Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 63

Chapter 63

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

na yafe miki, amma ki dinga sanin abin da za ki dinga fada mini". Da azama ta ce "In sha Allah, sannan don Allah ka hakura da kai Jawad Lagos, idan Allah ya kai mu na haihu sai ka kai shi, sannan ya kara girma". "Wannan ne kuma ba zai yiwu ba, ba kula shi, kike yi ba, idan na fita kullum hankalina, ba a kwance yake ba, Allah-Allah nake na dawo na kula da shi, kin ga aikina yana bu'katar nutsuwata, don haka ki yi hakuri, idan ya isa shiga makaranta zan dauko shi, idan kuma ta nuna sha'awar ci gaba da rike shi, to zan bar mata". Ta sake ri'ke hannun sa sosai, tana fadin, "Wallahi zan kula da shi fiye da yana jariri". "Na ji zan bar shi amma bisa sharadi". Da sauri ta ce, "Ina jin ka ko mene ne zan yi" Ya kalle ta ya ga ta matsu ta ji sharadin. Ya nisa ya ce "Ba za a yaye shi ba har sai na ce". Da sauri ta ce, "Na yarda, har sai na haihu ma". "Ni ba ruwana da haihuwa, ko kin haihu idan da yiyuwar ya ci gaba da sha, za ki dinga shayar da shi, idan lokacin sa ya yi, sai a cire shi! Idan kin amince da haka shike nan, idan bai miki ba, tabbas gobe zai bar gidan nan". Kai tsaye ta ce "shike nan na amince". Ya janyo ta, ya kwantar da ita a saman kirjinsa, yana shafa bayanta, yana fadin, "Allah Ya miki albarka Ya sauke ki lafiya." Yana ta ba ta misalai masu dadi, ba akanta aka fara irin wannan ba, sannan matan so ne su ke yin kwane.🤣 Rawahul Mk. ```Alkalamin *Surayya Dahiru* ✍🏼 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._* *A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*. *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 61-62. Washegari da karsashi Sa'adah ta tashi, kafin karfe bakwai na safe, ta kammala soya dankalin turawa da sauce, gefe kuma ta dama kunun gyada da ake yi da danyar shinkafa. Sai da ta share falon, sannan ta kai kayan abincin bayan ta shimfida ledar cin abinci. Tana cikin share tsakar gidan ya fito yana sabe da Jawad, ya kalle ta, ya ce, "sannu da aiki." Ba tare da ta dago ba ta amsa da, "yauwa!" Yana tsaye yana kallon ta har ta gama shararta ta kwashe, ta wanke hannuwanta, sannan suka rankaya zuwa falon, shi ya zuba musu, suka karya, Jawad na kwance yana ta shure-shure da furzar da yawu tabbacin yana cikin yanayin masu yin hakori. Suna kammalawa, ya shiga wanka, ya fito a shirye cikin shudin (blue) jeans da fararar shirt, mai yarfin blue, sai tashin kamshinsa yake yi. Har cikin dakinta ya bi ta ya tarar wanka ta yi wa Jawad, tun kafin a gama shirya shi ya yi barci. Cike da farinciki ya mikar da ita tsaye, ya ja ta jikinsa, ya rungume, ya rasa kalmar da zai fada mata, kowacce kalma sai ya ga ta yi kadan ta wakilci yadda yake jin ta a rayuwarsa, a karshe dai cewa ya yi "I really love you Sa'adah. Stay blessed!" Ya sake ta ya juya ya tafi ba tare da ya sake cewa komai ba. Ta dade a tsaye, cikin sanyi jiki, kalaman ba karamin tasiri suka yi a zuciyarta ba, da kyar ta tattara kayan Jawad ta mayar da komai inda yake, ita ma ta yo nata wankan ta shirya, ta kwanta kusa da Jawad, suka sha barci, don sai kusan sha biyun rana suka farka, ta fara kokarin hada abincin rana. Haka rayuwarsu ta ci gaba da gudana, ranar da tashi da karfin jiki, za ta yi komai, ranar da kuma jikin ba dadi zai yi abin da zai iya, kullum cikin tattalin ta yake, ba ya kaunar abin da zai tunzura ta, mai ha'kuri ne, amma a wannan yanayin da gimbiyar take ciki, ya sake ninka hakurinsa akan lamarinta kwarai da gaske yake tausayin ta. Har cikin ya shiga wata shida ba wanda ya sani, saboda kwatakwata ta ki fita, duk son ta da ta fita unguwa musamman gidansu, ko gidan su MK, amma yanzu juyin duniya ya yi da ita, fur ta ki zuwa, sai dai ta gaishe su ta waya. Tun Inna ba ta damuwa da rashin zuwanta har ta fara damuwa, idan lissafin ta daidai ne tunda ta koma gidanta sau daya ta je musu, sannan aka yi wattanni shida da zuwan. Ranar nan suna waya ta ce, "Iyah wato yanzu Jawad da mijinki sun debe miki kewata ko?" Da sauri ta ce, "Haba dai Inna! Kullum fa idan ban ji muryarki ba, kin san ba na jin dadi, har yaushe na same su! da za su dauke mini hankali?" "To ai gani na yi muna gari daya, amma ki iya shafe rabin shekara ba ki zo kin gan mu, mun gan ki ba. Mijin ki duk bayan sati biyu zai zo ya gaishe mu, abin mamaki har ki iya ba shi Jawad ya kawo mana, amma ke shiru! Anya za ki yi imani kuwa?" Jin haka ya sa Sa'adah ta fashe da kuka, tana fadin, "Ban da lafiya fa Inna duk zuwan da Uncle din yake yi bai taba fada muku ba?" A gaggauce ta ce "Me yake damun ki?" Kuka kawai take yi, da kyar ta ce "Ni dai idan na mutu ki yafe mini, ba da gangan na ki zuwa ba". Sai ta katse wayar tana goge hawayen, a fili ta ce, "Na san gobe zan gan ki kin zo, kin ga abin da nake boyewa." Hakan kuwa! Inna kwana ta yi tana zullumin wane ciwo ne ya addabi Iyah haka? Karfe goma na safe ta isa gidan don ma Baffa ne ya hana ta fitowar sassafe, da tuni ta dade da zuwa. Mamakin cikin da ta gani jikin Iyah ya zarta wanda ta yi a lokacin cikin Jawad, ta rasa mai za ta ce musamman da ta ga ya yi kwari, har yana shirin fitowa duniya. Ganin irin kallon mamakin da Innar ta bi ta da shi, yasa ta kifa kai a hannun kujera ta fara sana'ar kuka. Da tausayawa Inna tace, "Ni kin san akan koke-koken nan naki, muke batawa, mene ne kuma na kukan? Mene ne yake damun ki?" Sanin bata da matsalar komai sai na cikin nan da ya mata shigar sauri yasa ta kasa cewa uffan. "Idan na fahimce ki, halin da kike ciki yasa kika mayar da kanki mujiya a cikin jama'a, ke baki san baiwa ce Uabngiji ya miki ba, ai ba kowacce mace ke samun damar samun irin wannan haihuwar ba". Ta ja numfashi ta ci gaba da cewa "jiyan nan aka mana tarihin Nana Fadima a Islamiyyar da na shiga, ashe Sayyadi Hassan da Sayyadi Husain ba tagwaye ba ne? Duk zatona 'yan biyu ne, ashe daban-daban aka haife su amma Malamai sun yi ittikafin

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});