Chapter 101
Chapter 101
Sa'adah bata san mai yake going ba, sai ta fasa fa'da dan kuwa be kamata ace a bakinta aminiyarta zata ji wannan ba'kin labarin ba. Tasan da tana da waya da ta ji. Baffah da kansa ya fa'da wa Innah da Iyah auren Mk, ba Sa'a kawai ba hatta Inna kuka ta fashe da shi mussaman da ya tabbatar musu ya siyar da fili daya cikin filayen Sa'a ya biyawa Mk sadakin auren. Sosai suka tayar masa da hankalin sa domin irin kukan da suke tamkar ance Sumayya ta yi mutuwar fuju'a ne. Har cikin ran Inna take jin wani irin azabben kishi na ratsa ta, bata san kishi ba sai a ranar tunda ta wanzu ita kadai ne a wurin mijinta A kuma ranar ta fara jin tsanar Mk irin wadda bata yi zaton zata yi masa ba. Kuka na fitar hankali Sa'adah take yi 'karshe ta dinga kelaya amai ta hanci da baka. Hankalin Inna da Baffah ya yi tashin gauron zabi. Ranar Inna a wurin Sa'adah ta kwana karon farko da ta bar mijinta shi ka'dai alhalin suna gida 'daya. Sosai Inna ta ke jin takaicin Baffah a ranta, idan ba zai yi kishin 'yarsa ba, menene zai siyar mata da kadararta ya bawa tsohon mijinta kudin dan yayi aure, babbar damuwar ba wai Rashi ne yasa akayi hakan ba, kawai dan ya nunawa duniya har da shi a cikin masu musgunawa farin-cikin Iyah. Washagari da rashin kuzari ainun Iyah ta tashi, babban damuwarta ta ga Mk, ganin Inna ta shiga wanka yasa ta dauko wayarta ta 'kira layinsa, tana ta wasi-wasi ko an rufe layin?. Ai kuwa bugu 'daya ya shiga, da sauri ya 'daga zuciyar sa tana bugawa. "Malam ina son ganinka, ya za'a yi?" Yadda ya ji muryar ta, da yadda ta yi maganar ya san zancen aurensa ya sameta. "Ki saurare ni zan zo nan da awa guda". "Ni dai mu ha'du gidan 'KARFI". "Ok yanzu haka Ina gidan sai kin iso, ina jiran ki". Yana ajiye wayar Mahmoud na fitowa daga kicin 'dauke da ruwan roba da tumblers guda biyu, ya dire wa Mk yana ta faman cin magani, ko abincin da suka gama ci, haka suka ci tamkar kurame adalilin fishin da Mahmoud yake yi da auren da Mk zai yi nan da kwanaki biyu. Mk ya kalli Mahmod ya ce "Karfi ka daina wannan tunbatsar! kwanaki 'kalilan suka rage mini, na bar maka 'kasar ka huta da ganina". Da rauni ya yi maganar hakan yasa Mahmoud sassautawa ya ce "Mk tunda ka amince zaka auri yarinyar nan, to ka hada su da Sa'adah, wallahi kai take jira, ko mai ta yi maka ai ka hukunta ta, shekaru hudu ba wata hudu bane, ba kuma sati hudu bane, Ni kaina na taya ka jin kunyar Baffah, wallahi tallahi karfin hali kawai yake yi akan lamarin ku, shi ya haifi Sa'adah, alkunyar da yake yi fa ta kai geji". Kallo 'daya zaka yi wa Mk ka gane kalamin Mahmod sun sanyaya masa jiki kwarai da gaske, amma baya jin zai iya yin wannan al'amarin, ya kalle shi ya ce. "Mahmoud na 'dade da gane ban da kirki, Ni da kaina zaluntar kaina nake yi, saboda wallahi har ya zuwa yau ban huta da kewarta ba, ban daina jin cewar na tafka asarar rashinta ba, ina son na rayu da ita, amma tsoron ta nake ji, ko ayyanawa na yi a zuciyata ya kamata na bata wata damar, sai na shiga ru'du da tashin hankali". Ya yi shiru yana sakin ajiyar zuciya! Ya 'dora da cewa "wata'kila wannan na cikin 'kaddarata, na rayu a duniya ba da wadda nake so ba, alhalin tana raye". Mahmoud ya rasa abin cewa, tausayin Sa'a yake ji, amma yanzu har Mukhtar 'din tausayi ya bashi, ya tabbatar a matu'kar takure yake da 'kadddarar da ta fado masa na auren Farida ba'katatan Suna cikin haka! Yayan Mahmoud ya kira shi a waya, da sauri ya mi'ke yana cewa " yau tawa ta same ni wurin Auwal, sai da ya yi ta gargadi kar na bar shi yana jirah na. Mukallin mota ya 'dauka da sauri akan center table din da ke tsakiyar falon. Ya kalli Mk da ke kishingide bai da niyyar tashi, ya ce "ko na je na dawo?" Kai kawai Mk ya iya 'dagawa a dalilin mutuwar jiki, saboda yadda al'amarin Sa'adah ke damunsa. A hanzarce Mahmoud ya fita ya na fadin "saboda gidan ba kowa yasa ka yarda ka zauna". Da yake matar Mahmoud din sunje Kaduna bikin cousin sister dinta sai jibi zasu dawo. Mahmoud na fita 'kofar gidan inda ya ajiye motarsa, bai shiga da ita cikin gidan ba, saboda yasan ba wani jimawa zasu yi ba, kawai sai ganin Sa'adatu ya yi tana bawa mai adaidaitanm sahun da ya kawota, ku'dinsa. Da sauri ya karasa kusa da ita yana mata barka da zuwa, yana jin wani irin yanayin da ya ganta a ciki, alamun rashin lafiya da rasnin kwanciyar hankali baro baro a jikinta. Ba dan 'karfin dangantakar sa da Mk ba, da ya aure yarinyar nan ko ya huta da motsawar da zuciyarsa ke yi a duk sadda zai ganta, kai so masifa ne, Madallah da mutanan da suke sadaukar da soyayyar su dan halacci, aminci, ko masalaha. Suka gaisa, ta tambayi iyalinsa, Har zaice matarsa bata gidan, sai kuma ya yi shiru, ya ce "ki shiga, zan je na dawo". Ya dinga addua da fatan sulhu a tsakaninta da Mk. Tana shiga, kai-tsaye bangaren matar gidan ta dosa, ta dinga knocking, jim ka'dan Mk ya leko daga bangaren maigidan yana cewa "iso nan, bata nan matar gidan". Ta shiga falon da sallama, ta gaishe shi, sai kuma ta kasa magana, sun Jima a zaune suna ta sake-sake a zuci. Mk ne ya katse shirun ta hanyar fa'din "ina jin ki, kin ce zamu yi magana". "Malam da gaske ne wai aure zaka yi?" Zuciyarsa ta buga, mamaki ya kama shi na yadda ya ji fargaba ta kama shi, saboda yadda ta yi tambayar muryarta na rawa. Ya kasa koda motsi, hakan ya tabbatar mata da gaske auren zai yi". Hawaye ya balle mata, ta ce " Na shirya fa'da maka gaskiya". Ya ce "Ina sauraron ki, waya baki kayayyaki nan?" Cikin kuka mai yawa ta ce Khalil ne! ya bani agogo da rigunan Jawad tsarabar Egypt, shine ita kuma Halima ta ce da ya bar agogon ya siya mini waya! sai kuma ya hado har da wayar". Ransa ya matu'kar baci tamkar yanzu abin ya faru, ya fesar da iskar bacin rai, ya ce "Ta hannun wa sa'kon ya same ki?" Da kukan ta ce "wallahi Safina da Halima ne suka kawo mini! wannan itace gaskiyar magana ban munafunce ka ba". Idonsa ya ka'da ya yi jawur dan tsananin kishi, ya ce "Munafunci kuma na nawa Sa'a! Ni dai kafin ki yi hakan wallahi ban ta'ba tunanin zaki mini wannan Munafuncin da aurena akan ki ba". Kukan Sa'adah ya 'karu ta ce "Tsautsayi ne, ban ta'ba yin haka ba, wallahi a lokacin da kayan suka zo sai da na ce tsoron kar gani nake yi ba zan karba ba". Ransa ya sake ri'banya baci a tunzure ya ce "Amma da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157