Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 82

Chapter 82

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ya barta tana kukan ita yake yi wa baki da mugun fata?. SURAYYA DAHIRU ✍️✍️ 18/04 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *SADAUKAWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 75_77 Hannu ta 'dora aka ta dinga kuka,tana fadin "Hasbunallahi wa ni'imal wakil". Har akayi azahar tana zaune inda take, ba abin da tasa a bakinta, duk da ga tiren abincin nan a gabanta, ba idonta kawai ba, hatta fuskar ta kumbura ta aune sosai saboda kuka, ta fada ta yi zuru zuru, ta dinga lissafin adadin rikicinsu, aduk fa'dan da zasu yi ita take janyowa, ta sake tuno adadin alherinsa hatta iyayenta bai huta da yi musu alheri ba, tun kafin ma ya aureta. Ta sake tuna duk laifin da take ganin ya mata cikin biyu ne, ko dai kawai zuciyarta ta raya mata ya Mata kaza a matsayin musgunawa, sai wadda 'kawayenta zasu ce ya yi a makaranta, ko ya mayar da ita Bagidajiya, alhalin ita tasan yadda yake girmamata yake girmama dukkan ra'ayin ta, amma sai tunanin ta ya bace ta biye musu. Ta tuna yadda yake tsananin son su zauna lafiya, su rayu cikin walwala da mutuntata juna, sai gashi yau da bakinsa yana la'antar zaman lafiya, yana fa'din bai yafe mata ba, idan ta zauna lafiya da shi. Idan ta yi wadannan tunaninka sai ta rushe da kuka, tana yi tana cewa "wallahi da gaske na gane gaskiya". 'Kiran sallah ya sa ta tashi, ta yi alwallah ta yi sallah, ruwan Lipton kawai ta sha. Tana zaune har dare! sallah ke tayar da ita, gefe kuma tana tunanin Jawad, da ya nan da ya debe mata kewa, yau kwanansa uku a gidan Samira, tunda suna hutu. Akan idonta ya dawo, kusan a guje ta sha gabansa tana kuka, tana cewa "Dan Allah ka yi ha'kuri, ya girgiza da ganin yadda fuskarta ta koma a yini 'daya kacal, ta so bashi tausayi amma da ya tuna haka take idan tana son abu, da zarar ta samu muradinta kuma za ta sake kirkiro wata matsalar. Ya dubeta ya ce "Ba ki fara kuka ba, sai burina na raba Safina da gararanba a titi ya cika" Ta kalleshi a razane, bai damu ba ya ce "babban burina ta zame mini amarya, na tabbatar zan sami nutsuwa da ita, ki adana hawayenki zuwa wannan lokacin". A gurin ta yi fa'duwar yan bori tana kuka tamkar yarinya har da tirza 'kafa irin yadda Jawad ya ke yi. tsaki ya mata yana fadin "Ba kuka ba ko bubburwa za ki yi bai dame ni ba". Ya shige ya rufe kofarsa. Washagari daga sallar asuba bai dawo gidan ba, hankalin ta ya tashi ba ka'dan ba, ta kalli agogo ta ga har karfe uku ta tabbatar yana shago tunda yau lahadi. Abin duniya ya taru, ya mata yawa, idan ta tuna kalamunsa wai son Safina ya ke yi, sai taji tamkar ta shide, ta tuno yanayin halittar su daya, ko a makaranta ana yawan fadin dirin jikin su shigen iri daya ne, da gaske za ta iya daukan hankalinsa kenan? Hawaye ya sake goce mata, karon farko da ta fara jin tsanar Safina a ranta, tana raya ba zata kuma ganin dariyarta ba, bare ta ga fuskar zama a gidanta Maganar ta mata ciwo fiye da zaton mai zato. Tana zaune ta ji wayarta ta hau kuwwa, da hanzari ta dauka, ganin Hajiyar Bichi ce, tun daga muryarta Hajiyar ta gane ba ta cikin sukuni. "A kwance kike ne Sa'a? na ji muryarki ba walwala". Duk yadda ta ke danne kukan sai da ya subuce mata, hankalin Hajiya ya tashi ta dinga tambayar ta dalili amma ta kasa yin magana, sai kukan kawai. Dai dai lokacin kuma Mk na zaune dakin Hajiya yana cin alalan gwangwani da ya ji lafiyayyen manja da yaji. Ta kashe wayarta ta zubawa Mk ido, tana jin takaicinsa na kamata, a kausashe tace "mai ya hada ka da Sa'a?" A nutse ya ajiye cokalin hannunsa, ya kalleta yace "Me tace na yi mata?" Ranta ya sake baci ta ce " Na tambaye ka, ka amsa mini da tambaya! Na lura da kai, ka mayar da ni shashar uwa, duk sadda ka sami matsala da matarka sai ka tattaro ka dawo da kwanon abincinka wurina saboda ka zubar mini da mutunci a idon yarinya, amma zan gyara". Ya yi sukuri dan yasan gaskiya ta fada, yana yin hakan. A raunane yace "Hajiya ni fa ba abin da ya ha'damu, kinsan kuma yadda nake son 'dan'danon girkinki, dan na yi aure shikenan sai bazan ci ba?". Ido kawai ta kafe shi da shi, tun yana murmushi har ya fara shafa 'keyarsa, yana jin kallon na shiga jikinsa, yana tuna lokutan baya na 'kuruciya, idan Hajiya ta musu irin wannan kallon take suke shiga hankalin su, saboda yadda ya 'kunshi abubuwa da yawa ba sai ta yi magana ba . "Tashi ka kaini gidan, na ji ba'asin kukan da take ta faman yi, wa ya sani ma ko dukan ta ka yi". "Haba Hajiya! Kinsan dai ban samu tarbiyar dukan mace ba, ita kukan banza ne da ita, duk sadda zuciyarta ta raya mata, kuka take yi, da dalili ko babu". "Mahaukaciya ce ai". Jin amsar Hajiya yasa shi yin shiru ya lura ranta a bace yake da shi, ya mi'ke ya dauki waya da mukallin motarsa da ke gefensa ya kalleta ya ce "Allah ya huci zuciyar ki Hajiya, ina jiran ki a mota". Kozai kozai suka tarar da ita, cikin kwanaki uku kacal gaba'daya ta lalace, karon farko da Hajiya ta ganta kaca kaca, kullum fes zata tarar da ita, haka muhallinta. Hajiya ta ka'du kwarai da yadda ta ganta, da sauri ta isa kusa da ita, ta ri'ke ta, ita kuma ganin ta sami mai rarrashinta yasa ta kwantar da kanta a jikin Hajiyan ta dinga rera kukan tamkar mai wa'ka. Mamaki ya kama Mk! ya coge a bakin kofa yana kallon kukan shagwaba da iskanci a wurin Sa'adah, ta masa laifi, ta kai 'kararsa. Ya na'de hannunsa a 'kirjinsa, yana sauraren 'korafin da ta ke rattabawa Hajiya! "kuskure na masa cikin rashin sani, na yarda na yi laifi, na bashi hakuri tamkar harsena zai tsinke ya ki ha'kura, yanzu kuma sai ya fara soyayya da kawata dan ya ci mini fuska ya kuma janyo mini raini" Cikin kuka sosai take bayanin. Hajiya ta rasa mai za tace! ta fahimci Sa'a ba 'karamin kishi ne da ita ba, kishin nata kuma ya zarce ka'ida, amma da ta lura har da 'kuruciya a kanta, sannan dabi'a ce ta matan YAU sawa miji ido da kuma 'dorawa kai zazzafan kishi tamkar wadda aka musu busharar an janye ayar da ta bawa maza damar auren abin da ya musu da'di, daga mata biyu, uku ko hudu. A hankali ta ce "akan yana da budurwa ki ka maida kanki haka, Ina ruwan ki? ki daina sa ido ko bibiyarsa, ba ruwan ki da abin da yake yi matu'kar bai tauye miki hakkin ki ba, idan kuma ya na 'ketare dokokin shari'a wannan kuma tsakaninsa da ubangijinsa ne". Kan Sa'adah na

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});