abincin ma baya shiga". 'Karfi ya nisa ya ce "ka daina damuwa komai zai wuce, idan ka ga ka rasata, to kawai ka dauka babu alheri ne a kasancewar ku, ubangiji ne ya karar da zaman. Sai ka duba ai ka rayu shekaru bakwai babu ita, kuma baka mutu ba, idan har ita zata iya yin jarumtar hakuri da kai gaba'daya, bayan ta sha dukkan ba'kin ciki da tashin hankalin son komowa gareka, to kuwa kaine ka fi cancanta da irin wannan jarumtar". Mk ya yi shiru yana gasggata Sa'a ta fi shi jarumta, tunda har zuciyarta bata buga adalilin aurensa ba, don kuwa shi yanzu ya gama yin imanin duk ranar da aka daura aurenta da waninsa tabbas a ranar ajalinsa zai sauka adalilin bugawar zuciya, ko hawan jinin da ya zarce kima. A raunane ya kalli 'Karfi ya ce "Ai ita mace ce, ubangiji ya sanya musu wani irin karfin jure dukkan kalubalen tarbiya da kishi, amma mu ba a bamu wannan ba, namiji karfin gwagwarmaya aka bashi, da karfin tsayawa iyalinsa akan dukkan bu'katun yau da kullum". 'Karfi ya nisa ya ce "Hakane! Abin da nake so yanzu da kai shine, ka dora jarumtar gwagwarmaya a zuciyar ka, tunda ka gamsu muna da karfi da juriya anan bangaren, to idan kuwa hakane, zamu yi gwagwarmaya har mu samu mu kwato abin da yake namu ne". Tun daga ranar suka fara yiwa Iyah wani irin naci, mai cin rai. A Rana su kanje sau uku, kowanne lokaci zuwa suke yi, tun Inna tana ganin zasu gaji su daina, har ta fara ganin ba zasu gaji ba, domin kuwa kullum zaryar kara gaba take yi, ba baya ba. Haka gidan Sumayya, hatta Idris a yanzu tausayin Mk yake ji, shiyasa ya fa'dawa mai gadin gidan matu'kar Mk ne suka zo, to ya bude masa gate kai tsaye. Tsawon sati uku ana wannan zaryar bai fi kuma sau biyar suka samu nasarar ganinta ba, a cikin zuwa fiye da arbain. Duk inda hankalin Mk yake a tashe yake, yayin da Mahmoud yake ta karfafa masa guiwa duk da shima bai yi zaton kafiyar Sa'adah ta kai haka ba. Ranar alhamis da hantsi suka isa gidan Sumayya, sun shafe lokaci mai yawa a zaune, sannan ta fito, sanye da hijabi fuskar nan a daure, ta iso, da alamu tilas aka yi mata. Dr Karfi ya mike ya na fa'din barka da fitowa sarauniyar mata. Ta yi shiru tamkar ba da ita yake ba, domin ta lura shine jagoran wannan nacin da suke mata kamar ba'kaken mayu. Ya ce "Allah ya huci zuciyar giwa kuma gimbiyar Mata, ba zamu gaji da bada hakuri ba, ba kuma zamu gajiya ba, har sai kin dawo mana da walwalar da ta yi mana tutsu. Ki yi ha'kuri, ki zo ki haska mana zuciyar aminina da gidansa gaba'daya, Ina rokon ki, badan mu ba, sai dan ubangijin ki, ni shaida ne na irin tsananin son da yake Miki". A tunzure Sa'a ta ce "ka dinga jin tsoron ubangiji Baban Dady! Sai yanzu! Sai yanzu! Sai yanzu zaka tirsasa ni, me yasa a wanccan lokacin baka tirsasa shi ba, me yasa ka bari na wulakanta, na tabbatar ba zaka so ayiwa kanwarka abin da aka yi mini ba. Amma yanzu da yake farin-cikin abokinka kawai ne a gabanka, ka na'de 'kafar wandon yi mini dole, kasan ina jin nauyinka, akan me zaka takura ni irin haka, an ta'ba yin aure dole, to ko Baffah ma na tabbatar masa bana son wannan mutumin, kaima na fa'da maka, ka sakar mini mara, na ro'ke ka". Ta karasa cikin kuka sosai, Dukkan su sun yi laushi, mussaman Mk da yake jin tamkar ya hadiyi zuciya saboda yadda yake jin ciwon yadda take fadin bata sonsa, a gaban kowa. Mahmoud ya kalli Agogon hannun sa, ya ce "hakuri zaki yi, ba yadda zamu yi ne, ki 'kara hakuri, ubangiji zai baki ladan masu hakuri. Ya kalli Mk ya ce " ina da appointment nan da mintina talatin a makaranta, zan wuce, idan ka gama kawai mu hadu a gidanka bayan azahar". Daga haka ya fice da sauri, da mukallin motar Mk a hannunsa. Tana tsaye tamkar soja. A hankali Mk ya ce "zauna mana Dan Allah". Bata yi musu ba, ta zauna. Ya zuba mata ido yana kallon yadda ta ke cika tana batsewa ya saki ajiyar zuciya mai zafi ya ce "A gaban kowa kike fadin ba kya sona, Ni kike wulakantawa haka? Kada kishi yasa ki manta ke ce kika mini laifi?" Da kuka ta ce "Ni na maka laifi tabbas, ka kuma hukutan ni, to menene kuma ba sai a barshi a hakan ba, gaskiya kun matsa mini, tsakani da Allah kun shiga rayuwata, sau nawa zan fa'da maka bana sha'awar sake rayuwa da Kai? Na ha'kura, na bar mata, Ni ma ka bar ni, Dan Allah". Kafin ya yi magana ta sake cewa "kafin ka aure Ni ka kira ni Ballagaza, na yi hakuri saboda ina ta'kama da Budurci, yanzu kuma ka ce ina ha'intarka, fa'da mini dame zan kare kaina, tunda ba ni da Budurci a yanzu?" Da sauri Mk ya karaso kujerar da take zaune, ya zauna a hannun kujerar ya sassauta ya ce " Na da'de ina fada miki, bacin rai ne, ba ina nufin haka har zuciyata ba, ki yi hakuri. Na janye kalamina, wallahi tallahi ke din katangaggiya ce, ki bar wannan maganar, ko tunawa bana so, hankali na tashi yake yi. Na janye! Na janye! Na janye Dan Allah a rufe wannan maganar har abada". Ta dinga kuka sosai mai cin rai, ta kasa cewa komai. Ya nisa ya ce" kukan ya isa haka, ki yi hakuri ina fatan wannan ne kukan ki na karshe akan wannan matsalar". Ta kifa kanta a dayan hannun kujerar tana sake tsananta kukan sosai, Ta ce "indai baka rabu da ni ba, na tabbatar zan dauwama ina kuka ne, domin zan rayu ina raba ka da wata ne, Ni kuwa da haka gara na auri me mata uku na zama ta hudu". Mk ya rasa mai zai yi, ko ya ce, gaba'daya tunaninsa gaba'daya ya kulle. Ya tabbatar auren Farida ne cikas dinsa a gurinta, shine yasa ta kasa amincewa da shi. Ba yadda zai yi akan Farida kuwa domin bai aureta dan ya saketa akan wani 'karamin dalili ba. Ya sassauta ya ce "Yarda da 'kaddara na cikin sharuddan cikar imani, ki ture komai, ki kalle ni har yanzu ba abin da ya canja na soyayyar ki a tare ni, ki bani amanar kan ki wallahi ba zaki yi nadama ba". "Ko yanzu kika
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157