Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 59

Chapter 59

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da ta ke ciki na rashin tsarki. Idonsa sunyi ja, sun kankance saboda fitina, ya zuba mata su,ya ce "Hajiya Babba da Innah ne suka zartar da hukuncin nan, hakuri zamu yi, mu yi yadda suke so". Wani irin farin ciki ya sake kamata, amma a iya zuciyarta ya tsaya, tana jin zumudin sake zama da mahaifanta na taso mata. Haka suka kwana yana jaddada mata irin kewarta da zai yi, tamkar wadda kasar za ta bari. Kwanaki biyu a tsakani ta koma gida tare da dukkan abin da za'a bukata, Hajiya Babba ce kuma ta kaita kamar yadda ta yi al'kawari. Sosai Inna ta ke kula da Sa'adah, wankan rumfu take mata ba tausayi, ga duren kunu, da tuwo, duk ranar da zata mata gardama kuwa cewa take yi " Na lura dakinki kike son komawa, zan 'kira Hajiya ta zo ta mayar da ke, tunda ina tattalinki, kina 'ki! idan kika kufu'de na ga yadda za kiyi rawar jiki akan mijin, ko shi ya yi rawar kai akan ki". Shiru ta ke yi, kan dole kuma sai ta yi yadda Innar take so. Jawad ya sami kyakkawan kulawa, kullum safe aka masa wanka ya sha nono, Inna take goya shi, haka zai yini a baya sai anyi azahar yake tashi, cikin 'kan'kanin lokaci ya bundume, kammaninsa da Mk suka bayyana 'karara. A yini Mk na kiran Sa'adah kamar sau uku koma fiye, koyaushe cikin tambayar lafiyar su, ko yace Babana na kukan dare har yanzu, ko ya tambayi me take so, menene bata da shi, kar fa tace zata dinga 'dorawa Baffa nauyi. Ire iren tambayar kenan a kullum, itakuma cewa take, komai akwai Uncle. Duka-duka ma yaushe muka zo ne? Ranar da suka yi kwana biyar, ya je musu. Ana idar da sallar la'asar ya Isa gidan, a zaure ya tsaya, yana faman kiran wayarta, tana ta ringing amma ba'a dauka ba, ya jingina da bango, yana ri'ke da wayar. Baffah da yake faman jijjiga Jawad, saboda wankan da Inna ta ke yiwa Sa'adah, kullum ana idar da Sallar la'asar yake dawowa gidan dan ya ri'ke musu shi, su yi wankan, saboda riko da al'adar ba a barin jariri shi ka'dai.😁 Yau sai koke koke yake yi a dalilin cikinsa ya kumburaba a ankara ba, yana sa'be da shi a kafada ya doshi zauren, kwatsam yaga Mukhtar a tsaye. Cike da girmamawa ya tsugunna ya gaida shi, Baffa sai fadin "ya ka tsaya anan? da ga yau ka dinga shiga kanka tsaye". Baffah da kansa ya masa jagora har 'dakin Sa'adah yana cewa "wanka suke yi, zauna ka saurare su kadan". Ya mika masa Jawad tare da fadin "dama so na ke na fita ana jirana za mu je dubiya asibitin Malam". Cike da kunya ya karbe shi, yana masa godiya. Baffah na shirin fita Inna ta fito duk ta hada zufa, ta kalle shi, ta ce "kwantar da abokin naka ka yi?" "A a Babansa ne ya zo, yana gunsa, na shigo da shi, yana dakin Iyah ni fita zanyi, za mu je asibiti mu sake dubo Malam lado". "Adawo lafiya, shikuma Allah ya bashi lafiya". Ya fita, yana fadin "Ameen ameen". Sai da ta sako hijabi sannan ta shiga suka gaisa da Mk, da yake ta fama da Jawad. Ta karbe shi tana fa'din "Bari a masa wanka kar sanyin yamma ya sauka, ko idan ya ji ruwan dumi zai daina wannan koke koken". Murmushi kawai ya yi, kansa a kasa, ya bata shi, a zuciyar sa tana jinjina kunyarsa, ko Idris din Sumayya bai kai shi kunya ba. Yana zaune yana jin kukan wanka da Jawad ya ke tsalawa, jikinsa sai tsuma yake yi, yana jin tamkar ya leko yaronsa ko sabulu ne ya shigar masa ido, amma kawaici ya danne shi. Ana cikin haka Sa'adah ta shigo da daurin kirji, ta yi mayafi da faffadan tawul. Mamakin ganinsa a zaune ya daskarar da ita a tsaye. Da azama tace " Uncle yaushe ka zo?" "Tun dazu, dan Allah hanzarta ki dubo yaron nan , ki ji har shidewa ya ke yi?" Ri'ke baki ta yi tare da cewa"oh oh wato Innah tace mini bani da kunya ko?" "Haka yake da kukan wanka, da angama kuma ya yi ta barci, sai dare zai ishi Inna da kuka". "Oh barinta ki ke da shi?" Eh to, shi sai yace ba zai kwanta ba, sai dai a baya! itace kuma mai jure goyon, tace na kwanta na yi barci na huta". "Amma kuwa dai ba ki da tausayi ko da ya ke, Auta ce ai". Dariya suka yi a tare, ts shirya cikin doguwar rigar atamfa, irin dinkin masu shayarwa. Ta zauna tana shafa mai tare da turare, ta yi cas, ta masa kyau, da gaske ta huce din, duk wani kumburi ya sace, fuskar nan da ta aune, duk ta sabe, ta dawo masa Sa'adatun nan mai burge masu kallon ta. Yace "kin huce din fa Iyah, kin zama so mashallah". Ta tura baki gaba, tace "ai so na yi na zauna kar na huce din, naga yadda zaka yi". "Hmm ke dadina da ke misunderstanding dina kike yi sometimes". "Iyah Iyah" Ta mike da sauri tana amsawa ta fice gurin Innah da take 'Kiran. " Zo ki dauke shi ki bashi ya sha, ashe cikinsa ne ya kumbura shiyasa kukan yau yafi na kullum, yanzu Ina bashi wannan maganin ya hau gyatsa, sai kuma ga tutu, dole sai canja masa Pampers din na yi" Ta karbe shi tana fadin"Ayyah, sannu da kokari Innah". Ta dawo dakin ta zauna ta fara shayar da shi, Mk da ya zuba musu ido yana jin duk wani bugun da zuciyar sa ke yi da kaunar su ta ke bugawa. Sai da ya 'koshi, sannan ta mi'ka masa, ya karba yana mai masa kallon kurillah, yana ganin hoton fuskar sa, akan ta yaron. Ya dago ya kalleta, ya yi kasa da murya sosai, sannan ya furta "Duk yadda kika yi ta makale min, ashe ba wani abin da kike tabukawa? dubi! ba wani abu, na ki a jikinsa". Kunya ta kamata, ta kasa cewa komai sai ta buge da murmushi. Haka suka sha hirarsu, ta na shan yoghurt din L&Z da ya taho mata da shi. Kwana ashirin da haihuwar, Sumayya ta zo ganin Baby, tare da kayan uwa da jariri kala kala,sun zo juma'ah suka juya lahadi saboda makarantar Yara. Ranar da ta cika sati uku ta koma dakinta, rawar jiki ba irin wadda Mk bai mata ba. Sun tabbatar sunyi missing juna, irin wadda ba su taba yi ba! haka suka cigaba da rainon dansu cikin tattali, da kulawa mai yawa. Surayya Dahiru ✍🏼✍🏼✍🏼 19/03. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._* *A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*. *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 59-60 Irin kulawar da MK yake yi wa Sa'adah da danta, yasa take mamakin da ake cewa

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});