Chapter 157
Chapter 157
ya ajiye shi, ya dinga kuka yana cewa "Malam dauke ni" Ba zai yi shiru ba sai ya dauke shi, ko ya mayar da shi wurin uwarsa. A lokacin Sa'a ta yaye Jadid ta haifi mai sunan Mahmoud, da suke 'Kira da Junior, ta Kuma je asibiti ta sanya loop da amincewar Mk, tana addu'ar ta yi auta kenan, duk da tana tsananin son Baby girl, mussaman da ta lura Mk ma ya matsu ta haifi yar budurwa, amma itakam ta gaji ta fahimci ita da Sumayya basu da rabon haihuwar girls har gara ma Sumayya ta samu Khairat itama kuma sai a karshe domin itace ta biyar kuma autarta. A lokacin Ubangiji ya sua'kar da ayarsa Farida ta samu juna biyu, murnar da mk ya yi ba yar kadan bace, sosai yake tattalin ta har Ubangiji ya sa ta haihu lafiya duk da dai c.s aka yi mata, yarinyarta mace mai kama da su Jawad kwabo da kwabo mai tsananin gashi irin nata. Bidirin da akayi ba kadan bane, tun akan Amir farida ta gane jama'a na sonta na tausayinta, haka a wannan ma aka sake nuna mata kauna. Sosai Mk yake ji da yarinyar nan. Aka sanya mata sunan Hajiya Babba! Wato Aisha, Farida ta sanya mata Amira. Mafi yawa Mk ya fi yawo da Amir da Amira tun Sa'a na jin wani iri har ta hakura ta gane ba dan komai bane illah ya samu Amir ne bayan ya dauki lokaci babu haihuwa, ita kuma Amira only girl ce. Jawad ya kammala karatunsa na sakandire, ya wuce kasar Canada yana digiri dinsa akan engineering. Haka rayuwar ta cigaba da gudana cikin nasarori da kuma kalubale kala-kala. A yanzu haka Mk ya samu appointment ya zama minister ilimi na kasa, yayin da ya nada Mahmoud mai magana da yawunsa. Yana Abuja tare da Farida a dalilin itama ta samu transfer a wurin aikinta zuwa Abuja. Sa'adah kuma tana kano tana cigaba da zurfafa iliminta, a yanzu haka digiri na uku take duk a fannin shari'a. Duk week end din duniya sai ya biyo jirgi ya zo, sai dai idan baya ' kasar. Ta da'de da tarewa a gidan Jawad, haka nan Mk yana kan yi musu gini da ya zarta wadda take ciki. Ta dauko Hajiyar Bichi suna zaune tare cikin girmamawa. A yanzu da shekarun hankali da girma ya zo mata sai ta gane ba abu mai Dadi a rayuwar mace irin samun miji na gari mai adalci, ita da kanta idan ta tuno ta'barar da ta yi a baya sai ta ji kunya ta kamata, ta kuma godewa Mk domin ba abin da bai mata ba, ta kuma gasgata shi da ya ce shi din tamkar Sumayya ne a wajenta ba wai miji kawai ba, ba abin da bai yi mata, yana kuma tsaye akan dukkan bu'katunta, sannan yana hakuri idan borinta ya tashi. Haka nan ta gasgata shi da ya ce Baffanta Babansa ne ba nata ba, domin ba abin da bai yi musu ba, ya rushe gidansu ya zamanantar da shi, ya kai iyayenta sun sauke farali. Itama ta je, ta koma Umrah, duk da bata aiki kuwa. Ranar juma'ah ta yi ferfesun naman rago ta kaiwa Hajiyar Bichi dakinta, sannan ta ce "Hajiya zan je na gaida su Baffah". Da murmushi Hajiya ta ce "Ki gaishe su Sa'a, Ubangiji ya yiwa kokarinki albarka, yasa kema naki 'Ya'yan suji 'kanki. Ta isa gidansu ta tarar da iyayen nata zaune a falo sun yi shar da su tamkar tsufa bai cimma musu ba, ta zauna tana cewa "wayyo Baffahna". Da wata irin 'Kauna ya ce"sarkin hakuri, giwar mata, mowar 'ya'ya". Ta murmusa ta ajiye masa kwanon naman a gabansa. Inna ta ce "Danma dai uwa mafi uba ko da uban sarki ne". Cikin tsokana ta ce"Ai ni Baffah kam ya wuce ki Inna, sai dai ki yi 'hakuri kawai". Ta mike ta shiga kicin din da yanzu yana cikin falon ta debe bowls ta zuba musu, suna ci, suna saka mata albarka. Ta hada kan kayansu kananu ta wanke su tas. Ta yiwa Innah ganeral sanitation duk kuwa da ta daukar mata Yar aikin da take zuwa ta yi mata shara da wanke wanke. Amma duk da hakan duk karshen wata sai ta zo ta yi mata gyara na mussaman. Baffah ya tsura mata ido yana godiya ga Ubangiji, da ya arzuta shi da samun 'Yaya mata, ya tarbiyaantar da su har ya aurar da su, yanzu gashi sun zame masa gata, sun janyo masa mazajensu suna ta hidima da shi, ya yi Imani ko yana da 'yaya maza ba lallai su yi masa abin da Mukhtar d Idris din Sumayya suke yi masa ba. Gashi kuma ya'yan nasa sun haifa masa 'Ya'ya takwas maza, domin nassin al'kura'ani ya nuna jikanka danka ne. Madallah da iyayen da basa zaben jinsin da suke son su Haifa, suke godiya ubangiji ta hanyar tarbiyaantar da ya'yansu mata cikin adalci da tausayi. Sa'a ta koma gidanta, iyayenta suna saka mata albarka da nemawa zuri'arta tsari daga rudin *HALIN YAU* Mk ya cigaba da kula da iyalinsa cikin adalci da tausayi. 'Ya'yansa biyar Sa'a na da uku Jawad, Jadid da Junior. Yayin da Farida take da biyu Amir da Amira. Wani week end ya zo Kano, suna zaune a falo ya kalleta ya ce "sai nake tuna shekarun baya da kike ce mini kin yi mafarki, kin zama big Madam, na zama Alaji, na 'kera mana mansion". Itama ta ce "Na tuna amsar da ka ke bani cewar banga ka 'kara Aure ba?" Ya fashe da dariya tare da janyota Yana cewa 'dukkan mafarkin ki Allah ya tabbatar miki su, kin zama big Madam, abin alfaharin kowanne miji, tashi muje mu yi nafila mu sake godewa Ubangiji da ya cika mana ni'imominsa. Wani watan Ina son dukkan ku mini rakiya na gano 'Dan-iyah a Canada har da kannesa zamu tafi". Ta ce "Jawad bai zama 'dan Malam ba Sai D'an Iyah?" Da murmushi ya ce "shi ya ce mini sunan da zai sanyawa jirginsa kenan 'Dan-iyah Airlines. Yana kuma fatan ya samu sarautar 'Dan-iyan Bichi. Zan fadawa Baban Khairat zamu tafi da ita, ta gano mutumin nata, wata'kila dai zumuncin Jawad da Khairat nan gaba ya bada mamaki". A zuciyar Sa'a sai fata take Allah ya tabbatar da wannan hadin. ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH. *NA GODEWA ALLAH DA YA NUNA MINI WANNAN RANAR TA 27-7. DA NA KAMMALA RUBUTA WANNAN 'DAN LITTAFIN NAWA MAI SUNA A SAMA*. *INA MIKA GODIYATA GA DUKKAN WANDA YA KARANTA LABARIN*. *INA SAKE GODEWA MASU KIRANA, DA MASU YIN MAGANA TA WHATSAPP DAN SU YABA MINI, NA GODE MUKU SAOSAI, UBANGIJI YA FINI YABAWA* *INA ADDU'AR ALLAH YA KAWO MANA ZAMAN LAFIYA A KASARMU TA NIGERIA, YA KUMA BAMU DAMINA MAI ALBARKA*. *AUNTY RABI SANI GODIYA MAI YAWA, TABBAS KARFAFA GUIWAR DA KIKE YI MINI YA TAKA MUHIMMIYAR RAWA WURIN INGANTUWAR LABARIN NA GODE UBANGIJI YA FINI YABAWA*. *INA ADDU'AR ALLAH YA JIQAN MAHAIFANA DA DUKKAN WADDA SUKA RIGAYE MU*. *UBANGIJI YA SAKE HADA MU CIKIN WANI LABARIN, DA NAKE FATAN KU KAR'BE SHI TAMKAR HALIN YAU.* *INA RO'KONKU KAR A HA'DA MINI DOCUMENT, BANA SO, DAN ALLAH A KIYAYE.* *ASSALAMU ALAIKUM WA RAHMATULLAHI WA BARAKATUHU*🤝 *SURAYYA
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157