Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 22

Chapter 22

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·• *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. *Gaisuwar fatan alheri ga Zauren Fadila lamido!* *BA LABARI FANS 2* _MK DA SA'ADAH NA GAISUWA_🥰. 27_28. Cike da fargaba ta zuba wa Zainab ido, zuciyarta na bugawa ta ce, "Ban gane ba?" Muskutawa Zainab din ta yi sannan ta ce "Ina nufin ki toshe dukkan 'kofofin da kika bude na rashin 'da'a a gabanshi, kinga yanzu ya gamsu kin canja, kin shiga sahun 'dalibai masu dagewa, to ki tattaro dukkan ladabi da nutsuwa ki sanya su a fuskarki da dukkan ayyukanki, ba iya haka ba har a zuciya, ina tabbatar miki idan kika yi haka kin rufe 'kofar da zai dinga miki ganin mai 'karancin tarbiya. Sannan ki yi addu'a, ki bar wa Allah za'bi, idan alheri ne kuma an 'kaddara mijin ki ne, kina zaune Allah zai turo miki shi". Shiru ta yi tana nazarin maganganun Zainab, wanda ta tabbatar iyakar gaskiya ta fa'da mata. Ta nisa sannan ta 'dago ta ri'ke hannun Zainab ta ce Na fahimce ki, na kuma gode da shawarar ki, amma don Allah ki ri'ke mini sirrina." Murmushi Zainab ta yi tare da cewa, "Ki sa a ranki amana mu ka yi wannan maganganun, kuma mutum amintacce ne mai 'rike amana. Ina tabbatar miki da ikon Allah baki da matsala da ni" Haka suka ci gaba da hirarsu, bayan sun yi sallar La'asar ba da jimawa ba, ta musu sallama ta tafi, Zainab ta raka ta har kusan gidansu. Tunda suka koma makaranta gaba'daya ta mayar da hankali kan karatu, sannan ta bi shawarar Zainab, don haka gaisuwar girmamawa tare da mutuntawa take wa Uncle MK, har ya ji cewa lallai wannan ita ce Sa'adah 'diyar Malam Basiru, waccan da ta gabata ta aro ce. don haka ya daina duk wani gallazawa da yake mata, sai ma wani shiri da yake da ita. Wanda hakan ya janyo hankalin 'dalibai aka fara gaskata ra'de radin da ake yi cewar son ta yake yi. Wani abin mamakin kuma ita ma Farida sai ta fara jin haushin Sa'adah, tana ganin ta tamkar wata 'yar fashi a soyayya ko mai barazana a rayuwarta. ta san duk yadda take da 'kyaun da ya kai ya kawo, ba ta yaudari kanta ba, ta tabbatar ba za ta nuna wa Sa'adah komai ba, sai fari da gashi da kuma tsayi. Amma batun cikar halitta da kuma boyeyyen kyau da sai an nutsu ake gane shi ta sani Sa'a ta kere mata. Wata rana sun hadu a Biology Lab, kawai Sa'adah sai ji ta yi Farida ta ce "Iyah Basiru" Ranta ya yi mugun 'baci, tunda da izgilanci ta fada mata, take ko ta 'daga murya ta fara mata sababi, saboda Sa'adah mafadaciya ce ta gaske, sai dai kuma ita wacce ta yi tsokanar ta si'dade ta barta a gun. Wanda hakan da ta yi har ya fi wa Sa'a ciwo fiye da tsokanar da ta mata. Shike nan sai Farida ta mayar da tsokanar ta zame mata 'ka'ida sai dai idan ba su hadu guri 'daya ba, ranar kuma a shop suka hadu ta faki ido ta galla mata harara tace, "Sa'ade gwalli" Abinka da wanda aka dade ana tsokana kuma mai 'karancin ha'kuri sai kawai ta zabura ta kai mata wawura, ta sha'ke ta da 'karfin gaske, nan da nan hankalin mutanan gun ya kai kansu, aka taru aka karbe Farida a hannunta, tana mayar da numfashin wahala dan ba 'karamin sha'ka ta sha ba, musamman da ke ba ta da da kuzari saboda rashin cikakkiyar lafiya. Aunty Ngozi malamar (Mathematics) ce ta zo wucewa ta tsaya tana tambayar ba'asi, bayani aka mata wanda kusan duk gurin shaida aka wa Farida cewa tana tsaye kawai aka ga Sa'adatu ta kama ta da kokawa. Saboda haka sai ta tattara su ta tafi da su Staffroom wanda a can aka yi shari'a. Kusan dukkan staff din bayan Farida suka bi, saboda rashin hayaniyarta, ga ta kuma hazi'ka ce, haka aka yi punished din Sa'adah ta hanyar sa ta shara da kuma gargadi mai tsanani, akan komai za a mata ba ta da ikon daukar doka a hannunta. Hatta Uncle MK, Sa'adah ya jawa kunne akan zai yi wahalar gaske Farida ta tsokane ta wanda hakan da yayi yasa ta jin wani takaici ya kama ta fiye da yadda aka ba ta horo bayan kuma ita ce da gaskiya. Wannan abin ya yi matu'kar tsaya wa Sa'adah a ranta, shi yasa ta ji gaba'daya makarantar ta fita akanta musamman ko yaya idan ta ga gilmawarshi da Farida sai ta ji dukkan walwalarta ta kau, duk da dai ba ta da tabbacin abin da take zargi a tsakanin su. Tunda ga nan kuma Farida ba ta sake marmarin tsokanar Gogel ba dan kuwa ta ji 'kamshin mutuwa a hannunta🤩. Ana cikin haka aka fara register din JAMB, tana fada wa Baffan su maganar kai tsaye ya ce mata ba wata jarrabawar shiga Jami'ar da za ta yi don kuwa aure zai mata idan mijin ya yarda sai ya siya mata ta yi a 'dakinta. Wannan ma na cikin damuwar da ta sake sa mata tsanar FGC KANO. Dukkan 'yan ajinsu za su yi wannan jarrabawar sai ita kadai ce a ajin za a ce ba za ta yi ba. Wanne irin koma baya ne wannan? Wannan ba da kai har ina? Kamarta ace ita ce koma baya a komai?🤔 Sa'adah ke nan! Wadannan damuwowin sai suka sa ta ji gara ta koma asalin makarantar da ta bari a baya ta zana jarrabawar kammala sakandire, nan ma da ta gabatar da maganar gaban Baffa tare da ba shi uzirin ai ba sosai ake cin jarrabawa a wannan makarantar ba, kai tsaye ya ce mata bazai yiwu ba, tunda anriga an biya mata kudin jarrabawar ba, ba za a yi asarar su ba, wannan shi ne karon farko da Baffan bai goya mata baya akan wani abu ba. Ganin ba ta sami goyon baya ba, ga kuma ba'kin cikin da za ta kwasa a FGC KANO, sai kawai ta daina zuwa makarantar gaba'daya, wanda hakan bai damu Baffanta ba, sai cewa ya yi to ta fito da miji, ai Sumayya ma ba ta sami hakan ba ya aurar da ita ga shi nan kuma tana zaune lafiya cikin rufin asiri mai yawa, fiye ma da wanda suka yi karatun. Inna kuwa uffan ba tace mata ba saboda yadda take ganin take-taken Sa'adah nan gaba fin 'karfinsu za ta yi, garama a aurar da ita ya fi mata kwanciyar hankali. Tsawon sati tana gida ba ta je makarantar ba, rannan da yamma tana kwance a dakinta, tunda yanzu Inna fushi take da ita sosai, don haka ba ta jin da'din zaman gidan gaba'daya, ta ji murya Baffa na fadin"Iyah" Da sauri ta amsa ta fita tsakar gida inda yake tsaye, ta tsugunna tare da cewa "Gani Baffa" Ya kalle tay ya ga duk ta lalace tsabar fitinar da ta sawa ranta. ya ce, "Da ma yaron nan Mutari ashe a makarantarku ya ke koyarwa?" Shiru ta yi tana nazarin sunan, kafin ta ce, "Wani abu ya sake cewa?" "Dazu ya same ni a inda nake zama shima

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});