Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 67

Chapter 67

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,196 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kuma ta ganshi yana taimaka wa kanwarta da ta samu admission zata karanta economics fa? Farida ba tasan komai a new side ba, tunda ita a old side take karatunta, shikuma sai ya rakasu a kokarinsa na kyautata mata kamar yadda take girmama shi a matsayin malamin ta. Shi bai san har anzo anfesa mata ba.😄 Da yamma ya dawo, ya ya tarar da ita goye da Jawad, kayan da ya barta da su ya dawo ya same ta da su. kallo daya ya mata, ya gane bata ci komai ba, sannan bata yi wanka ba. Ya rasa gane wannan masifar da ta 'dorawa ranta, da 'kyar ta bude baki ta ce "Sannu" ya amsa da yauwa ya isa bayanta yana duba Jawad da yake ta Nishi, shi dai ta masa wanka fes yake, sai dai jikinsa kamar wuta. "Kin bashi maganin kuwa? na ga jikin, har yanzu bai sauka ba". Ko kala ba ta ce ba, ya isa inda ledar maganin take ya bude ya ga ba wadda aka taba, bare a sha. Ransa ya baci matu'ka da gaske, ya nunata da yatsa ya ce " Wai ke wacce irin yarinya ce marar mutunci?" Ta yi 'kasa da kanta tamkar wadda ta saduda, yaci gaba da fadin "kin fara kaini bango Sa'adatu, kullum a cikin zullumi nake zaune da ke, masifar yau daban, ta gobe daban, haka ta jibi". "Ai kaci moriyar ganga, sai ka kawo karshen zaman zullumi Mk" ta fada kanta tsaye. A razane ya zuba mata ido, yana kallon ta, itama ta kafe shi da idon da suka cika da 'kwalla ba alamun tsoro ko shakka a cikinsu. Ya kasa cewa komai, dan kuwa a yadda yake jin bacin rai zai iya na'da mata dukan tsiya, abin da baya fatan ya aikata kenan, dukan matar aurensa. Ya mika hannun yana fadin "bani yaron, kai tsaye ta ce "idan kai ka haifar min, ba sai ka 'kwata ba". Ya yi kanta yana fadin "Me kika sha ne? Bari na sauke miki iskancin da kike fama da shi". Ga mamakinsa ko motsi ba ta yi ba, sa'banin da, idan ya mata irin haka take kwasa a guje ta 'buya. Ya isa kusa da ita ya kama kafadunta ya girgiza da karfi har sai da Jawad ya motsa, ya ce " fada min me yake faruwa, me na miki har ya shafi wannan yaron da bai san komai ba?". Tsaki ta ja, tare da fizgewa, ta koma gefe tana sake 'daure goyonta sosai. " What! Ni Kika yiwa tsaki Sa'adatu? abin da kinfi kowa sanin na tsani a mini?" Ai kuwa ta sake jan wani fiye da na farko, sannan tace " ka kashe ni! an maka tsaki Mukhtar". Wani irin shock ya kama shi, a farko da tace Mk gatsal mamaki ta bashi, amma a yanzu da ta ambaci cikakken sunan sai ya gane ashe Mk din a mutunce ta fa'da. " Allah ya tsare ni da kisan kai, duk bala'in da kike nufi na da shi, in sha Allah ba zai same ni ba". "Tunda abin har ya kaimu ga haka, to shikenan! ki yi harkar ki na yi tawa, sauko shi na bashi maganin, sai ki mayar da shi". "Baka ji mai nace tun farko ba? ka 'kwata' a shirye nake da mu karya yaron nan! idan har ni na tsugunna na haife shi wallahi ba zai sha wannan maganin ba". "Ya zuba mata ido, yana jin haushin ta na samu gurin zama a zuciyarsa, ya ce "idan na siyo masa wasu zai Sha?" "Idan na tabbatar da sahihancin su ba". Ya dauki ledar maganin ya fita ba tare da ya sake cewa komai ba". Bai wani jima ba, ya dawo da su, a wata ledar mai tambarin lamco pharmacy. Ya mika mata, tare da cewa "gashi" ya juya ya fice. Ta dudduba ta tarar da su dinne, illah ledar da ya canja, ta yi 'kwafa ta dankwarar da su. Ana idar da Isha ya dawo, ya tarar da maganinsa akan kujera ita kuma ta shige 'daki ta rufe kofar, Jawad sai kuka yake yi. Ya duba maganin ya tabbatar ba'a bashi ba, ya hau dukan kofar, amma banda kukan yaron ba ya jin komai. Ya kirata ya fi sau hamsin amma tamkar bata gidan. Ya hassalo sosai ya ce "wallahi idan yaron nan ya mutu, ke kika kashe shi, da hannuna zan mika ki wurin hukuma". Sai lokacin ta ce "yi sauri kar 'kuda ya riga ka, wato ka maida ni bagidajiya, ka fita da magani kamar gaske, ka sake dawo min dashi, idona tar yake, bazan bashi ba". A fili ya dinga fadin "Innalillahi wa Inna ilaihir raji'un". Ya fice zuwa dakinsa, yana karfafawa kansa guiwar ya rabu da ita, ai ta fishi son yaron. Karfe shadayan dare ya dinga jin kukan yaron, da farko ya yi biris, amma da ya dinga jin 'ka'karinsa baisan yadda akayi ba sai ganin kansa ya yi a jikin kofar dakin Sa'adah yana bugawa, yana cewa "ki dubi girman Allah ki bude min kofar nan, komai na yi miki, na yarda kimin komai, amma banda yaron nan, ki ji tausayinsa, ki ji tsoron hakkinsa". Har ya gama bilayinsa bata tanka ba, tana jin ta shirya faruwar komai ciki har da rabuwarsu. Cikin ikon Allah, sai Jawad ya sami barci adalilin ta bashi tea, ta bashi maganin zazzabin sa da yake da shi. Da asuba kukan Jawad ya sake tayar da hankalin Mk, ya rasa inda zai tsoma ransa, a take ya kira Hajiyar Bichi a waya, bai fa'da mata komai ba, ya ce dai kwana suka yi Jawad bai yi barci ba. Ba bata lokaci, ta taho,har da garin kunun ko zai dinga sha, tare suka shiga falon, ya dinga kiran Sa'adah amma ta 'ki budewa, sai da taji muryar Hajiya tana cewa"Sa'a, menene yake faruwa ne?" Da sauri ta bude 'kofar, ta fito idonta, yayi luhu luhu, yayi ja tsabar kuka. Ta mi'ka mata Jawad ta zauna a gefe tana kuka tamkar wadda aka yi wa mutuwa. Hajiya ta kalleta, taga ta fita a hayyacinta, ta rame farat daya, ta maida kallonta ga Mk taga shima a firgice yake. Tace ciwon Jawad ne ya susuta ku haka, ko kuwa wata matsalar ce?" Ya dauko maganin ya mi'ka ma Hajiya ya ce "Dan Allah ki bashi maganin nan", ta karba, ai kuwa Sa'adah ta saka uban kuka tana cewa "Kar ki bashi Hajiya". Hajiya ta rasa maganar wa zata dauka a tsakanin su, ta dubi Sa'adah tace "Yi shirunki bazan ba shi ba, fada min me ya faru?" Ta kasa magana sai kukan da take yi mai dauke da shesshekar ajiyar zuciya. Ganin hakan yasa Hajiya ta rufe Mk da fa'da, ta inda ta shiga, ba tanan take fita ba, tana jaddadawa laifinsa ne, tunda Sa'a ba me fitina bace. Ya yi shiru ya dauki laifin da bai yi ba. da lallashi, Hajiya ta samu Sa'adah ta fada mata dalilin da bata son maganin alhalin ba expired suka yi ba. Da rawar murya ta ce " Budurwarsa ce ta siyi maganin, akan idona suka yi zance ta siya ta bayar". Ta karasa cikin gunjin kuka. Dariya abin ya bawa Hajiya, amma sai ta dake, ta dinga salati tana

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});