Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 108

Chapter 108

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kaza mana, amma yau duk sun yi likimo tabbacin sun watsa shi a kwandon shara.p A sanyaye sosai ya bar gidan. Washagari kuwa ya bi jirgin Mangal air zuwa Lagos daga can ya shiga jirgin arik air zuwa kasar Birtaniya. Haka Sa'adah ta cigaba da jinyar zuciyarta, tana samun karfin guiwa wurin mahaifanta da Sumayya, domin Baffah da ya ga sun hade masa kai a gidan dole ya ajiye powaer sa ta maigida ya lallashe su da kalmomi masu laushi, da kuma sanin muhimmancin hakuri. Ya sake fa'da musu ba su fi shi takaicin auren Mukhtar ba, amma tunda shari'a bata hana shi ba, akan me shi zai kullace shi? Ya rufe da cewa "kuna ganin laifina dan ban roki Mutari ya zauna da ke akan dole ba, alakawari na yi ba zan bada auren 'yata ba sai a inda nasan za ta yi daraja, a farko da yake so ai na bashi, idan kum zaki fadi gaskiya ai ya ri'ke ki da daraja! a yanzu kuma, da baya so, bashi da abin da zan kalla da zan nemi ya zauna da ke akan tilas, hakuri wuya ne da shi, idan aka daure sannu a hankali za'a cimma buri". Ya nisa ya sake 'daure su da cewa "A zatona Salamatu, da ke da yaran da kika haifa mini da kuma duk abin da kuka mallaka zan yi iko da ku kai tsaye, ba tare da jin shakku ko fargaba ba, amma tunda laifine dan na yi ikon da abin da yake mallakin Iyah ne to ku mini afuwa, Iyah ta bini bashi in sha Allah zan biya a hankali" Kunyar kalamansa suka kama su mussaman Innah da ta bari hankalinta ya kwace akan wannan lamarin. A ranta ta dinga fa'din babbar jarrabawar da aka yiwa mata kishi ne, domin da yawa Mata sun halaka adalilin kishi, da yawa sun rasa Imani, ubangiji ka tsare mu ka sau'ka'ka mana. Hakuri suka bashi, Innah ta ce "Ba siyar da filin bane ya ta'ba ni ba, yadda ka shiga cikin lamarin auren ka yi kane kane ne ya kidima ni, amma ka mini afuwa wallahi ban taba jin bin da ya dama mini lissafi irin halin da na ga Iyah a ciki ba, amma Alhamdulillah komai ai ya wuce ina rokon kar Allah ya sake maimata mana wannan wakiar". Sa'adah ta nisa ta ce " Dayan filin ma na barka maka Baffa tsakani da Allah bana so, tunda na mallakesu ne adalilin Mukhtar. Kawai so nake ka daina nunawa ya fini a gurin ka, sannan ka mini afuwa akan komai ka daina fushi da ni, domin a yanzu Ni Mukhtar ya zalunta". Ya yi murmushi ya ce " ko Sumayya ba ta fiki ba Iyata, amma ina son ki gane gaskiya ko kuna tare da Mutari ba zan 'ki shiga hidimar auren sa ba, domin ya mini alkairori daban daban da bazan mance su ba, duk girman kuskure kuwa bai kamata Dan adam ya shafawa idonsa toka ya mance alheri ba, nasani hukuncin da ya dauka akan ki ya yi tsauri da yawa, adalcin da nake yi masa shine ban san mai kika yi masa ba, sannan auren da yayi ba zaluntarki ya yi ba, domin kuwa ko kuna tare zai yi aure shari'a ta bashi dama, idan yana so kuma zai iya adalci. Fatana ki kwantar da hankalin, ki yi hakuri in sha Allah komai zai daidaita miki, Na da'de da ya yafe miki Iyah, fatana ki bu'de zuciyarki ki fuskanci goben ki, sai kinyi nazari hadi da tsinkaye masu zurfi sannan gobenki zata inganta, na yarda da nutsuwar ki a yanzu, na kuma gamsu a kame kike dan haka bana fargabar zamanki! Amma ba ina nufin kita zama a hakan bane, ki bawa masu sonki kofar da za su tunkare ki, domin a hakan kika samu Mutari, yanzu kuma da kika barwa Allah ya miki zabi, ina da yakinin ba zai barki haka ba". Jikinsu ya sake yin sanyi, suna gasgata maganganunsa, mussaman Sa'adah da take jin karfin zuciya na dirar mata, tana hango ya kamata ta budewa kanta kofofin farin-ciki, zata dawo da kwalliyar da ta da'de da daina yi, sannan zata sake dagewa a makaranta domin a yanzu da Mukhtar ya auri Farida sai take ganin tamkar ya raina arzikinsu ne. *SURAYYA DAHIRU* ✍️✍️. 16/06. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._* *A guji ta'ba wannan LABARIN ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*. *Gaisuwa da fatan alheri ga* *HADIZA TINAU*. *Ki yi yadda kike so da wannan shafin, farar mai farar zuciya, ubangiji ya yi mana abin da bamu yi zati ba na alheri* *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 89- 90. Maganganun Baffah sun sake 'karawa Sa'a kwarin guiwar gina sabuwar rayuwar da babu Mk a cikinta. Tana kwance har tsakiyar dare tana nazarin yadda zata koma sabuwar Sa'adah da bata san Mk ba, ta nisa tana hakaito abubawan da zata nema, bata da bu'katar sutura domin tana da su ba adadi tsadaddun gaske, da yawansu ma bata sake waiwaryasu ba. Kayan kwalliya da waya tafi bukata a yanzu, sai hanyar da zata dinga samun ku'di tunda yanzu bata bu'katar na Mukhtar, tasan shima ba zai yi gigin bata ba. Ta sani iyayenta da Sumayya suna iyakar kokarinta amma dai ba zai yiwu ace dukkan lalurarta sai an yi mata ba. Saura kwana uku tafiyar su Jawad, Ahamad ya kawo shi gurin Sa'adah inji Hajiya ya kwana mata biyu, tare da sallama, tunda Mk ya yi aure Hajiya ta shiga cikin wani hali na kunyar Sa'a da iyayen ta, mussaman da Mk ya fada mata Baffan Sa'a ne ya biya masa sadaki, sai ta ji inama ace Hajiya Babbace a raye ita kuma a mace, tasan Hajiyar ta fita juriya da shanye 'bacin rai. Sosai Sa'adah ta samu sau'kin zuciya cikin sati biyu nan, domin ko da ta ji tafiyar da Farida da Jawad za su yi bata wani damu ba, illah ta ji ba da'di, Jawad ne ma ya nemi karya mata zuciya da yawan tambayoyinsa akan me yasa ba zata bisu ba? Da daddare suna kwance kansa na kirjinta yana bata labarin abubuwan da zai siyo mata idan zai dawo. Can ya ce "to kawai Mami mu tafi tare mana, kema ai baki taba hawa jirgi ba". A hankali ta ce "Malam bai ce na je ba, Aunty Amarya ya ce ta je". "Mami idan kin je ai ba zai yi fa'da ba". Cike da soyayyar 'danta ta ce "Ai bai biya mini kudin jirgi ba". Ya yi shiru sai ya ce "Na ji kafin ya tafi ya fa'dawa Hajiya, Baban Antin ya ce shi zai biya kudin tafiyar mu". Zuciyarta'daya ta ce " To ka ga ba ni a tafiya kenan tunda Ni Baffahna bashi da ku'di". Ya yi shiru, can kuma ya kalleta tamkar wadda aka kitsa masa ya nisa! ya ce "Ni zan tara ku'di da yawa na kai ki, har jirgin ma zan

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});