Chapter 86
Chapter 86
sumewa ya wancakalar da ita, ya hau dukanta da hannuwansa. Ganin yana dukan amma ba abin da yake ji na sauki sai ma 'karin tafasar zuciya, ya kyaleta ya zauna a kasa dabas ya dinga ambaton innalillahi wa ilaihir raji'un, hawaye bakin ciki na tsere akan fuskar sa. Ta dago da 'kyar ta ga yadda ya ke zubar d hawayea! a fili bai damu da aga yana kukan ba, duk wata dauriyarsa sa ta kwace a YAU. Hankalin ta ya sake ri'banya tashi, ta dinga kuka tana fadin " Ka yafe mini, wallahi ba wayata bace". A tunzure ya antayo ashar irin wadda bata taba jinta ba, ya maka mata, tare da cewa "Idan ki ka kuma bude baki da nufin yi min, magana ko bani ha'kuri Billahillazi sai na miki abin da baza ki manta ba". Wayarsa ya ciro aljihu, da kyar ya iya lalubo sunan Fahad Auwal! Dalibinsa ne tun a FGC yana cikin samarin Sa'a duk da dai bata ta'ba kulashi ba, sannan yanzu ma dalibinsa ne a B.U.K. Da girmamawa ya gaida Mk. Cikin rashin sukuni Mk yace "Fahad cikin class mate din ku na FGC akwai mai karatu a Egypt kuwa?" Dan Jim Fahad ya yi sannan yace"Khalil Ibrahim ne kawai a Egypt". Ko godiya Mk bai tsaya yi ba, ya katse wayar. A fili ya ce "ban da tabbas, amma idan har yanzu kuna tare na tabbatar kun tabbata wakilan manyan shedanu a doron 'kasa". Ta 'kara karfin kukanta ta ce "Mala.. ya katseta ta hanyar jifanta da takalminsa da hagu. Tare da cewa "ki mini shiru, dama ai na fada miki ba zan sake yi miki uzziri akan shedanun yaron nan da baisan kimar da darajar aure ba". Ya jima yana ambaton addu'ar we yayewar ba'kin ciki, *"YA HAYYU, YA QAYYUM BI RAHMATIKA ASTAGIS*. Ya 'dan sami nutsuwa ka'dan ya kalleta ya ce " kin yi wankan ko ba ki yi ba?" Da'di ya kamata mussaman da ta tuna da asuba ya gama mitar hakurinsa ya 'kare, wannan karon period dinta takes too long. ta yi dariya ta ce bai 'karu ba kawai matsuwar da ka yi ne, amma dai nasan ba tantama I will be ready today. Tunaninta nemanta zai yi tunda dabi'arsa ce ya kusanceta a lokacin da ya ga shaidan zai dagula zaman lafiyar su. Da hanzari ta ce "Na yi". Ya zuba mata ido sosai yana so ya ji ko akwai sauran gurbi a zuciyarsa da zai sake yi mata uzziri, sai ya ji babu saura, yana jin idan bai rabu da ita ba, tabbas ba'kin cikinta ne zai zama ajalinsa. Dan haka muryar sa cike da rauni, hawaye na zirarowa ya ce "*Na sake ki, saki daya Sa'adatu*! Na ba ki dama ki zama yantacciyar da ki ke fata". Ta 'kwala uban ihu mai gigitarwa. 30/04. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 NA *SURAYYA DAHIRU*. •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ *_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai satar Dukiya._* _*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_ *Godiya ga makaranta* *Ina matu'kar Jin dadin yabawar ku kan rubutuna, Hakika da kune Halin Yau ya je inda ban yi zaton zai je ba. na gode muku dukkan makaranta littafin HALIN YAU da fatan ana lura da sakon da nake nufin isarwa, ana watsi da shiriritar da yake ciiki, Ubangiji ya bamu damina Mai albarka*. *Bari na sada zumunta da ku masoyan Sa'adah* *Hajiya Rabi Sani* *Aisha(cisse)* *Tababa ta Malam* *Asma'u Umar Ingawa* *Samira Annuri*. *Khadija Sadiq* *Safara'u Niger*. *Zainab Abdallahi* *Aishatu maina* *Khadija Bishir(Dijengala enterprises)*. *Masoyan da yawa mu tara a shafin gaba*. * SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 78. Kuka ta ke yi tamkar ranta zai fita, ta rarrafa ta ri'ke kafarsa ta dama. Cewa ta ke yi " Kar ka mini haka Malam, laifina bai kai ka 'dau wannan hukuncin ba, dan Allah ina sonka, ina son zama da kai". A hanzarce ya fincike kafarsa, ya nunata da yatsa amma ya kasa bude baki ya mata magana saboda yadda yake jin wani irin sanyi na ratsa shi duk kuwa da yanayin garin a daure yake da zafi, saboda hadarin da ya hadu amma ruwa bai sauko ba. Da 'kyar ya mike, ya shiga dakinta, ya dauko mukallin motar wadda yana tsakar dakin a yashe, rashin nutsuwa ya hana shi ya gani. Ya fito, ya tsaya yana kallon yadda take kuka mai tsananin ciwo, irin kukan nan da ba ya sa a ji sau'kin tashin hankalin da aka tsinci kai a ciki. A hankali ya ce "Tashi muje na kai ki gida". "Dan Allah Malam ka yi hakuri Ni bazan tafi ba". Fuskar nan a daure tamkar hadari ya ce " Ba za'bi na baki ba, ki tashi na kai ki cikin mutunci, tun ba ki tafi dutse a hannun riga ba". Hawaye face face a fuskarta, Ta ce "iddah zan yi a dakina kamar yadda shari'a ta tanadar, ka girmama shari'a. A kufule ya ce "wallahi ba anan gidan ba, ki je, ki yi a gidanku duk wata zan aiko miki abin da zai ishe ki! Na 'ki na girmama shari'ar, ke iyakokin ubangiji nawa ki ka take saboda son zuciyar ki, yanzu ne ki kasan ka'idojin shari'ar?" Ta yi 'kasa da kanta dan kaucewa kallon tsanar da yake mata. "Tashi muje" ya fada a kausashe. Ta 'ki koda motsin kirki, sai shesshekar kukanta kawai, wadda ta ke yinsa har cikin 'bargonta. A hasale sosai ya ce " Sa'adatu taurin kai a yau ba zai amfane ki da komai ba, bazan dauke ki da karfi ba, amma ki sani idan har ba ki tashi na mayar da ke cikin mutunci kamar yadda aka bani ke cikin mutunci ba, komai zai iya faruwa a tsakanin mu, na tsani na bude ido na ganki". Nan ma ko uffan ba ta ce ba, sannan kuma ta 'ki tashin. Ai kuwa ya ce "shikenan! Komai ya faru ki kuka da kanki, ya shiga 'dakinsa, mintina biyu ya sake fitowa ya dubeta tana kuka tamkar Baffah da Innah sun mutu rana 'daya, amma ko tausayi ba ta bashi ba. A kausashe ya ce "Zan fita yanzu! kuma wurin Baffan zani na fada masa yau na mayar da ke 'yantacciya, amma ki sani Billahillazi idan har na fita ni ka'dai na haramtawa kaina ke, idan haka ta faru, shari'ar ta ce ba dalilin ki zauna kimin idda a gida ko?". Tamkar tab'ab'biya ya ga ta mike ta fita waje a guje, ya bi bayanta dan ya lura tamkar ta zauce ne. Ba ta tsaya a harabar gate din su ba, waje ta fita kai tsaye, ta yi kicibus da wani tsoho sosai, zai wuce, a gabansa ta zube cikin fitar hayyaci tace "ka taimake ni Baba"! Dai dai lokacin Mk ya fito ya tarar da su a hakan. Da sauri ta dinga cewa "ga shi nan Baba, bashi ha'kuri saki na ya yi, fa'da masa Allah ba ya son saki, yana kuma tare da masu hakuri" Kallonta kawai za ka yi ka gane sakin nan ya susuta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157