Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 103

Chapter 103

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kika saba". Yana rufe baki ta ce "Ni Iyah Basiru Ado Gogel idan ka mayar da ni ban yafe maka ba, ko da gwal aka yi ka na barka, ai da tun farko nasan kallon fasi'ka kake mini, da ka yi tsararo na bika, wallahi Mukhtar ko zaman mota bana fatan ya sake hadamu balle zaman aure! Idan har ni diyar Malam Basiru da Malama Salamatu ce na barka. Koda kai ne autan maza, idan kuma ban aikiata abin da ka jefe ni da shi ba, to na yafe maka, idan kuma na aikata ubangiji ya bayyana ni, na kunyata na kuma tozarta a idon duniya". Ta juya ta tafi sai da taje ba'kin kofar barin falon ta juyo, suka hada ido tunda kallonta kawai yake yi, ta ce "ka manta ka sanni domin kuwa daga yau nima na rufe shafinka, sannan hidimar da kake yi da ni ta makaranta ka dakatar bana so, ban bu'katar komai daga gareka, idan kuma har na ji alert din kudi zan mayar wa da Mahmoud, turowar kuma na nufin in sha Allah baza ka rabu da Hajiya lafiya ba". Ta juya da saurin gaske ta fita, ta bar shi a tsaye cikin mugun mamakin kalaman da ta jefa masa, mafi tayar da hankalin a ciki shine alakanta Jawad da datti, ko makaho ya shafa ya san Jawad jininsa ne, domin komai na jikin Jawad nasa ne, hatta tawadar Allah da Mk yake da ita akan lebansa Jawad na da ita. Bugu da kari da ta masa fatan mugun alkaba'i na rashin gamawa da duniya lafiya, to ai mahaifiyar ka itace duniyar ka. Da kyar ya ja kafarsa ya isa kan kujera ya fadi yaraf yana jin tamkar kansa ba a jikinsa yake ba tsabar nauyin da ya masa. Zuciyarsa ta kuntata sosai, gumi ya dinga karyo masa, fargabar auren da zai yi gobe ta sake nunkuwa, fishin da ya gani a tare da Sa'adah ya sake kassara shi, Anya haka kawai Sa'a ta bar shi kuwa, wanne irin so yake mata haka? Ya dinga tambayar kansa, a cikin wannan yanayin 'Karfi ya dawo ya tarar da shi. Cike da tausayawa ya ce "Bichi ka dawo da Sa'a itace matsalar ka, Ina jin fargaba kar hawan jininka ya sababa maka ciwon zuciya". A shake sosai Mk ya ce "Dan Allah 'Karfi ya zanyi ne, ban son auren nan da zan yi, ka taimake ni ka 'boye Ni". Ido kawai 'KARRFI ya zuba masa amma zuciyarsa sai harbawa take fiye da 'kima saboda yadda maganar Mk take nuni da rashin nutsuwar da mai yin ta yake ciki. Amma ya san ganin Sa'adatu ne ya gigitashi haka, da kansa Mahmoud ya dinga jinjinawa kansa, ya tabbatar Mk na mutuwar son Sa'a amma ya tabbatar bai fi shi sonta ba, kawai girman aminci ke hakurkurtar da shi, sau tari zuciyarsa da tunaninsa na fa'da masa ba haramun bane, ya gwada Sa'arsa kawai, amma da ya tuna girman Mk da tarin sadaukarwar da ya masa a baya, sai ya ji a ransa ana barin halak dan kunya! A fili Mahmoud ya ce " Ashe dai ni jarumi ne na gaske, Allah ka samu a cikin masu yin soyayya da abota saboda Kai". Mk da yake fama da zafin da Sa'a ta hada masa, bai fahimci 'Karfi ba bare ya nemi fashin ba'ki kan kalamansa. Hannuwan Mk ya ru'ko ya ce "ka yi hakuri nasan yadda kake ji, auren Nan na cikin kaddarar ka, ka karbe shi da zuciya daya, ubangiji zai buda maka kirjinka in sha Allah! Fatana dai ka dawo da Ummu Jawad, ka sau'ka'ka muku wannan dambarwar tura ta fara kaiwa bango, bana son a kai matakin da zata janye nadamarta tunda ka ki bata damar da zata gyara kuskuren ta, wallahi yarinyar nan ta gane kurenta, komin sharrin zuciya da mahassadi ansan dai ta nutsu ta fahimci rayuwa yanzu". Ido jawur Mk ya ce "mumunar karyace baka ga Tijarar da ta mini ba yanzu, sosai ta wulakanta ni tare da yi mini mugun fata, ashe so yana zama tsiya?" Mahmoud ya fahimci Mk yana cikin tension sosai sai ya kyale shi, ya rasa gane wannan masifar ta Mk, Yana son abu yana cutar kansa, yana cutar Yar mutane, haushin yadda Mk yake wulakanta Iyah yana neman samun muhalli a zuciyarsa. **** Ikon Allah kawai ya kaita gida lafiya, domin daga gidan Mahmoud ba tasan ya aka yi ta isa titi ba. Haka nan tunda ta hau abin hawa, bata sake sanin inda take ba, sai da Mai adaidaita ya ce "Malama mun iso fa, ta daga kai ta ganta jikin shagon da suke kwatance da shi, a sukwane ta fice yana ta Kiran ta tsaya ta karbi canjinta amma ina, ba ta tsaya din ba, ta dai samu sukunin daga masa hannu alamun ta bar masa. Tamkar an jefota haka Inna ta ganta ta fa'do, ta shige dakinta ta kwanta ta dinga gunjin kuka mai dafa zuciyar Dan Adam, kuka take yi na kaicon yadda rayuwa bata zuwa mata a yadda ta zace ta, kuka take yi akan kalaman Mk da suke nuni karara kallon mai cin amanar aure yake mata, wanne irin zalunci ne wannan? A hanzarce Inna ta bita dakin ya zauna kusa da ita, ta dauki kanta ta dora a cinyarta, a tausashe ta ce "Iyah ki daina bibiyar Muutar, ba zai mayar da ke ba, ki fita harkar sa idan ba kina son ni na fita a harkar ki bane, ki fuskanci rayuwar ki, ki bawa wasu dama kafin ya dawo kasar kema ki yi aurenki". Kuka kawai Sa'a ta ke yi na fitar hankali har da shidewa, sosai hankalin Inna ya tashi mussaman da taga yadda lebunan bakin yarta suka kubura tabbacin an musu dukan zalunci. Kwalla ta cika idonta ta ce Muutar ne ya dake ki haka? Me kika mayar da kanki ne Iyah? To saurare ni da kyau, kinsan daukan kafafuwan da kike yi kina binsa ba komai bane face Ballagazanci, duk shashancin namiji kuwa bai son Ballagazar mace! Wallahi ba zai saurare ki a cikin wannan halin ba, ki fita a harkar sa, ki manta da shi, ki tattara shi ki watsar, ba shi kadai bane namijin kirki ba, Ina tabbatar miki Sa'adatu akwai wadda suke son ki kwatankwacin son da Muutar ya miki, ki kwantar da hankalin ki, zaki Sha mamaki". Idonta dauke da hawaye ta kalli Inna da mamakin jin ta ambaci zahirin sunanta, Bata taba jin ta fa'di hakan ba, saboda riko da al'adar ba a fadar sunan uwar miji. "So nake na manta shi Inna, amma na kasa! fada min me zanyi na huta da azabar da nake ji ta rashin sa" Ta fa'da cikin rushewa da kuka sosai. "Ki ji a ranki yanzu ba kece a gabansa ba, da yana sonki, da ya hadaku ku biyu ya aura, hakan ma wani nau'i ne na ladabtarwa tunda komai nasa zai raba muku biyu ne maimakon da, da bashi da komai a gabansa sai ke da 'dan ki, na sani ke kika jawowa kanki komai ya miki, amma ai ya ladabtar da ke, sannan kin yi nadama kin sauke girman Kai kin bada ha'kuri, ya kamata ya yi ha'kuri shekaru hudu yana jan ki

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});